Sashe 37
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dafe kanshi yai da hannu ɗaya saboda shi ma ya yarda da maganar ummi, cikin muryar lallashi Yace"Unaisah, bani ne nayi maki wanka ba, Aunty umminku ce, bayan na dawo dake jiya na kawo ki gida da taimakonta kika tsarkake jikinki har kikayi wanka.. " kafin Ya kare maganar, cikin muryar kuka tace"ni ba wannan bane damuwana ba, daddy meyasa za ka yi min haka?
Hankali atashe taj ya ɗan zaro idanu Ya dubi ummi babu alamun ya fahimci abunda Unaisah take nufi sai ma cewa yayi"kinyi mafarki ne da daddynki"? A tsiwace tace"ba mafarki nayi dashi ba, a zahiri na ganshi jiya, saboda me zaka dinga 6oye min kanka daddy, ko ka daina sona ne" ta faɗa tana haki
Dariya ce ta kubcewa ummi ganin yadda taj ya daura hannayensu biyu saman kanshi alamar Ya shiga Uku gaba daya yabi ya ruɗe Sai lokacin Ya tuna da abun da Ya faru Jiya, da kanshi Ya cire facemask dinsa Ya jefar da shi saboda baya ahayyacinsa ashe idonta biyu taga fuskarshi
Muryarshi tamkar zai fashe da kuka Yace"am really sorry my Angel, nayi laifi ay min afwa, nasan ban kyauta maki ba, amma dan Allah ki fahimce ni, ki nutsu ki saurari me zan fada maki.." kafin ya kare maganar ta katse shi da cewa"ni bazan saurari komai ba daddy, kawai ka daina sona ne ba ka damu dani ba, kuma ba ka yi kewata ba shiyasa kake 6oye min fuskarka..." ta fada tana jan majina kafin taci gaba da cewa"Daddy, what did I do to deserve this punishment from you? Daddy kasan kuwa irin kalubalan rayuwar dana fuskan ta? Daddy duk halin da na shiga ban ta6a mantawa dakai ba, bana kwana batare da na sanya ka acikin addu'ata ba, kullum zullumina ya rayuwar daddyna ta ƙare? Meya faru da shi bayan Ya jefa ni cikin ruwa, Ya rayu ko ya mutu.... "
Ba ta kare maganar ba saboda kukan daya ciyota, ta kuma fashewa da wani kuka tamkar ana zare ranta, abunne Ya tsaya mata aranta ya 6ata mata rai duk irin kewansa da tayi amma shine ya boye mata kansa.
Gaba ɗaya hankulansu Sajeed Ya koma kan fuskar tajuddeen, kalaman Angel ne suka fahimtar da su wanene shi
Muryar na rawa Azeeza tace"dama kai ne daddyn Angel wanda kullum take bamu labarin shi"?
Da sauri Parveen tace"idan bazan manta ba, duk in muka zauna fira unaisah saita bamu labarinka, itace tafara sanya mana kwaɗayin ganin ka, da zumudin son muje gidan su don muyi rayuwar ƴan ci, har fada mana takeyi daddyn ta zai kar6emu kamar ya'yansa..... Kasa karasa maganar tayi nan take ta fashe da kuka.
Cikin karyayyar murya Batool tace"ashe kai ne daddyn Angel, Ni burin da nake dashi idan Allah yasa na haɗuwa dakai shine inyi maka godiya saboda Angel ta faɗa min kaine ka ilmantar da ita, ka tsaya mata tsayin daka har ta samu ilmin addinin da take da shi, uwa uba kaine silar da Angel tazo duniya...." tana magana hawaye na wanke fuskarta.
"Wallahi ba mu ta6a sanin wanene mahaliccin mu ba, sai a sanadin zuwan Angel GIDAN KURKUKUN ƘADDARA, , In da mu ka yi rayuwar kulle, cikin duhun jahil ci, harta toilet atare muke shiga da ƴan uwanmu maza Angel itace ta tsawatar mana ta fada mana cewa babu kyau mu daina haramunne wani yaga tsiraicin wani......" kuka ne ya kubce ma batool, ummi dake sauraransu a matuƙar ruɗe take ɗan zare idanunta akan fuskokinsu, gaba ɗaya sun jefa ta a cikin ruɗani lamarin yayi muƙar girgiza ta, tayi matukar razana.
Bata gama shan mamaki ba cikin sanyin murya haris Yace"Allah ne kadai zai iya biyanka daddy, zuwan Angel cikin rayuwarmu tamkar baiyanar haske ne a cikin duhu, wallahi baki bazai iya furta irin wahalar da unaisah tayi akanmu ba, duk da kasancewar ta ƙarama a cikin mu amma tana da kaifin basira kuma tana da hankali, Angel ta zama jigo na rayuwarmu, ta share mana hawayenmu a lokacin da muke kukan radadin kuncin rayuwar da muke aciki, Angel uwace agare mu, saboda ta kwatar mana ƴancin mu da aka tauye mana......" zu6ewa haris yayi kan gwiwowinsa hawaye naci gaba da sintiri kan fuskarsa, Gaba ɗaya sun gama kashe ma tajuddeen jikinsa, yayi sanyi laƙwas zuciyarsa ta karaya, wasu irin zafafan hawayene masu ɗumi suka soma wanko fuskarshi yayin da yake kallonsu ɗaya bayan daya, yana mai jin tsantsar tausayin su da kaunarsu azuciyarshi, Angel ta gama masa komai a duniyar nan baisan ma ina zai tsoma kanshi ba tsabar yadda Yake jin mahaukacin sonta na kara nunkuwa acikin zuciyarshi, ba zai iya misalta irin alfarin da ya ke da ita, burin kowani ubane ya sami ƴa kamar Angel wadda zata kare masa martabarsa da kimarsa a idon duniya, wadda zata daukaka darajarsa ta kuma yi silar shigar shi aljanna, hannu ɗaya ya daura akanshi Yana cigaba da kallon su jikin shi har kerna kerma ya ke yi.
Duk wannan abun dake faru a kunnan chief owais da Big guy wadanda basu jima da zuwa bakin kofar dakin ba, sunzo zo ne don su duba jikin Unaisah sai kuma suka ji abunda ba suyi tsammani ba wannan dalilin ne yasa suka dakata suna sauraron su
Cikin shessheƙar kuka Naufal Yace"daddy duk yadda zamuyi maka bayani ba lallai ka fahimce mu, amma wallahi muna kaunarka muna son ka daddyn Angel" wasu hawayen nan suka kuma wanke fuskar taj, idanunshi sunyi jawur da su gaba ɗaya ya rasa bakin magana sai dai kallonsu da yake tayi gwanin ban tausayi
"Unaisah itace take ƙarfafa mana gwiwa, itace komai namu, itace muke gani muji dadi, unaisah ko mun 6ata mata rai bata yin fushi damu ba, sai ma taja mu ajikinta saboda tasan bayin kan mu bane, rayuwa mu ke a cikin duhun jahilci, ....."
gaba ɗaya suka dubi batool da ta dauko maganar hawaye na sintiri kan kuncinta, dakatawa tayi da yin maganar na ɗan wani lokaci kafin taja numfashi taci gaba cewa"ɗaya daga cikin abun da unaisah tayi wanda har a bada bazai ta6a gogewa acikin zuciyata ba, shine musuluntar da yar uwar mu unaiza da tayi, unaisah bata bari unaizah ta mutu a matsayin arniya ba, sai da ta taimaka mata ta kar6i shahada duk don saboda ta tsira a lahira..." muryarta na rawa tayi maganar, kusan atare suka rushe da kuka tunawa da yar uwarsu unaizah, maganar batool ta fama masu raunin dake acikin zuciyoyin su.
zu6ewa su ka yi gaba dayansu saman gwiwowinsu agaban tajuddeen, suna kuka yana kuka babu mai lallashin wani a cikin su, ummi da batasan kan zancen nasu ba tuni itama ta fara matsar ƙwalla cikin rauni na murya tace dan Allah ku fahimtar dani ku yi min bayani tun kafin zuciyata ta buga, saboda hankalina ya tashi na kwaɗaitu da son jin tarihin rayuwarku......."
Lumshe ido chief owais yayi, zuciyarshi ta karaya, wankan suit ne ajikin shi, bai jima da dawowa daga Airport ba wurin rakiyar prime minister.
A hankali Ya dubi Big guy dake a tsaye gefen sa, hawaye ya gani sun cika mashi idanunshi,
Shi kanshi dauriya ce kawai, amma kalaman su sun ta6a ta6a zuciyarsa.
Cikin sanyin murya ya furta"ka kira salsabeel a waya ka faɗa masa inji ni ya shirya sauran yaran, su zo nan gida su sameni, inaso suga yan uwansu"
cikin girmamawa big guy yace"okey, sir." ya faɗa tare da zaro wayarshi ya danna ma salsabeel kira wayar na fara ringing, yayi picking,
"barka da safiya yalla6ai"
"Yawwa barka, Ina fata dai ban katse maka baccinka ba" muryarshi da yar dariya yace"ay bana yin baccin safe saboda khadeeja kasan halinta kamar mai fama da cutar yunwa, tun da safe take tashina, don in shiga kitchen in dafa mata indomie"
"Allah sarki, ka cigaba da haƙuri da ita, Yanzu dai gani tare da chief, yace yana son ganin ka da sauran yaran yanzun nan ku same mu agidansa"
Muryar salsaleen da dan rudani yace"yallabai badai wani abune ya faru ba? Naji kace nazo da yara da sassafen nan"
"Ba wani abu kazo kawai, " amsa mashi yayi da toh, kafin su ka yi sallama Ya maida wayar cikin aljihu...
Angel dake atsugunne bakin kofar toilet din, jikinta ya gama yin sanyi tamkar wadda aka zarewa laka, duk abunda su batool ke fadi akan kunnanta tuni tayi shiru ta dakata da yin kukan, ita kanta bata ta6a tsammanin sun ruƙe kyautatawar da take yi masu ba acikin zuciyoyin su, shiyasa ake son bawa ya kasance yana aikata abun alkhairi arayuwarsa saboda duniya tayi alfahari dashi, al'umma su yi koyi dashi ko bayan ba ranshi, unaisah dai ta bada gudummuwa ta bangarori da dama harta ta bangaren addinin musulunci ta musuluntar kuma ta fadakar Allah ne kaɗai zai iya biyan ta.
Cikin shessher kuka suka soma yi mata magana, muryoyinsu duk sun disashe
"Yar uwarmu rabin ranmu, amadadin abban mu, muna baki hakuri dan Allah ki taimaki daddynmu, Kiyi hakuri ki fito yana son ganinki, daddy ya gane kuskurenshi kuma ashirye yake daya baki hakurin laifin da yayi maki.... " magiya suka dinya yi mata duk don su samu ta buɗe masu kofa
"Unaisah kin manta irin kyautatawar da daddynmu yayi maki tun kina karamarki, lokacin da mommynki ta gudu tabar ki a cikin kwamin wanka, ya daukeki yaci gaba da baki kulawa duk da kasancewar bakyajin magana ahaka yaci gaba da rainonki saboda irin son da ya ke yi maki shi bai tafi yabar ki ba, unaisah da bakin ki ki bamu labarin nan ko kin manta ne......" gaba ɗaya kowan nan su ya ƙosa ta fito saboda ta rungumi daddynta.
Ba zato ba tsammani, suka ga taj Ya dafe saitin zuciyarshi yana ambaton inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un Muryarshi da wani irin sauti na tashin hankali, gaba ɗaya suka zabura da sauri suka rufe shi suna ambaton daddy meke damunka? Baka da lafiya ne...."
Hankali atashe taj ya ɗan zaro idanu Ya dubi ummi babu alamun ya fahimci abunda Unaisah take nufi sai ma cewa yayi"kinyi mafarki ne da daddynki"? A tsiwace tace"ba mafarki nayi dashi ba, a zahiri na ganshi jiya, saboda me zaka dinga 6oye min kanka daddy, ko ka daina sona ne" ta faɗa tana haki
Dariya ce ta kubcewa ummi ganin yadda taj ya daura hannayensu biyu saman kanshi alamar Ya shiga Uku gaba daya yabi ya ruɗe Sai lokacin Ya tuna da abun da Ya faru Jiya, da kanshi Ya cire facemask dinsa Ya jefar da shi saboda baya ahayyacinsa ashe idonta biyu taga fuskarshi
Muryarshi tamkar zai fashe da kuka Yace"am really sorry my Angel, nayi laifi ay min afwa, nasan ban kyauta maki ba, amma dan Allah ki fahimce ni, ki nutsu ki saurari me zan fada maki.." kafin ya kare maganar ta katse shi da cewa"ni bazan saurari komai ba daddy, kawai ka daina sona ne ba ka damu dani ba, kuma ba ka yi kewata ba shiyasa kake 6oye min fuskarka..." ta fada tana jan majina kafin taci gaba da cewa"Daddy, what did I do to deserve this punishment from you? Daddy kasan kuwa irin kalubalan rayuwar dana fuskan ta? Daddy duk halin da na shiga ban ta6a mantawa dakai ba, bana kwana batare da na sanya ka acikin addu'ata ba, kullum zullumina ya rayuwar daddyna ta ƙare? Meya faru da shi bayan Ya jefa ni cikin ruwa, Ya rayu ko ya mutu.... "
Ba ta kare maganar ba saboda kukan daya ciyota, ta kuma fashewa da wani kuka tamkar ana zare ranta, abunne Ya tsaya mata aranta ya 6ata mata rai duk irin kewansa da tayi amma shine ya boye mata kansa.
Gaba ɗaya hankulansu Sajeed Ya koma kan fuskar tajuddeen, kalaman Angel ne suka fahimtar da su wanene shi
Muryar na rawa Azeeza tace"dama kai ne daddyn Angel wanda kullum take bamu labarin shi"?
Da sauri Parveen tace"idan bazan manta ba, duk in muka zauna fira unaisah saita bamu labarinka, itace tafara sanya mana kwaɗayin ganin ka, da zumudin son muje gidan su don muyi rayuwar ƴan ci, har fada mana takeyi daddyn ta zai kar6emu kamar ya'yansa..... Kasa karasa maganar tayi nan take ta fashe da kuka.
Cikin karyayyar murya Batool tace"ashe kai ne daddyn Angel, Ni burin da nake dashi idan Allah yasa na haɗuwa dakai shine inyi maka godiya saboda Angel ta faɗa min kaine ka ilmantar da ita, ka tsaya mata tsayin daka har ta samu ilmin addinin da take da shi, uwa uba kaine silar da Angel tazo duniya...." tana magana hawaye na wanke fuskarta.
"Wallahi ba mu ta6a sanin wanene mahaliccin mu ba, sai a sanadin zuwan Angel GIDAN KURKUKUN ƘADDARA, , In da mu ka yi rayuwar kulle, cikin duhun jahil ci, harta toilet atare muke shiga da ƴan uwanmu maza Angel itace ta tsawatar mana ta fada mana cewa babu kyau mu daina haramunne wani yaga tsiraicin wani......" kuka ne ya kubce ma batool, ummi dake sauraransu a matuƙar ruɗe take ɗan zare idanunta akan fuskokinsu, gaba ɗaya sun jefa ta a cikin ruɗani lamarin yayi muƙar girgiza ta, tayi matukar razana.
Bata gama shan mamaki ba cikin sanyin murya haris Yace"Allah ne kadai zai iya biyanka daddy, zuwan Angel cikin rayuwarmu tamkar baiyanar haske ne a cikin duhu, wallahi baki bazai iya furta irin wahalar da unaisah tayi akanmu ba, duk da kasancewar ta ƙarama a cikin mu amma tana da kaifin basira kuma tana da hankali, Angel ta zama jigo na rayuwarmu, ta share mana hawayenmu a lokacin da muke kukan radadin kuncin rayuwar da muke aciki, Angel uwace agare mu, saboda ta kwatar mana ƴancin mu da aka tauye mana......" zu6ewa haris yayi kan gwiwowinsa hawaye naci gaba da sintiri kan fuskarsa, Gaba ɗaya sun gama kashe ma tajuddeen jikinsa, yayi sanyi laƙwas zuciyarsa ta karaya, wasu irin zafafan hawayene masu ɗumi suka soma wanko fuskarshi yayin da yake kallonsu ɗaya bayan daya, yana mai jin tsantsar tausayin su da kaunarsu azuciyarshi, Angel ta gama masa komai a duniyar nan baisan ma ina zai tsoma kanshi ba tsabar yadda Yake jin mahaukacin sonta na kara nunkuwa acikin zuciyarshi, ba zai iya misalta irin alfarin da ya ke da ita, burin kowani ubane ya sami ƴa kamar Angel wadda zata kare masa martabarsa da kimarsa a idon duniya, wadda zata daukaka darajarsa ta kuma yi silar shigar shi aljanna, hannu ɗaya ya daura akanshi Yana cigaba da kallon su jikin shi har kerna kerma ya ke yi.
Duk wannan abun dake faru a kunnan chief owais da Big guy wadanda basu jima da zuwa bakin kofar dakin ba, sunzo zo ne don su duba jikin Unaisah sai kuma suka ji abunda ba suyi tsammani ba wannan dalilin ne yasa suka dakata suna sauraron su
Cikin shessheƙar kuka Naufal Yace"daddy duk yadda zamuyi maka bayani ba lallai ka fahimce mu, amma wallahi muna kaunarka muna son ka daddyn Angel" wasu hawayen nan suka kuma wanke fuskar taj, idanunshi sunyi jawur da su gaba ɗaya ya rasa bakin magana sai dai kallonsu da yake tayi gwanin ban tausayi
"Unaisah itace take ƙarfafa mana gwiwa, itace komai namu, itace muke gani muji dadi, unaisah ko mun 6ata mata rai bata yin fushi damu ba, sai ma taja mu ajikinta saboda tasan bayin kan mu bane, rayuwa mu ke a cikin duhun jahilci, ....."
gaba ɗaya suka dubi batool da ta dauko maganar hawaye na sintiri kan kuncinta, dakatawa tayi da yin maganar na ɗan wani lokaci kafin taja numfashi taci gaba cewa"ɗaya daga cikin abun da unaisah tayi wanda har a bada bazai ta6a gogewa acikin zuciyata ba, shine musuluntar da yar uwar mu unaiza da tayi, unaisah bata bari unaizah ta mutu a matsayin arniya ba, sai da ta taimaka mata ta kar6i shahada duk don saboda ta tsira a lahira..." muryarta na rawa tayi maganar, kusan atare suka rushe da kuka tunawa da yar uwarsu unaizah, maganar batool ta fama masu raunin dake acikin zuciyoyin su.
zu6ewa su ka yi gaba dayansu saman gwiwowinsu agaban tajuddeen, suna kuka yana kuka babu mai lallashin wani a cikin su, ummi da batasan kan zancen nasu ba tuni itama ta fara matsar ƙwalla cikin rauni na murya tace dan Allah ku fahimtar dani ku yi min bayani tun kafin zuciyata ta buga, saboda hankalina ya tashi na kwaɗaitu da son jin tarihin rayuwarku......."
Lumshe ido chief owais yayi, zuciyarshi ta karaya, wankan suit ne ajikin shi, bai jima da dawowa daga Airport ba wurin rakiyar prime minister.
A hankali Ya dubi Big guy dake a tsaye gefen sa, hawaye ya gani sun cika mashi idanunshi,
Shi kanshi dauriya ce kawai, amma kalaman su sun ta6a ta6a zuciyarsa.
Cikin sanyin murya ya furta"ka kira salsabeel a waya ka faɗa masa inji ni ya shirya sauran yaran, su zo nan gida su sameni, inaso suga yan uwansu"
cikin girmamawa big guy yace"okey, sir." ya faɗa tare da zaro wayarshi ya danna ma salsabeel kira wayar na fara ringing, yayi picking,
"barka da safiya yalla6ai"
"Yawwa barka, Ina fata dai ban katse maka baccinka ba" muryarshi da yar dariya yace"ay bana yin baccin safe saboda khadeeja kasan halinta kamar mai fama da cutar yunwa, tun da safe take tashina, don in shiga kitchen in dafa mata indomie"
"Allah sarki, ka cigaba da haƙuri da ita, Yanzu dai gani tare da chief, yace yana son ganin ka da sauran yaran yanzun nan ku same mu agidansa"
Muryar salsaleen da dan rudani yace"yallabai badai wani abune ya faru ba? Naji kace nazo da yara da sassafen nan"
"Ba wani abu kazo kawai, " amsa mashi yayi da toh, kafin su ka yi sallama Ya maida wayar cikin aljihu...
Angel dake atsugunne bakin kofar toilet din, jikinta ya gama yin sanyi tamkar wadda aka zarewa laka, duk abunda su batool ke fadi akan kunnanta tuni tayi shiru ta dakata da yin kukan, ita kanta bata ta6a tsammanin sun ruƙe kyautatawar da take yi masu ba acikin zuciyoyin su, shiyasa ake son bawa ya kasance yana aikata abun alkhairi arayuwarsa saboda duniya tayi alfahari dashi, al'umma su yi koyi dashi ko bayan ba ranshi, unaisah dai ta bada gudummuwa ta bangarori da dama harta ta bangaren addinin musulunci ta musuluntar kuma ta fadakar Allah ne kaɗai zai iya biyan ta.
Cikin shessher kuka suka soma yi mata magana, muryoyinsu duk sun disashe
"Yar uwarmu rabin ranmu, amadadin abban mu, muna baki hakuri dan Allah ki taimaki daddynmu, Kiyi hakuri ki fito yana son ganinki, daddy ya gane kuskurenshi kuma ashirye yake daya baki hakurin laifin da yayi maki.... " magiya suka dinya yi mata duk don su samu ta buɗe masu kofa
"Unaisah kin manta irin kyautatawar da daddynmu yayi maki tun kina karamarki, lokacin da mommynki ta gudu tabar ki a cikin kwamin wanka, ya daukeki yaci gaba da baki kulawa duk da kasancewar bakyajin magana ahaka yaci gaba da rainonki saboda irin son da ya ke yi maki shi bai tafi yabar ki ba, unaisah da bakin ki ki bamu labarin nan ko kin manta ne......" gaba ɗaya kowan nan su ya ƙosa ta fito saboda ta rungumi daddynta.
Ba zato ba tsammani, suka ga taj Ya dafe saitin zuciyarshi yana ambaton inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un Muryarshi da wani irin sauti na tashin hankali, gaba ɗaya suka zabura da sauri suka rufe shi suna ambaton daddy meke damunka? Baka da lafiya ne...."