← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 150 OF 238

Sashe 150

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tashin hankalin da ba'a saka mashi rana, Salsabeel bai tsaya yaji karashen zancen ba, Ya watsa aguje Ya fuce, Agaggauce Senior agents din suka rufa mashi baya, ya rage saura big guy da chief atsaye suna fuskantar juna

"Meya faru Omar? Meyasa Ya tafi? Wani ya 6ata masa rai ne ko abunda ya faru tsakanin mu ne"?

Dakyar big guy yai karfin halin zayyana mashi abunda ya faru bayan fitowar Danish

Girgiza kai yayi cikin sanyin murya yace"meyasa Omar? Meyasa zaka yi mashi haka? Kamanta wanene shi? Yaron da bai san komai ba yanzu daka bata mi shi rai ina kake tunanin zai dosa? Wa ya sani agarin nan"?
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
Yanayin yadda chief ke yi mashi magana araunace ba karamin karya mashi zuciya yayi ba.

"Duk abun da nayi nayi ne saboda kai, kasan irin kaunar da nake maka, zan iya jure komai amma wlh muddin wani yayi kokarin bata maka rai bazan kyale shi ba, koma wanene.."

"Nasani Umar, amma ni baka kyauta min ba, yakamata kayi amfani da hankalin ka, rayuwar shi abun tausayi ce, tabbas raina ya 6aci da abun da yayi min amma wlh ko kusa ban ji haushin shi ba, saima son shi da ya ƙara ninkuwa acikin zuciyata, yakamata mu yi mashi Uziri bai kamata mu ga laifin shi ba yaron da har yanzu suna iya control dinshi..." bai ƙare maganar ba ya juya cikin takun sauri Ya nufi hanyar fita daga Soc din da sauri big guy yabi bayan shi

*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE🔥✍️*

*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08169856268 ko 08103884440*

YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(302)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
[14/10, 6:06 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: _________________________________✍️

Sautin ringing ɗin wayarta ne ya farkar da ita daga dogon baccin daya ɗauke ta, tana a kudundune cikin lallausan duvet dinta.

da wata irin malalaciyar kasala ta fara ƙoƙarin buɗe idanunta da su kai mata nauyi saboda baccin da tasha ga wani irin tsami da jikin ta yayi mata, lalube ta fara yi tana shasshafa bedmattress din don taji idan yana nan har ta ƙare lalubawa bata ji mutum akan gadon ba, hakan na nufin ya jima da tafiya.

Tunawa da yanayin da take a ciki yasa tay saurin ware idanunta cike da fargaba ta dubi jikin ta zir take ba sutura, lumshe idanunta tayi cike da jin shaukin shi take ɗan jan numfashi, yayin da ƙwaƙwalwarta ke tariyo mata abun da ya faru tsakanin ta da shi a lokacin da suke tsaka da jin daɗin su.

A hankali ta miƙe zaune ta ja duvet din ta lullu6a kirjin ta da shi, kafin ta jingina bayan ta jikin headboard, sumar kanta ta yamutse saboda damƙar da tasha a hannun big boss, ko ina na jikin ta zafi ya ke mata.

idanunta sun kumbura sun kaɗa jajawur, haka la66anta ma sun kumbura don ba karamin tsotsa suka sha ba, ta galabaita sosai har wani jirin kasala take ji a jikin ta.

Kifa kanta tayi kan gwiwowinta tunawa da nasihar da mahaifinta ke yawan yi mata.

"Ke kadai Allah Ya bani mamana, tun kina ƙaramarki bani da burin daya wuce in inganta rayuwarki ki zama hafizar alkur'ani mai ilimin addini da zamani saboda inyi alfahari dake sannan ki zama abun kwatantace, Alhamdulillah cikin ikon Allah sai gashi kin cika min burina ko'ina zancenki ake duk in na shiga cikin jama'a sun dinga yabonki suna fadin ƴata malama ce hafiza mai cikar kamala da kamun kai ga kyautatama al'umma da son taimako, kowa yabon ki yakeyi, burin kowace mace tayi koyi da Aishatu bintu imam malik mace ɗaya tamkar da dubu, Ummi nasihar da zan maki ko bayan ba raina kiji tsoron Allah, kada ki canza daga yadda nasanki, abun da zaki min wanda zaki biyani shi ne Ki karemun martabana da kimata a idon duniya, kada kiyi abun da zai zubda min mutuncina Aishana"

Rushewa tayi da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita, a duk lokacin da ta tuna nasihar mahaifinta zuciyarta ba ƙaramar karaya ta ke yi ba, tana jin tsanar rayuwar data ɗaukarwa kanta, tana mai danasanin abun da yayi silar rabuwarta da mahaifinta, saboda bata da abu mafi soyuwa da ya wuce shi a duniyar nan, kai duk wani gata da ya zata samu agurin ubanta ta samu ninkin baninkin sa.

tana jin raɗaɗin karya alƙawarin mahaifinta da ta yi na kare mashi martabarsa.

kifa kanta tayi jikin pillow, ita kadai baiwar Allah babu mai lallashin ta.

Ba halin ta bane, ba laifin ta ba ne, tana da ilmi tasan zina ba kyau ta kuma san hukuncin wanda ke aikatata amma meyasa takasa dainawa ko da tayi nufin ta tuba ta koma ga Allah? Tasha yunƙurin yin hakan amma aduk lokacin da big boss ya buƙace ta bata iya bijire ma shi.

Ta yi kuka tamkar ranta zai fita kamar ƴar dambe ta dunƙule hannayenta ta dinga bugun mattress kamar zatai hauka ta tsani abunda take aikatawa bata so ta mutu batare da yafiyar mahaifinta ba, kuma batason ta mutu tana aikata sabon Allah tana matukar jin tsoron makomarta.

Ringing ɗin wayarta ne ya dawo da ita hayyacin ta, fuskarta sharkaf da hawaye ta janyo wayar daga kan drawer ta duba sunan me kiranta.

Maji daɗina shine sunan daya bayyana akan screen din, kasa picking call din tayi saboda fushin da zuciyarta ke yi.

Text message ne ya shigo on the top of the screen din wayar, cikin zuciya ta soma karanta abunda ya rubuta mata

_"ummi, na tafi ba tare da nayi maki sallama ba, ki yi hakuri da hakan nasan zaki tashi da kewana, anyi min kiran gaggawane, ba dan nagaji da jin ɗumin jikin ki ba, bazan iya misalta daɗin da kika jiyar dani ba, kin bani cikakkiyar gamsuwa da zan iya ɗaukar kwanaki ban nemi matana ba, bazan iya biyanki ba Ummi, ki fadamin me zanyi maki don in faranta maki"_

Runtse idanunta tayi gam, siraran hawaye suka dinga shararowa kan kuncin ta..

"Ya Allah Ka cire min jarabar son bawan nan naka, Ina neman tsari da shi...."

bata kare maganar ba kwatsam taji dirar motoci acikin gidan, a firgice ta jefar da wayar ta faɗa kan mattress ta duro daga kan gadon, tafin hannunta a tallabe da bargon ta faɗa toilet taja ƙofa ta datse, tana faman zare idanunta, sam ta manta da su Batool tasan bai wuci sune suka dawo gidan ba, abunda take jima fargaba kada wani ya shigo ɗakinta tasan in har suka ga gadonta sai sun zargi wani abu saboda ya 6aci ba kaɗan ba.

Cikin Takun sauri Chief Ya faɗo Falon Ya nufi upstairs, agurguje taj da big guy suka biyo bayan shi, kwata kwata babu kwanciyar hankali akan fuskokin su damuwace ƙarara saboda jami'an da suka tura su nemo Danish kusan awanni har yanzu ba wani labari, har tracking layin sa sukai a karshe suka gano location din da wayar take agida yabar ta baije da ita head quarter din ba, wannan dalilin ne yasa suka yanke shawarar su dawo gidan, watakil su gan shi.

bai nufi ko'ina ba sai bedroom din Danish Yana isa bakin kofar yayi knocking ɗin ta cike da fargaban kada su ki ganin shi.

Jin shiru ba'a buɗe kofar bane yasa shi tureta da hannun shi ya faɗa ciki Yana haki saboda gudun daya sha, bazai iya tuna when last yayi irin shi ba.

da matsanancin faduwar gaba yake bin dakin da kallo wayam babu kowa adakin dafe kan shi yayi da hannu ɗaya idanunshi sun kaɗa jawur babban tashin hankalin shi Ina Danish yaje? ya zai yi da yan uwan shi? Me zai fada ma Uncle hateem idan ya kira yana son yin magana da shi"?

"baya aciki ko"? muryar boss ce ta katse mashi zancen zucin shi
Big guy duk ya rasa kuzarin shi Ya daura ma kanshi alhakin 6atan Danish saboda shi ne silar daya ja har ya yi zuciya Ya tafi, sai yanzu ya ke danasanin bata mashi rai da yayi ganin yadda ya ɗaga hankalin chief Owais.

"Taj bansan ya zanyi ba, baya nan, ya tafi, ya zanyi da raina, bana so na rasa yaron nan wallahi danasan abun da zai faru zuwan mu headquarter da ban tursasa mashi akan yabi mu ba..."

dakyar yake magana saboda damuwar data cika zuciyar shi.

jikinsu yayi mugun yin sanyi.

Cikin raunin jiki ya dubi big guy"Omar, kaga abunda kaja min ko? Idan har yaron nan bai dawo gida nan ba, bazan yafe maka ba..." gaba ɗaya ya rikice masu.

"Sir kayi hakuri, na kar6i laifina, kuma nayi danasanin 6ata mashi rai da nayi, bada son raina ba ya 6ata min rai ne amma nayi maka alkawarin zanje in nemo shi duk in da ya shiga agarin nan..."
Chapter 150 · 0% Book details