← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 238

Sashe 74

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 7 min read

Fitowa daga kitchen Ana tayi hannunta ɗauke da tray na kayan abincin da suka shirya masu har zata gifta ta ɗan dakata tare da kallon baƙin nasu karaf idanunta suka sauka akan fuskar benazir, tsabar kiɗima da ganin Benazir Ƙiris Ya rage ta saki kayan abincin hannunta Jikinta Ya hau bari da sauri takai abincin Dining ta nufo su, gaba ɗaya ta zube kan carpet tana ambaton sunan Benazir,

Kusan atare suka ɗago suna kallonta duk tabi ta ruɗe muryarta na rawa take faɗin "Aunty Benazir! Kece? Ko dai makuwa nayi ne?"

Hawaye ne suka ciko idon benazir bakomai Ya faɗo mata aranta ba face Irin azabtarwar da tayi ma yar'uwar Ana mai aikin gidanta Janet taci azaba a hannunta in tai mata laifi hada duka take haɗa mata,

Cike da jin kunyar Ana tace"Ni ce Ana, ba makuwa kikai ba, fatan na same ki lafiya? Ina yar uwarki janet"

Matse ƙwalla Ana tayi "Allah Sarki Aunty Benazir Ina nan lafiyalou, Janet tana a Jos tare da Esther ni kaɗai ce anan, Aunty Benazir Ina kika shiga tsawon lokaci bamu ji ɗuriyarki ba..."

Kafin benazir ta bata amsa Aneelerh tayi saurin tarar numfashinta da cewa "Ana kije ki ƙarasa shirya masu abincin, zanyi maki bayanin komai" ta faɗi hakanne saboda bata son ana tayi maganar 6acewar su Angel gudun kada Benazir taji hankalinta Ya tashi,

"Kada ki damu, zuwa anjima kafin mu tafi zan nemeki..." amsawa Ana tayi da toh, Jiki asanyaye ta miƙe tana tafiya tana waiwayon su Benazir tana mamakin Matashiyar da suka zo da ita, aranta ta ayyana watakil itace Yar uncle ɗinsu da taji ance zasu zo da ita...har sai da ta shige kitchen tukunna ta daina kallon su,

Miƙewa Aneelerh tayi tare da kallon Benazir tace "mu shiga daga ciki",

Mami tace "kuyi me? Ba zaki bari su ci abinci ba, salon ki cika ta da surutu"

"Ba daɗewa zamu yi ba Yanzu zamu fito"

Ummi tace"ke ko an daɗe ba'a haɗu ba, tana son su ɗan ke6e ne ay firar yaushe rabo",

miƙewa Benazir tayi suka nufi bedroom ɗinta hannunsu cikin na juna,

"Shureim ya'yanka nawa Yanzu" sunnar dakai ƙasa yai jin tambayar da Mami tayi masa,

Dariya tayi "dan Allah kada kace min bakai aureba"

Cike da jin kunyarta Yace "banyi ba Mami, amma nakusa in sha Allah" tayi mamakin jin maganarsa gashi har ya fara manyanta baiyi aureba koda Yake komai sai Allah Ya nufa,

"Allah Ya tabbatar mana da alkhairinsa" amsa mata su kai da ameen,

Shigowa Ana tayi "Mami na gama shirya abincin"

Mami tace"toh, ku tashi mu ƙarasa Ciki" Dr Shureim Yace"Alhamdulillah, bana Jin yunwa sai dai ko Zeenatu in zata ci"

Maƙe kafaɗa Zeenatu tayi "nima bana jin yunwar ay naci abinci agida" yadda tai maganar yaso basu dariya har sun gane shagwa6a66iyace

"Haƙuri zukuyi ku tashi muje, Nasan baza'a rasa space a cikin ku ba ko ruwan zumunci ne ku sha" lalla6a su Ummi tayi har dai suka miƙe suka bi su Mami zuwa dining..

A 6angarensu Benazir bayan sun shiga ɗaki da Aneelerh, cike da zumuɗi suka zauna daga gefen gado

Sai faman bin juna da kallo suke yi kamar yau suka fada haɗuwa

"Kinga yadda kika canza? Kin ƙara girma kinyi kyau abunki, bani labari bayan kin tafi ina kika faɗa"?

Numfasawa tay kafin tace"Wani bawan Allah ne Ya taimaki Rayuwata, Mutumin kirki, ɗan family ɗin Obinna nasan ba zaki rasa saninsa ba, sunan shi Zaki Mubarak Obinna A ƙasar Canada Yake..." gaba ɗaya Benazir ta bata labarin Yadda suka haɗu da zaki a Abuja bayan ta gudu daga jos da yadda harya taimaketa suka bar kasar atare..

Jinjina kai Aneelerh tayi har cikin ranta taji dadi da rayuwar benazir bata wulaƙanta ba,

"Koma wanene Yayi miki wannan aika aikar in sha Allah sai yaga sakayya, tun agidan duniya, anso a cutar da rayuwarki, da yake Allah ba azzalumin bawansa bane cikin ikonsa kin faɗa hannu nagari",

"Ni inda nagode ma Allah, ban tafi da tsohon ciki na ba, da bansan a Ina zan haife shi ba, ba rabon ƴata tasha wahala wlh banyi zaton zata rayu ba, inaji ina gani nabarta a kwamin wanka tana kuka tana kallona..." kuka ne Ya ci karfinta da sauri Aneelerh ta fara lallashinta

"Ni damuwana wanene yake kokarin ganin ya rabani da dangina? Me na masa Aneelerh? Nasan bana jin magana tun a ƙuruciyata inada jan faɗa da masifa, mutane da dama na sanya su ciwon kai har da masuyi min mummunan fata amma wallahi ban ta6a zaton za'a samu wanda zaiyi min asiri, to waini me nayi masu haka??" idanunta jawur ta faɗa.

Dafa kafadarta Aneelerh tayi"in sha Allah duk wani mai nemanki da sharri kanshi zai koma, ubangiji Allah Ya tona asirin su"

"Ameen Aneelerh nagode sosai da kulawarki agareni, ni wlh banyi zaton zaku kar6e ni hannu biyu idan na dawo ba, ko gida da zan dawo nayi fargaban haɗuwa da su Daddy amma saina ga kowa Yana murnar gani na ba ƙaramin daɗi naji ba, yanzu damuwana ɗaya shine mijina da ƴata ina matuƙar jin shakkarsu saboda nasan da wuya su kar6eni hannu biyu kamar yadda kukai min..."

"Meyasa zaki ce haka? ay su sai sun fi kowa murnar ganinki"

Girgiza kai tay"ba zaki gane ba Aneelerh, bayan tafiyata lokacin ina agidan zaki, kwatsam wata rana saiga saƙon saki daga Taj hakan Ya tabbatarmin da yaji haushin abun da na masa" da mamaki Aneelerh tace"kina nufin bake kika nemi saki daga wurinsa ba?"

Ɗaga mata kai tay alamar eh, shiru Aneelerh tayi jikinta Ya ƙara mutuwa lakwas saboda taj da kanshi Ya ta6a faɗa mata Benazir ta tura masa text message tana neman ya saketa, to kenan wanene Ya shirya wannan tuggun?" Ta jafe ma kanta tambayar da bata da amsarta,

Ruƙo hannayenta Benazir tayi a cikin nata ta damƙe su sosai cikin sanyin murya tace "Dan Allah Aneelerh ki taimaka min Inason yin magana da tajuddeen, naji kince baki da layin da Yake amfani da shi, tun da suna a tare da mijinki dan Allah ki kira Uzair ɗin sai mu yi magana da shi..." Rass Aneelerh taji gabanta Ya faɗi, tuni ta nemi nutsuwarta ta rasa, batasan taya zata shawo kan Benazir ba sam ta manta da jiya ta faɗa mata hada mijinta suna a South Korea,

"Kinyi shiru baki ce min komai" ta faɗa idanunta acikin na Aneelerh, farat ɗaya ta fahimci wani abu daga yanayin da ta nuna, Wani irin kwarjini Benazir tayi mata muryarta da inda inda ta shiga faɗin "am..umm..bani da layin shima uzair...au wayarshi ta lalace zan ce....." bata ƙare maganar ba ta katse ta da cewa "Kada kiyi min karya Aneelerh ba halinki bane, dan Allah ki faɗamin gaskiya ni dama najima ina kokwanton maganar mami, daga baya sai da raina ya bani akwai wani abu da take boyemin don itama lokacin dana tambayeta lambar Taj tunda nasan bata rasata ba kamar da suka bayyana man cewa suke kula da yarinyata lokacin dana dawo amman sai ta nuna man basu da lambarshi ta inda yake, tun nan na fara shakkun maganar ta tunda ko don saboda yarinyar tawa ai ya kamata ace suna da lambar tashi da suke magana, kawai ki faɗamin in da akwae wani abu nayi maki alkawarin bazan tada hankalina ba, boyemin bashi da amfani tunda duk min daren daɗewa zanji ne kuma bazan ji daɗin ƙin sanar man da kuka yi ba...."

Jinjina kai Aneelerh tayi tuni taji ƙwalla ta cika idanunta don har yanzu zuciyarta da ciwon abun,

Numfashi taja kafin ta fara bata labarin abun da Ya faru na 6acewar su Tajudeen,

Tsabar tashin hankali Yasa Benazir saukowa daga zaunan da take a gefen gadon ta dawo kan floor dirshan ta ɗaura hannayenta biyu asaman kanta muryarta cike da tashin hankali take faɗin "INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJU'UN! INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHIRRAJU'UN......" Misalta tashin hankalin da zuciyarta ta fuskanta ba abune mai sauƙi ba, Idanunta sun kaɗa jawur facial muscle dinta har kerma take gaba ɗaya jikinta ya ɗau wani irin mahaukacin zafi kamar mai fama da zazza6i sai kerma take,

Dafa kafaɗarta Aneelerh tayi muryarta a raunace ta furta "Innallaha ma'assabirin Iya abun da zan iya furta maki kenan, abun da Ya faru Ya riga daya faru Benazir, illa iyaka mu cigaba dayi masu addu'a ubangiji Allah Ya bayyanar mana da su tunda har Yanzu babu labarin suna araye ko sun mutu,

Cikin shesshekar kuka Benazir take faɗin "nashiga uku Aneelerh! Meke faruwa da rayuwata ne? Da farko An rabani da dangina hakan bai isa ba sai da akayi silar da ƴata da mijina suka 6ace! Wai wanene ke bibiyar rayuwarmu ne? Uban me muka masa...." jin Yadda take ɗaga Murya Yasa Aneelerh saurin toshe mata baki da tafin hannunta gudun kada su Mami su jiyota....

A ƙarshe ma sai ta rungumeta saboda ta samu relief ɗin abunda ke damunta

Allah kaɗai Yasan tafarfasar da zuciyarta keyi mata kamar numfashinta zai ɗauke bakomai take tunawa ba face fuskar Taj dana yarta Unaisah yanzu shikenan ta rasa su?
Chapter 74 · 0% Book details