Sashe 203
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Aunty Benazir" Cikin kunnanta ta tsinkayi muryar Zeenatu, Kasa dagowa tayi saboda bata son yanayinta ya jefa zeenatu a hali na damuwa
Shigowa dakin zeenatu tay, jikinta sanye da jallabiya fara.
Ganin Benazir zaune ta kife kai gaban mirror yasa ta nufe ta.
"Aunty Benazir, lunch is ready, we're waiting for you" ta fada tare da karasawa gaban ta.
Jin shiru bata dago ba yasa zeenatu tayi tunanin ko bacci ta ke yi.
Dafa bayanta tayi"aunty Benazir, Wake up pls, " taji tayi shiru bata tanka mata ba.
tasan in har ba magana ta yi mata ba, ba tafiya za ta yi ba, a yanzu bata son kowa a kusa da ita tafi son kadaici.
"Zeenatu! Pls ki kyale ni, basai kun jira ni ba, Ki tafi kawai ku ci abincinku,"
ras gabanta ya dan fadi jin yadda Benazir take magana cikin shesshekar kuka arude ta furta"Aunty Benazir! Meke damunki? Baki da lafiya"?
Bata san sa'adda ta daka mata tsawa ba"bansani ba, Zeenatu! Nace ki kyaleni, Ki rabu dani, bana son ganin kowa akusa dani..."
zazzare blue eyes dinta tayi, abunka ga shagwababba ta fashe da kuka ta juya ta fuce da gudu ta nufi dining area.
A lokacin Mami da Hajiya sarah tare da Dr shureim da Alhaji Ubaida suna azaune kan dining Chairs har sun fara cin abincin, Kukan zeenatu ne yaja hankulansu ga dubanta, azabure suke mike suna kallonta, Ta na karasawa ta fada jikin mommynta tana ci gaba da kuka, Hankali atashe suka dubi juna kafin suka maida idanunsu akanta.
" Zeenatu meya faru? Ina Benazir din? Wa ya tabaki"? Alhaji ubaid ne ya tambaya.
Mami tace"ki bude baki kiyi magana mana! Wani abunne Ya hadaki da Benazir dinne"?
Dago da ita Hajiya sarah tayi"Daughter, Daina kuka, Fada min meya faru"! Cikin kula tayi maganar tana share mata hawayen fuskarta
Cikin shesshekar kuka tace"Ah.. an.. aunty Benazir ce take kuka, Nace tazo muci abinci shine ta daka min tsawa tace in tafi bata son ganin kowa a tare da ita"
Dr shureim bai tsaya ya karasa sauraron maganar Zeenatu ba, Ya zame jiki Ya nufi dakin Benazir tunkafin Ya karasa shiga Ciki yajiyo sautin kukanta, gabansa na faduwa ya afka ciki Ta cikin madubi Ya hango fuskarsa sharkaf da hawaye ta zabga uban tagumi kamar wadda ta rasa gata a duniya, da sauri ya nufe arude ya furta Benazir! Lafiya kike kuka? Meke damunkin ki ne?
mikewa tayi ta nufe shi ta kwantar da kanta saman kafadar shi tana kuka, bubbuga bayanta ya somayi da hannunsa cikin sigar lallashi yace"pls ki fadamin damuwarki, Zan taimaka maki mu nemi mafita, amma kukan nan bazai amfane ki da komai ba, saima yajaza maki ciwon kai"
dakyar ta hadiye kukan tace"yaya shureim ina ma mutuwa zata zama hutu agareni wlh dana mutu na huta, nagaji nagaji da azabtarwar da zuciya keyi min akan rashin mijina da yata, yaya shureim bana jin dadin komai, hankalina ba akwance yake ba, Ina so nagan su..." dakyar ta karashe maganar..
Gaba daya a kunnan su Mami da basu dade da shugowa dakin ba, Gaba dayansu sunyi tsaitsaye cirko cirko suna sauraron maganar Benazir, tausayinta ne ya kamasu mami tuni idanunta sun ciko tab da kwalla, batasan ya zatay ba, ita kanta zataso Benazir ta hadu da bayin Allahn nan ko ta samu nutsuwar hankali..
Zeenatu dake kuka kalaman benazir sun karya mata zuciya, wani kukan takuma fashewa da shi.
"Benazir, Kiyi hakuri, Ki kara jurewa dan Allah, Na roke ki, sanya damu arai bazai haifar maki da komai ba, saima ta fama maki raunin dake a cikin zuciyarki, bana so a koma yar gidan jiya, dan Allah Benazir kiyi hakuri zamu tayaki da addu'a kema ki dage in sha Allah zasu bayyana"
Hajiya sarah ce ta yimaganar cikin sanyin murya.
Girgiza kai Alhaji ubaid yai shi kanshi abun na damun shi.
"Kinga kukan Ya isa haka, Kiyi shiru, in sha Allah Idan Uncle dinku ya dawo zanyi magana da shi ya taimaka yasa a yi cigiyar su agidan jaridu watakil adace..."
gaba daya tunaninsu har yanzu babu labarinsu ita kadai tasan Da zaman su..
A hankali ta dago daga kan kafadar dr shureim Idanunta sun kada jawur ta dube su ji take kamar ta fada masu Taj da Unaisah suna nan kuma tasan inda suke, ko dan ta samu su tayata neman yafiyarsa.
Girgiza kai tayi"nagode da kulawarku agareni, Amma basai an yi cigiyarsu a gidan jaridu ba, Aneelerh ta fada min sunyi iyakar bakin kokarinsu gurin yada hotunansu a social media da Gidan jaridu amma har yau babu labarinsu...." ta dan dakata kafin ta daura da cewa"dan Allah kada ku damu da halin da nake a ciki, bawai don banyi imani da kaddara ba, wlh nayi kokarin In manta da su a cikin zuciyata amma abun Ya faskara..."
ta faɗa tana matse kwalla.
Kallonsu Dr shureim yayi"pls Ku barni da ita, ku je ku ci abincinku, Zan yi mata nasiha" Alhaji ubaid yace"yawwa shureim pls kayi kokarin shawo kanta, bana so ciwonta ya tashi" amsa mashi yai da toh, fita su ka yi ya rage saura su uku
Kallon zeenatu yayi, Tana atsaye bakin kofar sai shesshekar kuka take.
"Calm down your mind, Ki kawo min lunch din ta a daki" ta amsa da toh ta juya ta fuce..
Ruko hannunta yai suka zauna kan gadon ta.
Nasiha ya farayi mata cikin kwantar da murya har saida taji zuciyarta ta dan lafa da radadin da takeyi mata.
Sai da yaga ta samu nutsuwa sosai kafin yace"akwai inda ke maki ciwo" girgiza ma shi kai tay"a'a ya shureim, lafiyana lou"
"Okay, " ya fada tare da sauke ajiyar zuciya.
Shigowa zeenatu ta yi cikin dakin, hannayenta ruƙe da tray mai dauke da lunch ta mika ma dr shureim Yasa hannu ya kar6a yadago ya dube ta"thanks, yanzu sai hankalin ki ya kwanta, tunda auntyn naki ta daina kuka" murmushi tadan saki.
"Ki je ki ci abincin ki"
Cikin sanyin murya ta amsa mashi da toh.
Bayan fitar Zeenatu daga dakin Ya maida hankalinsa akan Benazir, A baki ya soma bata abincin tana ci, sai kallon shi takeyi har saida Ya tsargu da kallon Yace"Akwai wani abu ne"?
"Yaya shureim dan Allah ka taimaka ka kaini gidansu Anila Inason ganinta."
"Da yaushe"?
"Ko yanzu kace sai in shirya mu tafi"
"Kin fada mata ne"?
Shiru tayi jim don rabon da suyi waya da Aneelerh kusan two weeks babu wanda ya tuntubi wani amma saboda tana son Taje din yasa tay mashi karyar sunyi waya harma ta fada mata zasu zo
Yace toh idan sun kammala Cin abincin zai kai ta.
Dadine Ya lullubeta bayan sun gama cin abincin, Ya fita don yaje ya shirya.
Jikinta na rawa ta dauki waya ta danna ma Anila kira, don ta sanar da ita batun zuwansu, almost 3 times tana doka mata kira ba'a picking a karshe ta hakura da kiran nata ta fada toilet don tayi wanka.
*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE🔥✍️*
*Game bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08169856268 ko 08103884440*
[14/10, 6:06 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Health College
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe page 61 Complete by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
September 29, 2024
Sponsored Link
Takun Ƙarshe
Zaune yake a mazaunin driver na motarsa, ita kaɗai ya ke jira su tafi, har ya fara gajiya da jiran ta, wayarsa ya zaro daga front pocket din rigarsa ya danna mata Call.
"Idan kika ƙara minti ɗaya baki fito ba zan koma ciki ne." Yana fada yayi rejecting call ɗin, jingina kanshi jikin headrest ya yi tare da lumshe idanun shi.
Sam bai ji tahowarta ba, sai dai ya ji motsin buɗe cardoor din, buɗe idanunsa yai tare da kallon ta baki a buɗe ganin yadda ta ca6a ado kamar wadda zata je gidan surukanta, Wani hadadden Code lace ta saka orange riga da skirt sun ɗan kama jikinta, mayafin kayan a kafaɗa ta daura shi, ga wani hadadden daurin dan kwali da ta yi, baƙar sumar kanta ta sauko har mid back dinta, fuskarta ta sha make up....,sunkuyar da kai ƙasa ta yi ganin kallon da Dr Shureim ɗin ke yi mata.
"Benazir, wa ki kai ma kwalliyar nan? sai ka ce wadda zata je bikon mijinta?" Tuntsirewa ta yi da dariya, ta yi mamakin jin ya canki abunda ta shirya, don wannan kwalliyar da ta yi saboda Taj ta yi ta, yau ta ɗaura ɗamarar janyo hankalin shi gare ta.
"Zai iya yiwuwa."
ta faɗa tana sakin murmushi, ta6e baki ya yi tare da ɗan girgiza kan shi ba tare da ya kawo komai a ransa ba, Kafin ya yi wa motar key a hankali ya yi reverse, a tsanake Ya ke yin driving ɗin su...
"Zeenatu ta ganki da zaki fito daga gidan?"
Ya tambaya yayin da yake juya sitiyari.
"Eh, amma bata nuna zata bini ba, naji tace zata bi Aunty Sarah Office, may be shiyasa bata damu da ta biyo mu ba."
Tafiyar mintuna ƙalilan Suka ƙaraso layin su Aneelerh, Bayan Baba mai Gadi Ya buɗe masu gate Dr Shureim ya shigar da motar ciki, a parking space ya dakata.
"Mu shiga ciki" Girgiza kai ya yi, "ki fara shiga zan shigo daga baya" amsa mashi tayi da toh,
Fitowa ta yi ta nufi cikin gidan, bakinta ɗauke da sallama ta shiga...
"Muryar wa nake ji kamar Benazir?" Murmushi ta saki tare da sauke idanunta akan Mami da Ummi dake zaune a falo suna kallo a tv, gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta bayan sun amsa sallamar da ta yi...
"Wlh ni ce Mami, na yi maku zuwan bazata ban kira na faɗa ba" ta fada tare da karasawa ta dan duƙa gaban sofa ɗin da suke a zaune ta gaishe da su.
"Ina wuninku, fatan na same ku lafiya"
A tare suka haɗa baki "lafiya lou, ya mutanan gidan naku?"
"Suna nan lafiya, Sun ce agaishe masu da ku."
"Ina Zeenatu da Shureim namu"? A cewar Mami,
"Yaya Shureim shi ya kawo ni, yana a waje, shi ya ce in fara shugowa zai biyo ni, mun baro Zeenatu a gida za su je office tare da Mommynta."
Shigowa dakin zeenatu tay, jikinta sanye da jallabiya fara.
Ganin Benazir zaune ta kife kai gaban mirror yasa ta nufe ta.
"Aunty Benazir, lunch is ready, we're waiting for you" ta fada tare da karasawa gaban ta.
Jin shiru bata dago ba yasa zeenatu tayi tunanin ko bacci ta ke yi.
Dafa bayanta tayi"aunty Benazir, Wake up pls, " taji tayi shiru bata tanka mata ba.
tasan in har ba magana ta yi mata ba, ba tafiya za ta yi ba, a yanzu bata son kowa a kusa da ita tafi son kadaici.
"Zeenatu! Pls ki kyale ni, basai kun jira ni ba, Ki tafi kawai ku ci abincinku,"
ras gabanta ya dan fadi jin yadda Benazir take magana cikin shesshekar kuka arude ta furta"Aunty Benazir! Meke damunki? Baki da lafiya"?
Bata san sa'adda ta daka mata tsawa ba"bansani ba, Zeenatu! Nace ki kyaleni, Ki rabu dani, bana son ganin kowa akusa dani..."
zazzare blue eyes dinta tayi, abunka ga shagwababba ta fashe da kuka ta juya ta fuce da gudu ta nufi dining area.
A lokacin Mami da Hajiya sarah tare da Dr shureim da Alhaji Ubaida suna azaune kan dining Chairs har sun fara cin abincin, Kukan zeenatu ne yaja hankulansu ga dubanta, azabure suke mike suna kallonta, Ta na karasawa ta fada jikin mommynta tana ci gaba da kuka, Hankali atashe suka dubi juna kafin suka maida idanunsu akanta.
" Zeenatu meya faru? Ina Benazir din? Wa ya tabaki"? Alhaji ubaid ne ya tambaya.
Mami tace"ki bude baki kiyi magana mana! Wani abunne Ya hadaki da Benazir dinne"?
Dago da ita Hajiya sarah tayi"Daughter, Daina kuka, Fada min meya faru"! Cikin kula tayi maganar tana share mata hawayen fuskarta
Cikin shesshekar kuka tace"Ah.. an.. aunty Benazir ce take kuka, Nace tazo muci abinci shine ta daka min tsawa tace in tafi bata son ganin kowa a tare da ita"
Dr shureim bai tsaya ya karasa sauraron maganar Zeenatu ba, Ya zame jiki Ya nufi dakin Benazir tunkafin Ya karasa shiga Ciki yajiyo sautin kukanta, gabansa na faduwa ya afka ciki Ta cikin madubi Ya hango fuskarsa sharkaf da hawaye ta zabga uban tagumi kamar wadda ta rasa gata a duniya, da sauri ya nufe arude ya furta Benazir! Lafiya kike kuka? Meke damunkin ki ne?
mikewa tayi ta nufe shi ta kwantar da kanta saman kafadar shi tana kuka, bubbuga bayanta ya somayi da hannunsa cikin sigar lallashi yace"pls ki fadamin damuwarki, Zan taimaka maki mu nemi mafita, amma kukan nan bazai amfane ki da komai ba, saima yajaza maki ciwon kai"
dakyar ta hadiye kukan tace"yaya shureim ina ma mutuwa zata zama hutu agareni wlh dana mutu na huta, nagaji nagaji da azabtarwar da zuciya keyi min akan rashin mijina da yata, yaya shureim bana jin dadin komai, hankalina ba akwance yake ba, Ina so nagan su..." dakyar ta karashe maganar..
Gaba daya a kunnan su Mami da basu dade da shugowa dakin ba, Gaba dayansu sunyi tsaitsaye cirko cirko suna sauraron maganar Benazir, tausayinta ne ya kamasu mami tuni idanunta sun ciko tab da kwalla, batasan ya zatay ba, ita kanta zataso Benazir ta hadu da bayin Allahn nan ko ta samu nutsuwar hankali..
Zeenatu dake kuka kalaman benazir sun karya mata zuciya, wani kukan takuma fashewa da shi.
"Benazir, Kiyi hakuri, Ki kara jurewa dan Allah, Na roke ki, sanya damu arai bazai haifar maki da komai ba, saima ta fama maki raunin dake a cikin zuciyarki, bana so a koma yar gidan jiya, dan Allah Benazir kiyi hakuri zamu tayaki da addu'a kema ki dage in sha Allah zasu bayyana"
Hajiya sarah ce ta yimaganar cikin sanyin murya.
Girgiza kai Alhaji ubaid yai shi kanshi abun na damun shi.
"Kinga kukan Ya isa haka, Kiyi shiru, in sha Allah Idan Uncle dinku ya dawo zanyi magana da shi ya taimaka yasa a yi cigiyar su agidan jaridu watakil adace..."
gaba daya tunaninsu har yanzu babu labarinsu ita kadai tasan Da zaman su..
A hankali ta dago daga kan kafadar dr shureim Idanunta sun kada jawur ta dube su ji take kamar ta fada masu Taj da Unaisah suna nan kuma tasan inda suke, ko dan ta samu su tayata neman yafiyarsa.
Girgiza kai tayi"nagode da kulawarku agareni, Amma basai an yi cigiyarsu a gidan jaridu ba, Aneelerh ta fada min sunyi iyakar bakin kokarinsu gurin yada hotunansu a social media da Gidan jaridu amma har yau babu labarinsu...." ta dan dakata kafin ta daura da cewa"dan Allah kada ku damu da halin da nake a ciki, bawai don banyi imani da kaddara ba, wlh nayi kokarin In manta da su a cikin zuciyata amma abun Ya faskara..."
ta faɗa tana matse kwalla.
Kallonsu Dr shureim yayi"pls Ku barni da ita, ku je ku ci abincinku, Zan yi mata nasiha" Alhaji ubaid yace"yawwa shureim pls kayi kokarin shawo kanta, bana so ciwonta ya tashi" amsa mashi yai da toh, fita su ka yi ya rage saura su uku
Kallon zeenatu yayi, Tana atsaye bakin kofar sai shesshekar kuka take.
"Calm down your mind, Ki kawo min lunch din ta a daki" ta amsa da toh ta juya ta fuce..
Ruko hannunta yai suka zauna kan gadon ta.
Nasiha ya farayi mata cikin kwantar da murya har saida taji zuciyarta ta dan lafa da radadin da takeyi mata.
Sai da yaga ta samu nutsuwa sosai kafin yace"akwai inda ke maki ciwo" girgiza ma shi kai tay"a'a ya shureim, lafiyana lou"
"Okay, " ya fada tare da sauke ajiyar zuciya.
Shigowa zeenatu ta yi cikin dakin, hannayenta ruƙe da tray mai dauke da lunch ta mika ma dr shureim Yasa hannu ya kar6a yadago ya dube ta"thanks, yanzu sai hankalin ki ya kwanta, tunda auntyn naki ta daina kuka" murmushi tadan saki.
"Ki je ki ci abincin ki"
Cikin sanyin murya ta amsa mashi da toh.
Bayan fitar Zeenatu daga dakin Ya maida hankalinsa akan Benazir, A baki ya soma bata abincin tana ci, sai kallon shi takeyi har saida Ya tsargu da kallon Yace"Akwai wani abu ne"?
"Yaya shureim dan Allah ka taimaka ka kaini gidansu Anila Inason ganinta."
"Da yaushe"?
"Ko yanzu kace sai in shirya mu tafi"
"Kin fada mata ne"?
Shiru tayi jim don rabon da suyi waya da Aneelerh kusan two weeks babu wanda ya tuntubi wani amma saboda tana son Taje din yasa tay mashi karyar sunyi waya harma ta fada mata zasu zo
Yace toh idan sun kammala Cin abincin zai kai ta.
Dadine Ya lullubeta bayan sun gama cin abincin, Ya fita don yaje ya shirya.
Jikinta na rawa ta dauki waya ta danna ma Anila kira, don ta sanar da ita batun zuwansu, almost 3 times tana doka mata kira ba'a picking a karshe ta hakura da kiran nata ta fada toilet don tayi wanka.
*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE🔥✍️*
*Game bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08169856268 ko 08103884440*
[14/10, 6:06 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite
Health College
Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe page 61 Complete by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
September 29, 2024
Sponsored Link
Takun Ƙarshe
Zaune yake a mazaunin driver na motarsa, ita kaɗai ya ke jira su tafi, har ya fara gajiya da jiran ta, wayarsa ya zaro daga front pocket din rigarsa ya danna mata Call.
"Idan kika ƙara minti ɗaya baki fito ba zan koma ciki ne." Yana fada yayi rejecting call ɗin, jingina kanshi jikin headrest ya yi tare da lumshe idanun shi.
Sam bai ji tahowarta ba, sai dai ya ji motsin buɗe cardoor din, buɗe idanunsa yai tare da kallon ta baki a buɗe ganin yadda ta ca6a ado kamar wadda zata je gidan surukanta, Wani hadadden Code lace ta saka orange riga da skirt sun ɗan kama jikinta, mayafin kayan a kafaɗa ta daura shi, ga wani hadadden daurin dan kwali da ta yi, baƙar sumar kanta ta sauko har mid back dinta, fuskarta ta sha make up....,sunkuyar da kai ƙasa ta yi ganin kallon da Dr Shureim ɗin ke yi mata.
"Benazir, wa ki kai ma kwalliyar nan? sai ka ce wadda zata je bikon mijinta?" Tuntsirewa ta yi da dariya, ta yi mamakin jin ya canki abunda ta shirya, don wannan kwalliyar da ta yi saboda Taj ta yi ta, yau ta ɗaura ɗamarar janyo hankalin shi gare ta.
"Zai iya yiwuwa."
ta faɗa tana sakin murmushi, ta6e baki ya yi tare da ɗan girgiza kan shi ba tare da ya kawo komai a ransa ba, Kafin ya yi wa motar key a hankali ya yi reverse, a tsanake Ya ke yin driving ɗin su...
"Zeenatu ta ganki da zaki fito daga gidan?"
Ya tambaya yayin da yake juya sitiyari.
"Eh, amma bata nuna zata bini ba, naji tace zata bi Aunty Sarah Office, may be shiyasa bata damu da ta biyo mu ba."
Tafiyar mintuna ƙalilan Suka ƙaraso layin su Aneelerh, Bayan Baba mai Gadi Ya buɗe masu gate Dr Shureim ya shigar da motar ciki, a parking space ya dakata.
"Mu shiga ciki" Girgiza kai ya yi, "ki fara shiga zan shigo daga baya" amsa mashi tayi da toh,
Fitowa ta yi ta nufi cikin gidan, bakinta ɗauke da sallama ta shiga...
"Muryar wa nake ji kamar Benazir?" Murmushi ta saki tare da sauke idanunta akan Mami da Ummi dake zaune a falo suna kallo a tv, gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta bayan sun amsa sallamar da ta yi...
"Wlh ni ce Mami, na yi maku zuwan bazata ban kira na faɗa ba" ta fada tare da karasawa ta dan duƙa gaban sofa ɗin da suke a zaune ta gaishe da su.
"Ina wuninku, fatan na same ku lafiya"
A tare suka haɗa baki "lafiya lou, ya mutanan gidan naku?"
"Suna nan lafiya, Sun ce agaishe masu da ku."
"Ina Zeenatu da Shureim namu"? A cewar Mami,
"Yaya Shureim shi ya kawo ni, yana a waje, shi ya ce in fara shugowa zai biyo ni, mun baro Zeenatu a gida za su je office tare da Mommynta."