Sashe 102
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
tun da asuba aka canza masu room yanzu suna a privet room na asibiti, tamkar bedroom na gida haka Yake, har gado ɗaya aka ƙara masu saboda ya ishe su ita da unaisah.
"Mommy wlh bata nan, ta 6ace, wani ya sace min ita, nama san taj ne Ya gudu da ita saboda yana jin haushina...." saukowa tayi daga kan gadon ta durkusa tana leƙen karkashin gadon sumar kanta duk ta rufe fuskarta da bayanta...
"Benazir me kikeyi anan ki tashi mana, nace maki yarki tana atare dake yanzu zata fito, Ki zo ki sha maganin ki, ga breakfast an kawo mana..." ta faɗa tare da ruko hannunta, fashewa tayi kuka tana fadin"wayyo Allahna mami, wlh babu ita, na shiga uku na bani na lalace, baby ta 6ace..." duk yadda hajiya layla taso ta shawo kanta abun Ya faskara gaba daya nema take ta zauce...
Motsin buɗe kofar toilet ne Ya katse mata kukan nata, a firgice ta juya tana kallon kofar tana faman zare dara daran idanunta, tundaga kasa ta fara kallon kafafuwanta dake asanye da slippers farare tas da su, da sauri benazir ta wurga idanunta kan fuskarta, harsaida ta lumshe su saboda wani sanyi daya ratsa zuciyarta, fitowarta kenan daga wanka, doguwar riga ce a jikin ta pink colour tayi wani fresh da ita kamar babu damuwa atare da ita.
Ƙurawa juna ido sukayi batare da kyaftawa ba, hajiya layla dake kallon su tsabar murna bakinta yaƙi rufuwa yadda kasan gonar auduga.
Cikin sanyin murya unaisah ta furta"mamana! Kin tashi lafiya! Ya jikin naki? Kin farka baki ganni ba am sorry na shiga toilet yin wanka ne..." wani irin bugu zuciyar Benzar tayi yanayin fuskarta ya nuna kamar tana kokarin dawowa hayyacin ta ne.
Murmushi Angel ta sakar mata har dimple dinta suka lotsa, kamar ta samu tv haka ta ƙura mata ido tana kallon ta.
"Benazir baki gane ta ba? Babyn da kike nema ce, Kije wurin ta..." jikinta na 6ari kamar mazari ta mike ta nufi unaisah, tana karasawa ta zube kan gwiwowinta ta sanya hannu biyu tayi huggin dinta tightly akan kirjinta, wani irin yanayi suka tsinci kansu mara misaltuwa, kusan a tare heart dinsu ke bugu da karfi da karfi, tuni kwalla sun cika idanun kowan nan su.
"Babyna ne"? Ta fada tare da tallabo fuskar unaisah ta ƙura mata ido tana faman zare mata idanunta har saida gaban angel ya fadi tarasa gane meyasa take jin ta kamar mahaifiyarta.
"Kinyi shiru baki amsa min ba! Baby na ne? Ke ce? Ta fada tana ɗage mata eye brows dinta.
Jinjina mata kai unaisah tayi"ni ce mamana" yawu benazir ta haɗiya kafin ta furta"taj ne Ya kawo min ke uhum? Yana ina"? Rass gaban Angel Ya faɗi ta zaro ido tare da kallon hajiya layla wadda ta kura masu ido tana kallon su gwanin ban sha'awa.
Lamarin ya daure mata kai, meyasa take ambaton sunanta da sunan daddynta? To kodai itama sunan yarta ne da mijinta hakan? Abun da daure kai, tayaya akai sunan su yazo ɗaya"? Ta jefa ma kanta tambayar da bata da amsar ta, ranta ne ya raya mata ay ba ita kadaice me irin nickname dinta ba suna dayawa, shima sunan taj din ba daddynta kadai ke da shi ba, hakan yasa ta saki jikin ta.
Jinjina mata kai tayi"daddyna ne Ya kawo ni, shima yana nan zaizo wurinki amma sai kin kwantar da hankalinki..." cike da zumudi tace toh toh zan kwantar da hankalina..."
Huggin dinta unaisah ta karayi wani irin dadi takeji, ta dade batayi bacci mai dadi irin na jiya ba, bata ta6a zaton zata iya runtsawa ba saboda halin damuwar datake a ciki na abun da ya faru tsakaninta da Danish amma cikin ikon Allah silar baiwar Allahn nan jiya tayi bacci mai nauyi kuma ta samu relief na radadin da zuciyarta keyi mata.
"Mamana, Ki shiga toilet, kiyi wanka zaki ji dadin jikin ki, Idan kika fito dakaina zan baki abinci abaki .." wani irin dadine Ya lullu6e benazir, da sauri ta kalli hajiya layla idanunta cike tab da kwalla tace"mommy tana sona sosai, dama nasan bazata guje ni ba, saboda ita jinina nace, kuma tasan bada san raina na gudu nabarta ba..."
rass gaban angel ya fadi maganar benazir ta jefata arudani, lokaci daya brain dinta tafara tariyo mata labarin mamanta data gudu tabarta a kwamin wanka, tuni yanayin fuskarta ya canza zuwa tsantsar 6acin rai, gani take kamar yawancin iyaye mata basu da tausayin ya'yansu shiyasa suka watsar da su bayan sun haife su.
"Benazir ki shiga kiyi wankan, babynki zata jiraki anan" jikin ta na rawa ta mike ta shiga toilet din, tun zuwansu hajiya layla ke taimaka mata tayi wanka saboda rashin nutsuwar da bata da ita, amma yau da kanta tayi wanka abun ba karamin dadi yayi ma hajiya layla ba, atare suka zauna da angel ta fara bata abinci abaki tana ci sai dadi take ji, ita ma ta dauki spoon ta debo ta sanya ma angel abaki hajiya layla nata kallon su gwanin ban sha'awa bayan sun kammala cin abinci, dr jazz ya shigo duba lafiyar benazir shi kanshi ya fahimci nasarar da suka fara samu don alamu sun nuna takusa regaining hankalin ta....yau ko allura ba'ayi mata ba, magungunanta kadai suka bata tasha.
Kafin dr jazz yabar dakin saida Ya kira unaisah, suka ke6e a kofar dakin ya tambayeta meke damunta? Chief ya fada mashi bata da lafiya..." murmushi tayi masa kafin tace"ba abunda ke damuna, lafiyata qalou.." lallashinta ya dinga yi yana lalla6ata duk don ta fada mashi amma ta nace akan ita lafiyarta qalou, yace toh shikenan idan akwai wani abu da kike bukata ki sanar dani, chief ya bani amanarki bana son ganin damuwa atare dake, har cikin ranta taji dadin maganarshi, tace in sha Allah zan baka hadin kai dr, nagode da kulawarka agare ki, bayan tafiyar jazz ta juya zata shiga dakin har saida suka bangaji juna ita da benazir, taji shiru bata ganta ba shine tabiyota kada asace mata babynta, murmushi unaisah tayi tare da ruko hannunta suka koma cikin dakin, daga jiya zuwa yau wata irin shakuwace mai karfi ta shiga tsakaninsu, duk wani motsin unaisah akan idon benazir ta hanata sukuni tana a maƙale da ita ko toilet bata son ta shiga, tafi son taji dumin jikin ta anata, haka itama unaisah ko tari Benazir tayi saita nuna damuwarta akanta.
Wuraren karfe 12 dr shureim da Alhaji ubaid suka zo asibitin, a bakin kofar dakin jami'an dake sanye da fararen kaya suka dakatar da su suka ce ba abada iznin shiga ciki ba, hankalin dr shureim ba karamin tashi yayi ba saboda baisan da dokar za'a hanasu shiga room din ba, Alhaji ubaid yace bazai yiwuba babu yadda za'ay su hana shi ganin yar shi, tun da harya tako yazo dole ya shiga ya duba lafiyarta, ganin dagaske ba zasu bari su shiga bane yasa dr shureim kiran layin hajiya layla, bayan ta ɗaga ya sanar mata zuwansu, fitowa tayi daga dakin sanye da hijabi, wani irin annurin farin ciki suka gani akan fuskarta, bayan sun gaisa Alhaji ubaid Yace"ya mai jikin? Ina fata jikin nata da sauki. " murmushi hajiya layla tayi"mai jiki Alhamdulillah, benazir ta fara samun lafiya, shureim bai fada maka abun farin cikin daya faru jiya ba"? Murmushi alhaji ubaid yayi"ya fada min, wlh naji dadi nayi murna naso ace na gana da iyayen yarinyar don inyi masu godiya"
labari ta fara basu na abunda ya faru da safen nan ta ƙara da cewa"yarinyar tana da wayou, baka ganta ba kamar benazir dince ta haifata sunyi kama, abunda yafi daure mun kai shakuwar su baka ga yadda suke tarairayar junansu ba. " wani irin dadine Ya lullu6e dr shurem da Alhaji ubaid
"Alhamdulillah, ubangiji Allah Yasa yarinyar ta zama silar warakarta. " suka amsa mashi da ameen
"Yanzu ba zamu samu ganin Benazir din ba"? Alhaji ubaid ne yayi maganar,
Hajiya layla tace"ba zasu bari ku ganta ba, kuyi hakuri kawai har zuwa lokacin da zasu salleme mu"
Dr shureim Yace"gaskiya ni bazan iya hakura ba, ina son ganin yar uwata..Alhaji ubaid yace ni bansan dalilin kafa dokar ba, in ma za'a hana wani ya shiga ay dai ba a hana ni ba, ni da nake mahaifinta.." kiri kiri jami'an suka hana su shiga ciki gashi sun kwallafa rai akan son ganin su, zuwan dr jazz ne Ya sama masu maslaha, da farko yayi kokarin fahimtar da su dangane da dalilin dayasa suka hana shiga, Yace iyayen yarinyar ne basa son wani abu ya samu yar su, shiyasa suka sanya tsaro a asibitin bayan haka basu san wani abu da zaisa ita benazir din ta gane ba mamanta bace" Alhaji ubaid yace su dai a taimaka abarsu su ganta.."_ ganin ya kafe ne yasa dr jazz ya kira chief a waya ya sanar da shi dangane da zuwansu Alhaji ubaid, shiru yayi jim yana nazari dama don saboda Alhaji ubaid suka kafa dokar amma daya tuna yadda taj ya fada masa ya yi ma unaisah bayani akan ko wani ya nuna ya santa kada ta nuna ta sanshi, ya dai san in suka hadu idan ta ganshi zata iya gane shi tun da yarinyar da wayon ta amma bai kamata su hana family din mara lafiyan ganin ta ba zasu iya zargin wani abu, hakan yasa chief furta"Jazz ku bar su su shiga, amma kada su ɗauki lokaci, sannan ka sanya ido akan su bana son fira mai tsayi ta shiga tsakanin su da yarinyar .." amsa mashi yayi da toh, bayan sun gama wayar ya sanar da su Alhaji ubaid sun samu iznin shiga amma kada su wuce mintuna biyar, lokacin da suka shiga unaisah ta shiga toilet, bata samu ganin su ba, ta dai jiyo muryoyinsu a dakin suna magana, sunyi jiran fitowarta amma har time ya cika ba ta fito ba, sai bayan da suka fita daga ɗakin kafin ta fito daga ciki.
"Mommy wlh bata nan, ta 6ace, wani ya sace min ita, nama san taj ne Ya gudu da ita saboda yana jin haushina...." saukowa tayi daga kan gadon ta durkusa tana leƙen karkashin gadon sumar kanta duk ta rufe fuskarta da bayanta...
"Benazir me kikeyi anan ki tashi mana, nace maki yarki tana atare dake yanzu zata fito, Ki zo ki sha maganin ki, ga breakfast an kawo mana..." ta faɗa tare da ruko hannunta, fashewa tayi kuka tana fadin"wayyo Allahna mami, wlh babu ita, na shiga uku na bani na lalace, baby ta 6ace..." duk yadda hajiya layla taso ta shawo kanta abun Ya faskara gaba daya nema take ta zauce...
Motsin buɗe kofar toilet ne Ya katse mata kukan nata, a firgice ta juya tana kallon kofar tana faman zare dara daran idanunta, tundaga kasa ta fara kallon kafafuwanta dake asanye da slippers farare tas da su, da sauri benazir ta wurga idanunta kan fuskarta, harsaida ta lumshe su saboda wani sanyi daya ratsa zuciyarta, fitowarta kenan daga wanka, doguwar riga ce a jikin ta pink colour tayi wani fresh da ita kamar babu damuwa atare da ita.
Ƙurawa juna ido sukayi batare da kyaftawa ba, hajiya layla dake kallon su tsabar murna bakinta yaƙi rufuwa yadda kasan gonar auduga.
Cikin sanyin murya unaisah ta furta"mamana! Kin tashi lafiya! Ya jikin naki? Kin farka baki ganni ba am sorry na shiga toilet yin wanka ne..." wani irin bugu zuciyar Benzar tayi yanayin fuskarta ya nuna kamar tana kokarin dawowa hayyacin ta ne.
Murmushi Angel ta sakar mata har dimple dinta suka lotsa, kamar ta samu tv haka ta ƙura mata ido tana kallon ta.
"Benazir baki gane ta ba? Babyn da kike nema ce, Kije wurin ta..." jikinta na 6ari kamar mazari ta mike ta nufi unaisah, tana karasawa ta zube kan gwiwowinta ta sanya hannu biyu tayi huggin dinta tightly akan kirjinta, wani irin yanayi suka tsinci kansu mara misaltuwa, kusan a tare heart dinsu ke bugu da karfi da karfi, tuni kwalla sun cika idanun kowan nan su.
"Babyna ne"? Ta fada tare da tallabo fuskar unaisah ta ƙura mata ido tana faman zare mata idanunta har saida gaban angel ya fadi tarasa gane meyasa take jin ta kamar mahaifiyarta.
"Kinyi shiru baki amsa min ba! Baby na ne? Ke ce? Ta fada tana ɗage mata eye brows dinta.
Jinjina mata kai unaisah tayi"ni ce mamana" yawu benazir ta haɗiya kafin ta furta"taj ne Ya kawo min ke uhum? Yana ina"? Rass gaban Angel Ya faɗi ta zaro ido tare da kallon hajiya layla wadda ta kura masu ido tana kallon su gwanin ban sha'awa.
Lamarin ya daure mata kai, meyasa take ambaton sunanta da sunan daddynta? To kodai itama sunan yarta ne da mijinta hakan? Abun da daure kai, tayaya akai sunan su yazo ɗaya"? Ta jefa ma kanta tambayar da bata da amsar ta, ranta ne ya raya mata ay ba ita kadaice me irin nickname dinta ba suna dayawa, shima sunan taj din ba daddynta kadai ke da shi ba, hakan yasa ta saki jikin ta.
Jinjina mata kai tayi"daddyna ne Ya kawo ni, shima yana nan zaizo wurinki amma sai kin kwantar da hankalinki..." cike da zumudi tace toh toh zan kwantar da hankalina..."
Huggin dinta unaisah ta karayi wani irin dadi takeji, ta dade batayi bacci mai dadi irin na jiya ba, bata ta6a zaton zata iya runtsawa ba saboda halin damuwar datake a ciki na abun da ya faru tsakaninta da Danish amma cikin ikon Allah silar baiwar Allahn nan jiya tayi bacci mai nauyi kuma ta samu relief na radadin da zuciyarta keyi mata.
"Mamana, Ki shiga toilet, kiyi wanka zaki ji dadin jikin ki, Idan kika fito dakaina zan baki abinci abaki .." wani irin dadine Ya lullu6e benazir, da sauri ta kalli hajiya layla idanunta cike tab da kwalla tace"mommy tana sona sosai, dama nasan bazata guje ni ba, saboda ita jinina nace, kuma tasan bada san raina na gudu nabarta ba..."
rass gaban angel ya fadi maganar benazir ta jefata arudani, lokaci daya brain dinta tafara tariyo mata labarin mamanta data gudu tabarta a kwamin wanka, tuni yanayin fuskarta ya canza zuwa tsantsar 6acin rai, gani take kamar yawancin iyaye mata basu da tausayin ya'yansu shiyasa suka watsar da su bayan sun haife su.
"Benazir ki shiga kiyi wankan, babynki zata jiraki anan" jikin ta na rawa ta mike ta shiga toilet din, tun zuwansu hajiya layla ke taimaka mata tayi wanka saboda rashin nutsuwar da bata da ita, amma yau da kanta tayi wanka abun ba karamin dadi yayi ma hajiya layla ba, atare suka zauna da angel ta fara bata abinci abaki tana ci sai dadi take ji, ita ma ta dauki spoon ta debo ta sanya ma angel abaki hajiya layla nata kallon su gwanin ban sha'awa bayan sun kammala cin abinci, dr jazz ya shigo duba lafiyar benazir shi kanshi ya fahimci nasarar da suka fara samu don alamu sun nuna takusa regaining hankalin ta....yau ko allura ba'ayi mata ba, magungunanta kadai suka bata tasha.
Kafin dr jazz yabar dakin saida Ya kira unaisah, suka ke6e a kofar dakin ya tambayeta meke damunta? Chief ya fada mashi bata da lafiya..." murmushi tayi masa kafin tace"ba abunda ke damuna, lafiyata qalou.." lallashinta ya dinga yi yana lalla6ata duk don ta fada mashi amma ta nace akan ita lafiyarta qalou, yace toh shikenan idan akwai wani abu da kike bukata ki sanar dani, chief ya bani amanarki bana son ganin damuwa atare dake, har cikin ranta taji dadin maganarshi, tace in sha Allah zan baka hadin kai dr, nagode da kulawarka agare ki, bayan tafiyar jazz ta juya zata shiga dakin har saida suka bangaji juna ita da benazir, taji shiru bata ganta ba shine tabiyota kada asace mata babynta, murmushi unaisah tayi tare da ruko hannunta suka koma cikin dakin, daga jiya zuwa yau wata irin shakuwace mai karfi ta shiga tsakaninsu, duk wani motsin unaisah akan idon benazir ta hanata sukuni tana a maƙale da ita ko toilet bata son ta shiga, tafi son taji dumin jikin ta anata, haka itama unaisah ko tari Benazir tayi saita nuna damuwarta akanta.
Wuraren karfe 12 dr shureim da Alhaji ubaid suka zo asibitin, a bakin kofar dakin jami'an dake sanye da fararen kaya suka dakatar da su suka ce ba abada iznin shiga ciki ba, hankalin dr shureim ba karamin tashi yayi ba saboda baisan da dokar za'a hanasu shiga room din ba, Alhaji ubaid yace bazai yiwuba babu yadda za'ay su hana shi ganin yar shi, tun da harya tako yazo dole ya shiga ya duba lafiyarta, ganin dagaske ba zasu bari su shiga bane yasa dr shureim kiran layin hajiya layla, bayan ta ɗaga ya sanar mata zuwansu, fitowa tayi daga dakin sanye da hijabi, wani irin annurin farin ciki suka gani akan fuskarta, bayan sun gaisa Alhaji ubaid Yace"ya mai jikin? Ina fata jikin nata da sauki. " murmushi hajiya layla tayi"mai jiki Alhamdulillah, benazir ta fara samun lafiya, shureim bai fada maka abun farin cikin daya faru jiya ba"? Murmushi alhaji ubaid yayi"ya fada min, wlh naji dadi nayi murna naso ace na gana da iyayen yarinyar don inyi masu godiya"
labari ta fara basu na abunda ya faru da safen nan ta ƙara da cewa"yarinyar tana da wayou, baka ganta ba kamar benazir dince ta haifata sunyi kama, abunda yafi daure mun kai shakuwar su baka ga yadda suke tarairayar junansu ba. " wani irin dadine Ya lullu6e dr shurem da Alhaji ubaid
"Alhamdulillah, ubangiji Allah Yasa yarinyar ta zama silar warakarta. " suka amsa mashi da ameen
"Yanzu ba zamu samu ganin Benazir din ba"? Alhaji ubaid ne yayi maganar,
Hajiya layla tace"ba zasu bari ku ganta ba, kuyi hakuri kawai har zuwa lokacin da zasu salleme mu"
Dr shureim Yace"gaskiya ni bazan iya hakura ba, ina son ganin yar uwata..Alhaji ubaid yace ni bansan dalilin kafa dokar ba, in ma za'a hana wani ya shiga ay dai ba a hana ni ba, ni da nake mahaifinta.." kiri kiri jami'an suka hana su shiga ciki gashi sun kwallafa rai akan son ganin su, zuwan dr jazz ne Ya sama masu maslaha, da farko yayi kokarin fahimtar da su dangane da dalilin dayasa suka hana shiga, Yace iyayen yarinyar ne basa son wani abu ya samu yar su, shiyasa suka sanya tsaro a asibitin bayan haka basu san wani abu da zaisa ita benazir din ta gane ba mamanta bace" Alhaji ubaid yace su dai a taimaka abarsu su ganta.."_ ganin ya kafe ne yasa dr jazz ya kira chief a waya ya sanar da shi dangane da zuwansu Alhaji ubaid, shiru yayi jim yana nazari dama don saboda Alhaji ubaid suka kafa dokar amma daya tuna yadda taj ya fada masa ya yi ma unaisah bayani akan ko wani ya nuna ya santa kada ta nuna ta sanshi, ya dai san in suka hadu idan ta ganshi zata iya gane shi tun da yarinyar da wayon ta amma bai kamata su hana family din mara lafiyan ganin ta ba zasu iya zargin wani abu, hakan yasa chief furta"Jazz ku bar su su shiga, amma kada su ɗauki lokaci, sannan ka sanya ido akan su bana son fira mai tsayi ta shiga tsakanin su da yarinyar .." amsa mashi yayi da toh, bayan sun gama wayar ya sanar da su Alhaji ubaid sun samu iznin shiga amma kada su wuce mintuna biyar, lokacin da suka shiga unaisah ta shiga toilet, bata samu ganin su ba, ta dai jiyo muryoyinsu a dakin suna magana, sunyi jiran fitowarta amma har time ya cika ba ta fito ba, sai bayan da suka fita daga ɗakin kafin ta fito daga ciki.