Sashe 14
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuskarshi a yamutse ya kalli 6eran da idanunsa masu dauke da bacci, sun kaɗa jawur da su, yayi mamakin da har ta iya kamo 6era, tun da suka fara zama gidan bai ta6a ganin gifcin 6era ba sai yau.
Muryarshi adisashe yace"khadeeja ba zaki barni inyi bacci ba? Ke baki runtsa ba nima kuma kin hana in runtsa, Meke damun ki ne"?
Ta6e mashi lips dinta tayi alamar zata fashe mashi da kuka
Da sauri yace"ya isa ni bance kimin kuka ba, Yanzu fada min ya kikeso ayi da 6eran nan da kika kama"
"Ka cire mashi hannuwa" gyada kai yayi tare da sanya hannu ya kar6i 6eran"ki jira ni yanzu zan dawo amsa mashi tayi da toh, fita yai daga dakin tana atsaye tana jiran shi, badajimawa ba ya dawo hannunsa babu 6eran
"Yana ina"?
"Na cire mashi hannuwa na yar" murmushi tasaki"mun hutu da masifa ko"? Ɗaga mata gira yai alamar eh
"Muje na rakaki daki kiyi bacci" maƙe mashi kafada tayi"Ni yunwa nake ji, kaje kitchen ka dafa min abinci"
Wahalallan kallo yabita dashi gaba ɗaya ta takurasa
"Shikenan muje" Ya fada tare da yin gaba tabi bayan shi suka shiga falo, ta zauna saman sofa.
Kitchen Ya shiga bawan Allah ga gajiyar bacci A haka Ya dafa mata indomie, Ya haɗo mata da water bottle, Ya shigo Da plate din Ya miƙa mata, gefen ta ya zauna don yasan koya koma daki indai batayi bacci ba to shima bazai runtsa ba.
Yana kallonta Har ta cinye taliyar ta kora da ruwa, kwanciya tayi saman sofa din ta daura kafafuwanta saman laps dinshi bai tanka mata ba, yasan rigima take nema, Cikin sa'a bacci yai awon gaba da ita, A hankali Ya zame ƙafafuwanta ya miƙe tare da ɗaukarta ya nufi upstairs da ita, a kan gado ya kwantar da ita, yabi da bargo ya lullu6e mata jikinta, kafin ya fito ya datse kofar dakin nata, cikin sauri ya nufi dakinsa don ya kwanta ya karasa baccin dabai isheshi ba, bayan shigarshi daki har ya kwanta ya soma tunanin ko me ya hana jazz zuwa? Tun safe yake jaraba kiran layin shi baya picking, har ta 6angaren danish ba a kira shi ba wunin yau, fatan shi Allah yasa lafiya da wannan tunanin bacci 6arawo ya ɗauke shi.
*💋BENAZIR❤*
Kwance take a saman darduma, tun bayan data kammala sallar Isha bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita, yayin da zeenatu take a can saman gado tana bacci.
Tana a nannaɗe cikin dogon hijab dinta, tayi nisa acikin baccin ta, Ba zato ba tsammani hasken fitilar bedroom ɗinta ya ɗauke ɗuff, wani iko na Allah ba wutar gidan bace ta samu matsala, ɗakinta ne kadai hasken ya ɗauke, abun ka game bacci sam bata ji alamun hasken dakin ta ya ɗauke ba.
Kwatsam! taji an damƙi wuyanta, tsabar zafin shaƙar da akayi mata ne yasa ta ware idanunta waje, bata iya ganin komai sai duhu baƙi wulik a idanunta
Wani irin mahaukacin bugun fargaba zuciyarta keyi mata, Hankalinta a matuƙar tashe ta soma kokarin kwace wuyanta daga hannun mutumin daya shaƙeta, wuyanta tuni ya soma yi mata zogin azaba, zufa ta ko'ina ta wanke fuskarta, duk yadda benazir taso ta kwace kanta sai dai kash takasa, ga zeenatu kwance saman gado sai dai babu halin da zata iya buɗe baki ta nemi agajin ta, koma wanene yayi mata muguwar shaƙar da ko yatsanta takasa ɗagawa, bakinta tamkar an ɗaure mata shi takasa buɗe shi, hakan yasa tafara kukan zuci tana ambaton sunan Daddy, mommy, yaya shurem, Zeenatu, A karshe ta kamo kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraji"un tacigaba da anbatonta acikin zuciyarta.
Tana acikin wannan mawuyacin Halin har tafara fidda rai da rayuwa kwatsam wayar zeenatu da ta ajiye kan gado ta soma ringing, taken karatun al'ƙur'ani mai girma ne, Kamar Walkiya taji alamun an sakar mata wuyanta, kuma nan take hasken ɗakinta ya kawo, a gigice ta zabura ta miƙe zaune tana faman zazzare idanunta, bin ko'ina na dakin tayi da kallo bata ga kowa ba, Lamarin ya daure mata kai, tagaza gane meke shirin faruwa da ita? Don wannan yafi karfin a kirashi da mafarki, tabbas akwai me son rabata da rayuwarta, lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka tamkar ƙaramar yarinya ita kadai tasan radaɗin da wuyan ta ke yi mata, zeenatu dake ta sharar baccin ta tuni ta soma mutsu mutsun farkawa saboda sautin kukan benazir daya fara addabar kunnuwanta, da sauri benazir ta tsagaita da yin kukan gudun kada zeenatu ta farka taga halin da take a ciki, cikin juriya ta miƙe ta zame hijab din jikinta, ta jefar da shi gefen gado, gaban madubi taje ta tsaya tana kallon wuyanta yayi jawur da shi hada sawun yatsun hannuwan mutun rudu rudu..
Hakika Ta gigita ta kuma tsorata a yanzu ta ƙara tabbatarwa kanta cewa akwai me son ganin bayan ta? Wanene? Laifin me ta aikata da har ake son kashe ta? Zuciyarta ce ta raya mata cewa zai iya yiwuwa jinnu ne, tafi yarda da abun da zuciyan nata ta raya mata saboda babu wanda take zargin zai iya yi mata haka acikin mutanan da take rayuwa da su,ta dai yanke shawarar zata sanarwa yaya shureim ko dan su nemi mafita a tare.
Miryarta na rawa ta furta"Ya Allah ban cutar da kowa ba, Kada ka bada damar da wani zai cutar dani" ta jima atsaye gaban mirror, zuciyarta cike da rudani, ta nufi toilet, tsawon mintuna kafin ta fito jikinta da alamun lemar ruwan da ta watsa ma kanta.
Tunawa da kiran wayar da akai mata ne yasa ta nufi bakin gado ta ɗauko phone din ta soma daddanawa call logs ta shiga nan take taga missed call na bakuwar number din nan
Sai da ta fara kallon agogo, karfe wani abu na dare kafin ta danna call tana faman zazzare idanunta, jikinta nata kerma kamar wadda aka kada ma mazari
Adai dai wannan lokacin Unaisah tana a zaune kan darduma ta zumbula hijabi a jikinta ta ɗaga hannayenta sama fuskarta sharkaf da hawaye bakomai take yi ba face yima danish addu'ar samun lafiya, Batul tana a kwance gefen ta, tun bayan da boss ya tashe su domin yin nafilfilin da za su yi kowannansu bai koma bacci ba, duk suna a dakunansu suna yin sallah, ita dama batul bata da jumurin yin sallah duka raka'a biyu ta samu tayi adaddafe kafin bacci yai awon gaba da ita, shigowar kiran wayar ta ne yasa takai hannu ta dauke ta, a inda ta ajiye ta gefen prayer mat din da suka akai
Ko da tayi tozali da layin da take ta dannawa kira taga da shi aka kirata Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin yin picking din kiran, hadi da kara wayar a kunnanta.
Tamkar kurame sunyi shiru suna sauraran sautin fitar numfashin juna.
Jira take taji wanene mamallakin layin nan daya kira, Haka zalika itama benazir jira take tafara jin wanda ya ɗaga kiran yayi mata magana.
Jin shirun yayi yawane yasa unaisah tace"Assalamu Alaikum" sautin daddaɗan muryarta ne ya daki kunnan Benazir, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin faɗuwar gaba ba.
Muryarta babu nutsuwa ta amsa mata sallamar"Wa'alaikum Salam, barka da dare, dan Allah zan iya sanin dawa nake magana" ta fada cikin ƙagara.
Shiru Unaisah tayi tana tunanin wacece wannan matar mai muryar ƴan gayu? Daga ji dai wayayyiya ce.
Jin shiru ba'a ƙara magana ba yasa banezir furta"nayi magana anyi shiru b'a bani amsa ba, in ansan baza'a tanka min ba meyasa za'a takurani da kira da tsakar dare"? Har zata katse kiran Unaisah tayi saurin cewa"Aunty kiyi haƙuri, bakisan wacece ni ba, nima bansan ki ba"
Ajiyar zuciya Benezir ta sauke kafin tace"okey, amma meyasa kika kira layina bayan baki sanni ba"!
"Nayi kuskurene wurin rubuta number din da zan kira"
"Okey" shiru su ka yi, babu mai magana na tsawon mintuna kafin benazir tayi karfin hali cewa"meye sunan ki? Shekarun ki nawa"? ta tambaya ne jin muryar kamar ta ƙaramar yarinya
"sunana Unaisah, shekarata goma sha shida, ke fa"?
Murmushine ya bayyana akan fuskar benazir, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin farin ciki ba.
"Sunana Aunty pretty, Amma fa ni ba yarinya bace, na girme ki, Shekarata talatin da wani abu"
Murmushi unaisah tayi ita kanta dadi take ji, duk da halin damuwar da take aciki silar kiran nan ya haifar mata da kwanciyar hankali.
"Kiyi hakuri na kiraki bisa kuskure, sannan na katse maki baccin ki"
"Kada ki damu, Naji dadin haduwa dake"
Shiru sukayi Kamar karsu Kashe kiran haka suke ji.
"Baki so na sake kiranki"? Unaisah ce ta jefa mata tambayar .
Murmushi benazir tayi don ta fahinci yarinyar batason su daina magana.
"Ina so mana, tun da naji muryarki naji kin kwanta min araina, da ace babba ce ke da mun kulla kawance sai dai kin min ƙanƙanta"
Cike da zumuɗi Unaisah tace"zan dinga kiranki muna gaisawa a matsayin aunty na, Idan kuma kina da ɗiya kamar ni, ko ƙanwa to ki hadani da ita sai mu dinga zumunci"
"In sha Allah, yanzu ki kwanta ki yi bacci kada mommyn ki ta kama ki kina waya da dare, gobe zan kiraki mu ƙarasa gaisawa, Yanzu kinga dare yayi,"
Kamar karsu rabu, Haka sukayi sallama da junansu, fuskar kowannansu dauke da murmushi.
Karatun kur'ani benazir ta kunna a wayar, saboda ta fahimci Kiran wayar da akayi mata sautin karatun kur'ani ya fita shine silar da Aljanin daya shaƙeta ya gudu, Gefenta ta ajiye wayar, ta kwanta tare da jan bargon da zeenatu ta lullu6a da shi, itama ta lullu6e kanta, zuciyarta acike fal da annurin farin ciki, Harta kosa gobe tayi, kodan ta kira Yarinyar su ƙara gaisawa, ita kadai take ta tufka da warwara har ta yanke shawarar zata haɗa yarinyar da zeenatu su dinga zumunci, in yaso ita sai ta kar6i layin maman yarinyar suna gaisawa da wannan tunanin wani baccin ya kuma daukarta.
Muryarshi adisashe yace"khadeeja ba zaki barni inyi bacci ba? Ke baki runtsa ba nima kuma kin hana in runtsa, Meke damun ki ne"?
Ta6e mashi lips dinta tayi alamar zata fashe mashi da kuka
Da sauri yace"ya isa ni bance kimin kuka ba, Yanzu fada min ya kikeso ayi da 6eran nan da kika kama"
"Ka cire mashi hannuwa" gyada kai yayi tare da sanya hannu ya kar6i 6eran"ki jira ni yanzu zan dawo amsa mashi tayi da toh, fita yai daga dakin tana atsaye tana jiran shi, badajimawa ba ya dawo hannunsa babu 6eran
"Yana ina"?
"Na cire mashi hannuwa na yar" murmushi tasaki"mun hutu da masifa ko"? Ɗaga mata gira yai alamar eh
"Muje na rakaki daki kiyi bacci" maƙe mashi kafada tayi"Ni yunwa nake ji, kaje kitchen ka dafa min abinci"
Wahalallan kallo yabita dashi gaba ɗaya ta takurasa
"Shikenan muje" Ya fada tare da yin gaba tabi bayan shi suka shiga falo, ta zauna saman sofa.
Kitchen Ya shiga bawan Allah ga gajiyar bacci A haka Ya dafa mata indomie, Ya haɗo mata da water bottle, Ya shigo Da plate din Ya miƙa mata, gefen ta ya zauna don yasan koya koma daki indai batayi bacci ba to shima bazai runtsa ba.
Yana kallonta Har ta cinye taliyar ta kora da ruwa, kwanciya tayi saman sofa din ta daura kafafuwanta saman laps dinshi bai tanka mata ba, yasan rigima take nema, Cikin sa'a bacci yai awon gaba da ita, A hankali Ya zame ƙafafuwanta ya miƙe tare da ɗaukarta ya nufi upstairs da ita, a kan gado ya kwantar da ita, yabi da bargo ya lullu6e mata jikinta, kafin ya fito ya datse kofar dakin nata, cikin sauri ya nufi dakinsa don ya kwanta ya karasa baccin dabai isheshi ba, bayan shigarshi daki har ya kwanta ya soma tunanin ko me ya hana jazz zuwa? Tun safe yake jaraba kiran layin shi baya picking, har ta 6angaren danish ba a kira shi ba wunin yau, fatan shi Allah yasa lafiya da wannan tunanin bacci 6arawo ya ɗauke shi.
*💋BENAZIR❤*
Kwance take a saman darduma, tun bayan data kammala sallar Isha bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita, yayin da zeenatu take a can saman gado tana bacci.
Tana a nannaɗe cikin dogon hijab dinta, tayi nisa acikin baccin ta, Ba zato ba tsammani hasken fitilar bedroom ɗinta ya ɗauke ɗuff, wani iko na Allah ba wutar gidan bace ta samu matsala, ɗakinta ne kadai hasken ya ɗauke, abun ka game bacci sam bata ji alamun hasken dakin ta ya ɗauke ba.
Kwatsam! taji an damƙi wuyanta, tsabar zafin shaƙar da akayi mata ne yasa ta ware idanunta waje, bata iya ganin komai sai duhu baƙi wulik a idanunta
Wani irin mahaukacin bugun fargaba zuciyarta keyi mata, Hankalinta a matuƙar tashe ta soma kokarin kwace wuyanta daga hannun mutumin daya shaƙeta, wuyanta tuni ya soma yi mata zogin azaba, zufa ta ko'ina ta wanke fuskarta, duk yadda benazir taso ta kwace kanta sai dai kash takasa, ga zeenatu kwance saman gado sai dai babu halin da zata iya buɗe baki ta nemi agajin ta, koma wanene yayi mata muguwar shaƙar da ko yatsanta takasa ɗagawa, bakinta tamkar an ɗaure mata shi takasa buɗe shi, hakan yasa tafara kukan zuci tana ambaton sunan Daddy, mommy, yaya shurem, Zeenatu, A karshe ta kamo kalmar Innalillahi wa'inna ilaihirraji"un tacigaba da anbatonta acikin zuciyarta.
Tana acikin wannan mawuyacin Halin har tafara fidda rai da rayuwa kwatsam wayar zeenatu da ta ajiye kan gado ta soma ringing, taken karatun al'ƙur'ani mai girma ne, Kamar Walkiya taji alamun an sakar mata wuyanta, kuma nan take hasken ɗakinta ya kawo, a gigice ta zabura ta miƙe zaune tana faman zazzare idanunta, bin ko'ina na dakin tayi da kallo bata ga kowa ba, Lamarin ya daure mata kai, tagaza gane meke shirin faruwa da ita? Don wannan yafi karfin a kirashi da mafarki, tabbas akwai me son rabata da rayuwarta, lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka tamkar ƙaramar yarinya ita kadai tasan radaɗin da wuyan ta ke yi mata, zeenatu dake ta sharar baccin ta tuni ta soma mutsu mutsun farkawa saboda sautin kukan benazir daya fara addabar kunnuwanta, da sauri benazir ta tsagaita da yin kukan gudun kada zeenatu ta farka taga halin da take a ciki, cikin juriya ta miƙe ta zame hijab din jikinta, ta jefar da shi gefen gado, gaban madubi taje ta tsaya tana kallon wuyanta yayi jawur da shi hada sawun yatsun hannuwan mutun rudu rudu..
Hakika Ta gigita ta kuma tsorata a yanzu ta ƙara tabbatarwa kanta cewa akwai me son ganin bayan ta? Wanene? Laifin me ta aikata da har ake son kashe ta? Zuciyarta ce ta raya mata cewa zai iya yiwuwa jinnu ne, tafi yarda da abun da zuciyan nata ta raya mata saboda babu wanda take zargin zai iya yi mata haka acikin mutanan da take rayuwa da su,ta dai yanke shawarar zata sanarwa yaya shureim ko dan su nemi mafita a tare.
Miryarta na rawa ta furta"Ya Allah ban cutar da kowa ba, Kada ka bada damar da wani zai cutar dani" ta jima atsaye gaban mirror, zuciyarta cike da rudani, ta nufi toilet, tsawon mintuna kafin ta fito jikinta da alamun lemar ruwan da ta watsa ma kanta.
Tunawa da kiran wayar da akai mata ne yasa ta nufi bakin gado ta ɗauko phone din ta soma daddanawa call logs ta shiga nan take taga missed call na bakuwar number din nan
Sai da ta fara kallon agogo, karfe wani abu na dare kafin ta danna call tana faman zazzare idanunta, jikinta nata kerma kamar wadda aka kada ma mazari
Adai dai wannan lokacin Unaisah tana a zaune kan darduma ta zumbula hijabi a jikinta ta ɗaga hannayenta sama fuskarta sharkaf da hawaye bakomai take yi ba face yima danish addu'ar samun lafiya, Batul tana a kwance gefen ta, tun bayan da boss ya tashe su domin yin nafilfilin da za su yi kowannansu bai koma bacci ba, duk suna a dakunansu suna yin sallah, ita dama batul bata da jumurin yin sallah duka raka'a biyu ta samu tayi adaddafe kafin bacci yai awon gaba da ita, shigowar kiran wayar ta ne yasa takai hannu ta dauke ta, a inda ta ajiye ta gefen prayer mat din da suka akai
Ko da tayi tozali da layin da take ta dannawa kira taga da shi aka kirata Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin yin picking din kiran, hadi da kara wayar a kunnanta.
Tamkar kurame sunyi shiru suna sauraran sautin fitar numfashin juna.
Jira take taji wanene mamallakin layin nan daya kira, Haka zalika itama benazir jira take tafara jin wanda ya ɗaga kiran yayi mata magana.
Jin shirun yayi yawane yasa unaisah tace"Assalamu Alaikum" sautin daddaɗan muryarta ne ya daki kunnan Benazir, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin faɗuwar gaba ba.
Muryarta babu nutsuwa ta amsa mata sallamar"Wa'alaikum Salam, barka da dare, dan Allah zan iya sanin dawa nake magana" ta fada cikin ƙagara.
Shiru Unaisah tayi tana tunanin wacece wannan matar mai muryar ƴan gayu? Daga ji dai wayayyiya ce.
Jin shiru ba'a ƙara magana ba yasa banezir furta"nayi magana anyi shiru b'a bani amsa ba, in ansan baza'a tanka min ba meyasa za'a takurani da kira da tsakar dare"? Har zata katse kiran Unaisah tayi saurin cewa"Aunty kiyi haƙuri, bakisan wacece ni ba, nima bansan ki ba"
Ajiyar zuciya Benezir ta sauke kafin tace"okey, amma meyasa kika kira layina bayan baki sanni ba"!
"Nayi kuskurene wurin rubuta number din da zan kira"
"Okey" shiru su ka yi, babu mai magana na tsawon mintuna kafin benazir tayi karfin hali cewa"meye sunan ki? Shekarun ki nawa"? ta tambaya ne jin muryar kamar ta ƙaramar yarinya
"sunana Unaisah, shekarata goma sha shida, ke fa"?
Murmushine ya bayyana akan fuskar benazir, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin farin ciki ba.
"Sunana Aunty pretty, Amma fa ni ba yarinya bace, na girme ki, Shekarata talatin da wani abu"
Murmushi unaisah tayi ita kanta dadi take ji, duk da halin damuwar da take aciki silar kiran nan ya haifar mata da kwanciyar hankali.
"Kiyi hakuri na kiraki bisa kuskure, sannan na katse maki baccin ki"
"Kada ki damu, Naji dadin haduwa dake"
Shiru sukayi Kamar karsu Kashe kiran haka suke ji.
"Baki so na sake kiranki"? Unaisah ce ta jefa mata tambayar .
Murmushi benazir tayi don ta fahinci yarinyar batason su daina magana.
"Ina so mana, tun da naji muryarki naji kin kwanta min araina, da ace babba ce ke da mun kulla kawance sai dai kin min ƙanƙanta"
Cike da zumuɗi Unaisah tace"zan dinga kiranki muna gaisawa a matsayin aunty na, Idan kuma kina da ɗiya kamar ni, ko ƙanwa to ki hadani da ita sai mu dinga zumunci"
"In sha Allah, yanzu ki kwanta ki yi bacci kada mommyn ki ta kama ki kina waya da dare, gobe zan kiraki mu ƙarasa gaisawa, Yanzu kinga dare yayi,"
Kamar karsu rabu, Haka sukayi sallama da junansu, fuskar kowannansu dauke da murmushi.
Karatun kur'ani benazir ta kunna a wayar, saboda ta fahimci Kiran wayar da akayi mata sautin karatun kur'ani ya fita shine silar da Aljanin daya shaƙeta ya gudu, Gefenta ta ajiye wayar, ta kwanta tare da jan bargon da zeenatu ta lullu6a da shi, itama ta lullu6e kanta, zuciyarta acike fal da annurin farin ciki, Harta kosa gobe tayi, kodan ta kira Yarinyar su ƙara gaisawa, ita kadai take ta tufka da warwara har ta yanke shawarar zata haɗa yarinyar da zeenatu su dinga zumunci, in yaso ita sai ta kar6i layin maman yarinyar suna gaisawa da wannan tunanin wani baccin ya kuma daukarta.