← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 166 OF 238

Sashe 166

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Good morning everyone, i'm director Owais Sharafudeen Obinna, the Chief of Isod, With me are my team members," ya faɗa tare da yin nuni da su,

"Deputy Director General Omar Musa Wadata, Chief of Operations Ahmad Hassan, Chief of Intelligence Commander Haroon, and Senior Agents Dr. Zarah Saeed, Agents Ethan Kim and Jabeer Osman."

yanayin yadda yake gabatar da su ba ƙaramin burge su yayi ba komai nashi cikin aji yake yin shi, duk wanda ya ambaci sunanshi zakaga ya saki ƙayataccen murmushi kan fuskar shi..

"Muna yiwa kowa barka da zuwa" ya fada tare da komawa kan kujerarsa ya zauna suma duk suka zauna.

The next person General Noah ne wani bayerabe baƙi mai jiki ya miƙe yana gyara necktie ɗinsa,

"Hello everyone, nice to meet you all, I am General Noah the General Officer Commanding the Nigerian Army, It's an honor to be here today." ya faɗa fuskar shi da murmushi kafin ya koma ya zauna.

Cike da kwarin gwuiwa Commender James Ya miƙe tare da tawagarsa su shidda,

"Hello everyone, I am Colonel James, the U.S. Commander of the Joint Task Force. I am joined by my team.." ya faɗa tare da nuna U.s armies din dake gefen shi,

Ya fara zayyana sunayen su,

"Major Smith, Captain Lewis, Canal herry and Lieutenant Thompson tare da Jackson lee, munayi ma kowa barka da zuwa, mun ji daɗin gayyatar mu da ku ka yi" gaba daya sunji dadin gabatarwar da yayi bayan sun zauna ɗakin yayi shiru na ɗan wani lokaci.

Kafin Chief ya numfasa calmly ya cigaba da kora jawabi, "Thank you, everyone, Let us proceed with the agenda, we are gathered here today to discuss a grave and urgent matter, already mun riga da mun san abun da ya tara mu, dangane da yaran da sojojin America suka tsinta a dajin Evil forest suka damƙa case dinsu a hannun hukumar mu ta Isode..."

gaba ɗaya sun nutsu suna sauraron shi hadi da kallon fuskar shi,

Ɗan dakatawa yayi kafin ya daura da cewa, "...bayan bincike da hukumarmu tayi mun samu bayanai daga gurin yaran, wato wasu miyagun matsafa ne suka ƙirƙiri wani gini a karkashin ƙasa wanda suke kira da Gidan Kurkukun kaddara! Inda suke kulle mutanan da basu ji ba basu gani ba ta ƙarfi da yaji suke killace su, anan suke aikata duk wani fasadin su.." gaba ɗaya hankalin Jami'an ya karkata akan shi cos ba komai suka sani dangane da yaran.

"But that's not all, bayan ƙuntata rayuwar yaran, suna azabtar da su azaba mai raɗaɗi, ta hanyar yin amfani da karfin sihirin su gurin sarrafa su, su yi amfani da su ta ƙarfi da yaji..."

"But that's still not the worst of it. They use these innocent children as sacrifices for their dark magic rituals, draining their blood and exploiting their suffering for their own gain. And, tragically, they have been known to target young girls during their period, subjecting them to... unspeakable atrocities..."

kasa ƙarasa maganar yayi saboda takaici da baƙin ciki da ya mamaye zuciyar shi, tuni gumi ya fara tsartsafo mashi akan fuskar shi,

haɗa ido su ka yi da commender kasancewar suna fuskantar juna, tun daga kan yanayin yadda ya ƙura mashi ido ya fahimci maganar da yayi tayi matuƙar girgiza shi, a ƙagare yake da son jin karin bayani, hatta sojojin sun yi matuƙar girgiza da jin maganar kurkukun ƙaddara.

Mamakinsu wai har za'a samu yan adam da zasu iya shirya mugunta da zalunci a ƙarƙashin ƙasa na tsawon lokaci batare da asirin su ya tonu ba?

"Owais, kai muke sauraro, Muna bukatar ƙarin bayani daga gurin ka." General Noah ne ya yi maganar...

Cikin sanyin murya ya amsa mashi da Okay, kafin ya kunna laptop din gabanshi ya fara operating ɗinta nan take large screen ɗin dake a jikin bangon dake fuskantar su ya kawo haske kamar tv nan take ya yi displying video ɗin su Unaisah a Questioning room wato ɗakin tambayoyi, lokacin da suke bada bayani dangane da rayuwarsu agidan kurkukun ƙaddara komai da suka tattauna camera ta naɗe shi.

Yayin da suka nutsu suna sauraron tattaunawar su, wata irin zufar bacin rai da tashin hankali ce ta wanke goshin su kamar ba A .c a dakin, wlh sun yi matuƙar kiɗima da jin labarin kurkukun ƙaddara da kuma irin mugunyar azabar da ake yi ma matasan yaran da basu ji ba basu gani ba... tsabar fusata da baƙin ciki da takaici yasa jikin commender ya fara tsuma yana zubda gumi.

Bakomai yafi Karya masu zuciya ba face Labarin Unaizah da Majnoon duk irin dauriyar Soja saida ruwan hawaye suka cika idanuwansu kamar zasu fashe da kuka,

Dunƙule hannu General Noah yayi ya dinga bugun gaban table din yana cizon lower lips dinshi, saboda tsabar fusata.

Commender James kuwa da shi da tawagar shi tsantsar mamaki da al'ajabi Ya hana su ko motsa, sai faman jinjina kawunansu suke yi al'amarin ya girmi tunaninsu, su mamakinsu yadda har matsafan suka share tsawon lokaci suna aikata 6arna a ƙasa batare da an iya kama su ba, a ganinsu sakacin shuwagabannin ƙasarne da kuma waɗanda keda alhakin kula da tsaron ƙasar"

Jikin kowannansu yayi mugun yin sanyi lakwas, ɗakin taron yayi tsit baka jin sautin komai saina muryoyin su Unaisah.

Murya na rawa General Noah Ya furta"Owais, I can't believe what I'm hearing. Am I not dreaming? What cruelty and evil? I have never heard of such a thing before! a kasar nan wannan tashin hankalin ke faruwa batare da saninmu ba? Toh meye amfaninmu? Nayi danasanin mukamin da nake dashi tun da har ban iya kawo karshen ta'addanci a kasar nan ba, bamu ba al'umma tsaron da ya dace ba..."bai ƙare maganar ba saboda ƙululun baƙin cikin da ya tokare maƙoshin shi. da sauri Canal dake gefen shi ya dafa kafaɗarshi cikin sigar lallashi ya fara ƙoƙarin kwantar mashi da hankali.

Cikin sanyin jiki chief Owais Ya zaro hanky daga front pocket ɗinsa Ya miƙa ma general Noah ganin yadda yake zubda gumi yatsun hannunsa na kerma Ya kar6a ya fara share hawayen dake sintiri kan kuncin sa..."

"Owais lamarin Ya ɗaga hankali na! Wai dagaske ne Yana faruwa?"

Commender James ne ya yi maganar tsabar ruɗin tashin hankali yasa shi jin al'amarin kamar almara.

Jinjina mashi kai ya yi alamar eh ba tare da ya iya furta kalma ba.."

Gaba ɗaya saida ya kunna masu videos ɗin prisoners lokacin da aka zo kan nasu Jemimah kifa kai general Noah yayi kan table ɗin kamar zai fasa ihu saboda tsananin tausayin yaran, kukan zuci yake mai azabar radadi.

Babban abun takaicin da ya haddasa matsananciyar damuwa a zuciyarsu yadda matsafan suke lalata rayuwar ƙananun yaran saboda rashin imani a lokacin da suke tsaka da raɗaɗin ciwon cikin jinin al'ada.

Bayan haka sun karaya da jin irin kullan da suke yi masu tun suna jarirai babu shige babu fuce, abinci sau ɗaya a rana, kaya kala ɗaya, sun ƙasƙantar da rayuwarsu sun tauye masu hakkinsu na rayuwar duniya sun maida su kamar dabbobi.

"Wlh, na rantse da wanda raina yake a hannun shi, mutanan da suka ƙirƙiri gidan kurkukun ƙaddara ba zasu ƙara shaƙar numfashi cikin kwanciyar hankali ba, ɗaya daga cikin su bazai sha ba, idan har suka kuskura suka zo hannu wlh sai sunyi danasanin haihuwarsu da uwayensu suka yi a duniyar nan, sai sun ɗanɗani kuɗarsu sai sun manta da duk wani jin daɗi da suka ta6a ji a duniyar nan..." a harzuƙe Noah ya faɗa kamar ana tunzarashi da ƙyar suka lalla6a shi ya koma ya zauna yana faman yin haki kamar wanda yasha gudu...

Shiru suka yi na ɗan wani lokaci, batare da wani ya ƙara furta uffan ba, ƙoƙari suke su kwantar da hankalunsu don su samu nutsuwar faɗin ta cikin su, tashin hankali ya hana ko ruwan sanyi su kora ma maƙoshin su.

Muryar Big guy ce ta katse shirun nasu

"Abunda muka gano dangane da kungiyar matsafan, sadaukarwa da su ke yi, dole sai danginka, mutun ba zai iya sadaukar da wanda bai haɗa alaƙar jini da shi ba".

Girgiza kai Dr. zahra ya yi, "Banma san me zance ba, mutanan nan sun san me suka taka, kuma daga ji manyan mutane ne a ƙasar nan, shiyasa suka daɗe suna aikata ta'addanci batare da asirin su ya tonu ba..." Maganar Dr. Zahra ta ɗaga hankalin Chief Owais da Big guy saboda sunsan su wanene ke ruƙe da ƙasar wato family ɗin su.

"Mutane ne masu hatsarin gaske, tunkarar su ba abune mai sauƙi ba, ta ya za'ae ma mu san su wanene su balle har mu iya kawo ƙarshen su? Babban abun da ya ɗaure mana kai yaran gaba ɗaya ba su ta6a ganin fuskokinsu ba, hatta shi babban cikin su Salsabeel da ya fi su daɗewa a gidan kurkukun, kai hatta yaron da ke ruƙe da muƙamin garkuwarsu, ya rayu tsawon shekaru baisan fuskokinsu ba amma yasan Nicknames ɗin su, saidai yaƙi faɗa mana komai dangane da su, yana da taurin kai, mutunne mai wuyar sha'ani, ɗan uwansa Salsabeel ya faɗa mana cewa yafi shi sanin su wanene elders..." Big guy ya ƙare maganar yana dubansu.

Ci ya ɗaura da cewa, "Har yanzu suna sarrafa shi, mawuyacin abune ya bamu haɗin kai, ɗan uwansa yace in har muka tursasa mashi zai iya ja mana gagarumar matsalar da bazamu iya magance ta ba..."

Agent Jabeer Osman ya ɗaura da nashi bayanin, "Matsafan suna da kaifin basira da wayau, sun san cewa wata rana asirin su zai iya tonuwa shiyasa basu ta6a yin kuskuran da wani zai san fuskarsu a cikin yaran da suke raino ba, sun iya takun su..." ya faɗa yana jinjina kan shi.

"Garkuwar nasu Yaro ne mai kafiyar tsiya, bai yarda da bare ba, yan uwansa kaɗai ya sani, amma abun ɗaure kai shine silar ɗaukar yarinyar da suka ruƙa matsayin ƙaddararsu suka kaita gidan kurkukun wanda silar kasantuwarta a gidan ya ja har suka samu shaƙuwa mai ƙarfi tsakaninta da shi garkuwar nasu ta yadda su kan su suka gaza raba shi da ita, silar hakan yaja har ya ku6utar da su daga kurkukun.
Chapter 166 · 0% Book details