Sashe 70
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Faɗowa Dakin Haris Yayi, fuskarsa dauke da tsantsar farin ciki sai faman sakin murmushi Yake yi, ba don komai ba sai don zumudin ganin deejansa jiya da ita Ya kwana Aransa yanzu haka yazo ne don Ya ƙara ganinta ya kuma tabbatarwa kansa ba mafarki bane abun da Ya faru Jiya.
Unaisah Na ganinsa Tace"ba sallama? Me ma Ya kawoka dakinmu da sassafe"?
Shafa sumar kansa yai"ina deejana"? Aɗan ruɗe tay pretending"deeja kuma? Kayi mafarki da ita ne"!
Hankali atashe Yace"bangane me kike nufi ba, wani irin mafarki bayan jiya sun zo gidan nan har mu ka yi shagali, da kaina ma na rakota dakin ku da tace min tana jin bacci.
Fuska adaure tace"haris? Ko dai ka fara samun ta6in hankali ne? Meya kawo maganar deeja? Bayan ta riga da ta rasu tun a prison"? Yanayin yadda tayi magamar ba karamin kayar masa da gaba tayi ba jikin shi yai sanyi gwiwarsa ta sage
"Kina nufin mafarki nayi jiya" ɗaga masa gira tay"zai iya yiwuwa" shiru yayi zuciyarsa ajagule yake kallon unaisah gaba daya so take ta rikita lissafin ƙwalwarsa ..
"Lafiya ka tsaya kana kallona? Meke damunka ne"? Ƙwalla ce ta ciko idanunsa muryarsa na rawa ya furta"deeja na ta mutu? mafarki nayi jiya sunzo? har ta buɗe baki zata bashi amsa Kwatsam Deeja Ta banko kofar toilet din kamar an wurgo ta da karfi ta furta"Laahh! Haris kaine? Yana jin muryarta a ruɗe Yakai dubansa gareta lokaci ɗaya ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya, da gudu Deeja Ta nufe sa ta ƙanƙame shi tana fadin"wallahi jiya har mafarkinka nayi harisuna"
"Deejana Kin tashi lafiya"?
Tana faman Washe Baki tace"lafiyalou wlh, nima muryarka najiyo ina ga daga Cikin toilet, Har na fara alwala na katse ta"
Unaisah dake kallonsu tana dariya gaba daya mamakin ƙaunarsu ya gama cikata, wani abu daya ɗaure mata kai yadda deeja Ta yarda dashi bayan jiya sukai ta fama da ita akan ta tuna shi amma taƙiya sai gashi da yake kaunar tasu a jini take har sun shaƙu jiya izuwa yau
"Sister kada ki sake yi min irin wannan wasan, zuciyata zata Iya bugawa Allah" Yai maganar idonsa akan Unasah
"Naji romeo, bazan ƙaraba, Yanzu sai kabarta ta koma ta karasa alwalar ko fa salla batai ba" Harara deeja ta watsa mata"waike ina ruwanki dani in ma banyi sallar ba, ay ni ba kullum nakeyi ba sai na ga dama, Ko su hawwa basu min dole balle ma ke da bansan wacece ba' muryarta da shagwa6a take magana hakan bakaramin dariya ya basu ba
Lalla6ata haris yayi"rabu da ita, kishi takeyi da take don taga kinfi ta kyau, " washe baki tayi jin Yana yabonta
"Yanzu ki koma ki karasa alwalar in kin gama ki yi wanka sai ki fito muje muyi breakfast" amsa mashi tayi da toh da gudu ta juya tana fadin Kada ka tafi harisuna ka jira ni in fito Yana murmushi ya amsa mata da toh har ta shige bai daina kallon ta ba
Da zolaya unaisah tace"Hankali Ya kwanta Haris, deeja Ta dawo, No more heartbreak " dariyar farin Ciki Ya saki" ba zaki gane ba, wlh daren jiya bayan na rakota dakin ku ta kwanta dana koma dakinmu har nafila nayi saboda in nuna godiya ga Allah daya sake hadani da ita, Ina son deeja Allah Yabar mun ita har abada, in ma mutuwa zata dauke ni ta dauke mu atare" idanu abude Unaisah ke kallon shi aranta tunani take tsakanin deeja da haris da kuma ita da danish suwaye sukafi son juna tsakani da Allah? anya idan danish Ya rasata zaiyi ciwon zuciya kamar yadda haris yayi akan deeja? Ko kuwa ita idan tarasa shi zatai hauka? tabbas A yanzu bata iya ganewa tun da wani bai ta6a rasa wani a cikin su ba, kuma bata fatan abun da zai raba ta da muradin ranta, her eternal lover
"Haris Ina tayaka murna, Allah Ya nuna mana ranar auranku mu sha biki" da mamaki ya maimaita kalmar aure" yar dariya tay"cikar burin masoya kenan idan time yayi basai na maka bayani ba" murmushi kawai yayi duk da baisan me akeyi a auranba but maganarta tasa shi fara jin son ganin auran nasu.
Ƙarfe tara daidai agogo ta buga, ɗaya bayan ɗaya suke fitowa daga dakunansu zuwa dining Room kowan nan su yayi wanka Ya shirya sunyi kyau daga ganin fuskokinsu zaka shaida Anyi kwanan farin ciki daren Jiya....
Da wani irin ɗaukin junansu suka fara ƴan rungume rungumen juna, gwanin ban sha'awa, ƙaunar su a jini ta ke, harta chefs din dake a dakin cin abincin kallon su sukeyi saboda sun siye zuciyoyin su.
Mutun ukune ke babu acikin su, ummi da batool sai Danish, su kadai ne ba su kaiga ƙarasowa ba.
Sun cika dining room din da surutu Ko zama sun kasa yai,
Gyaran murya chef Yai masu Hankalinsu Ya dawo kan shi
"Barkanku mu da safiya yan mata da samari, ina fata kun tashi Lafiya" a tare suka amsa mashi da lafiyalou
"Yawwa, Yanzu ba lokacin surutu bane, lokacin bama ciki hakkinsa ne, nasan kunyi kewar Juna amma Ku ɗanyi hakuri ku zauna mana"
murmushi Kowan nan su Ya saki, ɗayan Chef din Yace"Amma in ba damuwa zamu iya sanin sunayenku? Don gaskiya bansan sunanku ba unaisah kadai nasani' Ya faɗa Yana nuna ta da yatsa
"Ba damuwa ni zan faɗa maku sunayen su," unaisah ce tayi maganar, kafin ta fara faɗa masu sunayen
"wadannan biyun masu kama da twins sunayen su Jemimah sai Azeeza" ta faɗa tana nuna su da yatsa sai faman sakin murmushi sukeyi.
Ɗaga masu hannu chefs din sukai alamar suna miko gaisuwa
"Sajeed Naufal and Javed" ta nuna kowannansu da yatsa
"Wannan Kuma sunan sa Haris ga deejarsa a gefe, kamar anta da jini suke"
"Kina nufin masoya ne"? Ɗaga masu kai tay alamar eh"
"Wow masha Allah, shiyasa suke bala'en kama da junansu ashe soyayyace atsakani, Muna miƙo maku gaisuwa" chefs din suka fada suna ɗaga masu hannu, washe baki deeja tayi shima haris din murmushi ne kan fuskarsa
"Ita kuma wannan sunanta Hannah" ta nuna hannah dake tsaye gefen parven, ga kuma Parveen acici" dariya sukai don sunsan Halinta na cin abinci"
Juyawa tayi kan su Rubina"rubina, eve and yasmin sai hibba" da sauri eve tace"kin manta jiya na fada maki yaya salsabeel Ya canza min suna hawwa"
"Yeah Na tuna sunanta Hawwa, ga kuma sarah da mubeen" ta nuna su da hannu
"thank You unaisah, kunga yanzu munsan sunan kowan nan ku saura mu saba da juna koba haka ba"? Atare suka hada baki wurin amsa masu da Yeah
"Yanzu zamu fara shirya maku wurin zamanku tun da mun samu ƙaruwa"
Ba tare da 6ata lokaci ba, mutun sha Biyu daga cikinsu suka zauna akan 12-seater dining table din da suka saba cin abinci akan shi, sauran suka samu gurbin akan 6-sitter dama ukune a dakin cin abincin.
Har sun fara cikin abincin, sautin cokulansu Ya cika dining room din kamar a restaurant yanayin yadda suka zauna, chefs din suna daga tsaye suna kallon.
Miƙewa unaisah tayi tare da kallon chefs din tace"zanje na kira aunty ummi da batool" bata jira amsar su ba tay saurin kama hanya don tasan zasu iya tsayar da ita..
Har takusa isa ga stairs, sai ga su sunfito daga daki, Hannunsu ruke cikin juna yadda kasan uwa da ɗiyarta, ummi na asanye da abaya maroon tayi rolling, batool tun kayan jiyane a jikin ta riga da wando na bacci
Suna ganinta a tare suka sakarwa juna murmushi da sauri batool ta saki hannun ummi ta nufi unaisah suka rungume juna kamar sun jima ba su a tare
"Barka da safiya My own sis, jiya ko ki neme ni, aunty ummi ta ƙwace min ke" ta faɗa tare da raba jikin su daga na juna.
"Ni da ke waye mai laifi? jiya kamar zanyi hauka wurin nemanki, ina kika je baki fada min ba"? rai aɗan 6ace tayi maganar suna kallon juna
"I'm sorry, nima bada son raina na tafi nabarki ba, naga kuna firar yaushe rabo kuma bana son in katse ku shiyasa na tafi...."
"Ina kike je ne"? Ummi ce ta jefa mata tambayar
"Part din daddyna dake acikin gidan nan, " da mamaki ummi tace"oh dama anan yake zaune? Ko da yake naga gidan ba karamin girma ne da shi ba, ay ko zan haɗu da shi maimakon ya gayyace mu muje baki ɗaya shine ya ware ki ko"? Ta fada da zolaya
yar dariya unaisah tayi"wlh ba haka bane, yace min next time kuma zai gayyace ku kuje part dinsa wurin auntyna danejo"
Murmushi ummi tayi"ai ko bai gayyace ni ba zanje da kaina, ko dan ingano danejo, inyi mata godiya saboda taimakon da tayi mana wurin ceto rayuwarki"
Fuskarta dauke da murmushi tace"naji dadin maganarki aunty ummi, Allah yabarmu atare" amsa mata sukai da ameen
"angama shirya mana breakfast a dining, naga baku futo ba shi ne nazo don in kira ku"
"Yanzu haka da kika ganmu yunwar ce ta koro mu nida baby girl dina" ta faɗa tare da ruko hannun batool har zata ruko na unaisah donsu tafi a tare tayi saurin cewa" zanje na kira danish ne" amsa mata tai da okey, bayan sun tafi ta nufi bedroom dinsa tana gab da zata shiga taji motsin fitowarsa kusan atare idanunsu suka shiga cikin na juna kwata kwata fuskarsa babu annuri ganinta da yayi ne yasa shi ɗan sakin fuskarsa tun daga kan yatsan kafarta ya fara kallonta ba karamin kyau tayi mashi ba, rigar ta ƙara fito mata shape dinta.
"My man, ina fata ka tashi lafiya," lumshe mata ido yai alamar eh
"Oh ba zaka min magana ba, kasan kuwa yadda na ƙagu da inzo ganinka" ta faɗa tana jifar shi da kallo mai kama da harara irin kallon da ke jan hankalin shi gareta
"Saboda kaga na damu kai ko" ta fada tana ruƙe qugunta
Daƙyar Ya iya haɗiyar yawu Ya furta"kin tashi lafiya"
Ɗaga mashi gira tayi"ina lafiya, pls ka shiga ka canza kayan baccin nan, sauran yan uwanmu suna jiranmu a dining muyi breakfast"
Unaisah Na ganinsa Tace"ba sallama? Me ma Ya kawoka dakinmu da sassafe"?
Shafa sumar kansa yai"ina deejana"? Aɗan ruɗe tay pretending"deeja kuma? Kayi mafarki da ita ne"!
Hankali atashe Yace"bangane me kike nufi ba, wani irin mafarki bayan jiya sun zo gidan nan har mu ka yi shagali, da kaina ma na rakota dakin ku da tace min tana jin bacci.
Fuska adaure tace"haris? Ko dai ka fara samun ta6in hankali ne? Meya kawo maganar deeja? Bayan ta riga da ta rasu tun a prison"? Yanayin yadda tayi magamar ba karamin kayar masa da gaba tayi ba jikin shi yai sanyi gwiwarsa ta sage
"Kina nufin mafarki nayi jiya" ɗaga masa gira tay"zai iya yiwuwa" shiru yayi zuciyarsa ajagule yake kallon unaisah gaba daya so take ta rikita lissafin ƙwalwarsa ..
"Lafiya ka tsaya kana kallona? Meke damunka ne"? Ƙwalla ce ta ciko idanunsa muryarsa na rawa ya furta"deeja na ta mutu? mafarki nayi jiya sunzo? har ta buɗe baki zata bashi amsa Kwatsam Deeja Ta banko kofar toilet din kamar an wurgo ta da karfi ta furta"Laahh! Haris kaine? Yana jin muryarta a ruɗe Yakai dubansa gareta lokaci ɗaya ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya, da gudu Deeja Ta nufe sa ta ƙanƙame shi tana fadin"wallahi jiya har mafarkinka nayi harisuna"
"Deejana Kin tashi lafiya"?
Tana faman Washe Baki tace"lafiyalou wlh, nima muryarka najiyo ina ga daga Cikin toilet, Har na fara alwala na katse ta"
Unaisah dake kallonsu tana dariya gaba daya mamakin ƙaunarsu ya gama cikata, wani abu daya ɗaure mata kai yadda deeja Ta yarda dashi bayan jiya sukai ta fama da ita akan ta tuna shi amma taƙiya sai gashi da yake kaunar tasu a jini take har sun shaƙu jiya izuwa yau
"Sister kada ki sake yi min irin wannan wasan, zuciyata zata Iya bugawa Allah" Yai maganar idonsa akan Unasah
"Naji romeo, bazan ƙaraba, Yanzu sai kabarta ta koma ta karasa alwalar ko fa salla batai ba" Harara deeja ta watsa mata"waike ina ruwanki dani in ma banyi sallar ba, ay ni ba kullum nakeyi ba sai na ga dama, Ko su hawwa basu min dole balle ma ke da bansan wacece ba' muryarta da shagwa6a take magana hakan bakaramin dariya ya basu ba
Lalla6ata haris yayi"rabu da ita, kishi takeyi da take don taga kinfi ta kyau, " washe baki tayi jin Yana yabonta
"Yanzu ki koma ki karasa alwalar in kin gama ki yi wanka sai ki fito muje muyi breakfast" amsa mashi tayi da toh da gudu ta juya tana fadin Kada ka tafi harisuna ka jira ni in fito Yana murmushi ya amsa mata da toh har ta shige bai daina kallon ta ba
Da zolaya unaisah tace"Hankali Ya kwanta Haris, deeja Ta dawo, No more heartbreak " dariyar farin Ciki Ya saki" ba zaki gane ba, wlh daren jiya bayan na rakota dakin ku ta kwanta dana koma dakinmu har nafila nayi saboda in nuna godiya ga Allah daya sake hadani da ita, Ina son deeja Allah Yabar mun ita har abada, in ma mutuwa zata dauke ni ta dauke mu atare" idanu abude Unaisah ke kallon shi aranta tunani take tsakanin deeja da haris da kuma ita da danish suwaye sukafi son juna tsakani da Allah? anya idan danish Ya rasata zaiyi ciwon zuciya kamar yadda haris yayi akan deeja? Ko kuwa ita idan tarasa shi zatai hauka? tabbas A yanzu bata iya ganewa tun da wani bai ta6a rasa wani a cikin su ba, kuma bata fatan abun da zai raba ta da muradin ranta, her eternal lover
"Haris Ina tayaka murna, Allah Ya nuna mana ranar auranku mu sha biki" da mamaki ya maimaita kalmar aure" yar dariya tay"cikar burin masoya kenan idan time yayi basai na maka bayani ba" murmushi kawai yayi duk da baisan me akeyi a auranba but maganarta tasa shi fara jin son ganin auran nasu.
Ƙarfe tara daidai agogo ta buga, ɗaya bayan ɗaya suke fitowa daga dakunansu zuwa dining Room kowan nan su yayi wanka Ya shirya sunyi kyau daga ganin fuskokinsu zaka shaida Anyi kwanan farin ciki daren Jiya....
Da wani irin ɗaukin junansu suka fara ƴan rungume rungumen juna, gwanin ban sha'awa, ƙaunar su a jini ta ke, harta chefs din dake a dakin cin abincin kallon su sukeyi saboda sun siye zuciyoyin su.
Mutun ukune ke babu acikin su, ummi da batool sai Danish, su kadai ne ba su kaiga ƙarasowa ba.
Sun cika dining room din da surutu Ko zama sun kasa yai,
Gyaran murya chef Yai masu Hankalinsu Ya dawo kan shi
"Barkanku mu da safiya yan mata da samari, ina fata kun tashi Lafiya" a tare suka amsa mashi da lafiyalou
"Yawwa, Yanzu ba lokacin surutu bane, lokacin bama ciki hakkinsa ne, nasan kunyi kewar Juna amma Ku ɗanyi hakuri ku zauna mana"
murmushi Kowan nan su Ya saki, ɗayan Chef din Yace"Amma in ba damuwa zamu iya sanin sunayenku? Don gaskiya bansan sunanku ba unaisah kadai nasani' Ya faɗa Yana nuna ta da yatsa
"Ba damuwa ni zan faɗa maku sunayen su," unaisah ce tayi maganar, kafin ta fara faɗa masu sunayen
"wadannan biyun masu kama da twins sunayen su Jemimah sai Azeeza" ta faɗa tana nuna su da yatsa sai faman sakin murmushi sukeyi.
Ɗaga masu hannu chefs din sukai alamar suna miko gaisuwa
"Sajeed Naufal and Javed" ta nuna kowannansu da yatsa
"Wannan Kuma sunan sa Haris ga deejarsa a gefe, kamar anta da jini suke"
"Kina nufin masoya ne"? Ɗaga masu kai tay alamar eh"
"Wow masha Allah, shiyasa suke bala'en kama da junansu ashe soyayyace atsakani, Muna miƙo maku gaisuwa" chefs din suka fada suna ɗaga masu hannu, washe baki deeja tayi shima haris din murmushi ne kan fuskarsa
"Ita kuma wannan sunanta Hannah" ta nuna hannah dake tsaye gefen parven, ga kuma Parveen acici" dariya sukai don sunsan Halinta na cin abinci"
Juyawa tayi kan su Rubina"rubina, eve and yasmin sai hibba" da sauri eve tace"kin manta jiya na fada maki yaya salsabeel Ya canza min suna hawwa"
"Yeah Na tuna sunanta Hawwa, ga kuma sarah da mubeen" ta nuna su da hannu
"thank You unaisah, kunga yanzu munsan sunan kowan nan ku saura mu saba da juna koba haka ba"? Atare suka hada baki wurin amsa masu da Yeah
"Yanzu zamu fara shirya maku wurin zamanku tun da mun samu ƙaruwa"
Ba tare da 6ata lokaci ba, mutun sha Biyu daga cikinsu suka zauna akan 12-seater dining table din da suka saba cin abinci akan shi, sauran suka samu gurbin akan 6-sitter dama ukune a dakin cin abincin.
Har sun fara cikin abincin, sautin cokulansu Ya cika dining room din kamar a restaurant yanayin yadda suka zauna, chefs din suna daga tsaye suna kallon.
Miƙewa unaisah tayi tare da kallon chefs din tace"zanje na kira aunty ummi da batool" bata jira amsar su ba tay saurin kama hanya don tasan zasu iya tsayar da ita..
Har takusa isa ga stairs, sai ga su sunfito daga daki, Hannunsu ruke cikin juna yadda kasan uwa da ɗiyarta, ummi na asanye da abaya maroon tayi rolling, batool tun kayan jiyane a jikin ta riga da wando na bacci
Suna ganinta a tare suka sakarwa juna murmushi da sauri batool ta saki hannun ummi ta nufi unaisah suka rungume juna kamar sun jima ba su a tare
"Barka da safiya My own sis, jiya ko ki neme ni, aunty ummi ta ƙwace min ke" ta faɗa tare da raba jikin su daga na juna.
"Ni da ke waye mai laifi? jiya kamar zanyi hauka wurin nemanki, ina kika je baki fada min ba"? rai aɗan 6ace tayi maganar suna kallon juna
"I'm sorry, nima bada son raina na tafi nabarki ba, naga kuna firar yaushe rabo kuma bana son in katse ku shiyasa na tafi...."
"Ina kike je ne"? Ummi ce ta jefa mata tambayar
"Part din daddyna dake acikin gidan nan, " da mamaki ummi tace"oh dama anan yake zaune? Ko da yake naga gidan ba karamin girma ne da shi ba, ay ko zan haɗu da shi maimakon ya gayyace mu muje baki ɗaya shine ya ware ki ko"? Ta fada da zolaya
yar dariya unaisah tayi"wlh ba haka bane, yace min next time kuma zai gayyace ku kuje part dinsa wurin auntyna danejo"
Murmushi ummi tayi"ai ko bai gayyace ni ba zanje da kaina, ko dan ingano danejo, inyi mata godiya saboda taimakon da tayi mana wurin ceto rayuwarki"
Fuskarta dauke da murmushi tace"naji dadin maganarki aunty ummi, Allah yabarmu atare" amsa mata sukai da ameen
"angama shirya mana breakfast a dining, naga baku futo ba shi ne nazo don in kira ku"
"Yanzu haka da kika ganmu yunwar ce ta koro mu nida baby girl dina" ta faɗa tare da ruko hannun batool har zata ruko na unaisah donsu tafi a tare tayi saurin cewa" zanje na kira danish ne" amsa mata tai da okey, bayan sun tafi ta nufi bedroom dinsa tana gab da zata shiga taji motsin fitowarsa kusan atare idanunsu suka shiga cikin na juna kwata kwata fuskarsa babu annuri ganinta da yayi ne yasa shi ɗan sakin fuskarsa tun daga kan yatsan kafarta ya fara kallonta ba karamin kyau tayi mashi ba, rigar ta ƙara fito mata shape dinta.
"My man, ina fata ka tashi lafiya," lumshe mata ido yai alamar eh
"Oh ba zaka min magana ba, kasan kuwa yadda na ƙagu da inzo ganinka" ta faɗa tana jifar shi da kallo mai kama da harara irin kallon da ke jan hankalin shi gareta
"Saboda kaga na damu kai ko" ta fada tana ruƙe qugunta
Daƙyar Ya iya haɗiyar yawu Ya furta"kin tashi lafiya"
Ɗaga mashi gira tayi"ina lafiya, pls ka shiga ka canza kayan baccin nan, sauran yan uwanmu suna jiranmu a dining muyi breakfast"