Sashe 64
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaune ya ke kan sofa ya ɗaura ƙafarsa ɗaya bisa ɗaya, yayin da idanunsa ke akan laptop din gabansa da yake operating lokaci ɗaya ya ɗan dakata Ya jingina bayansa jikin Sofa haɗi da lumshe idanunsa zuciyarsa a cike take fal da tunanin prettynsa har yau jiran hajiya laurat yake yi don jin amsarta, tun jiya bayan kammaluwar dinner din hateem ziyad ya nemi alfarmar yin magana da ita bayan sun ke6e cikin girmamawa ya gaishe ta, ta amsa masa daga bisani ya fara kora mata jawabi game da bukatarsu, lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya canza zuwa 6acin rai kamar bata son zancen Benazir da yake yi mata, acikin ranta tayi mamakin jin cewa a hannun Zaki ta faɗa ita sam ta manta da rayuwar benazir tamkar ma ba'a halicce ta adoron duniya ba, saboda tun fil azal hajiya laura basa ga maciji da hajiya layla wata irin gaba ce atsakaninsu shiyasa bata shiga shirgin abun da ya shafi layla, a lokaci shi kanshi ziyad ya lura da 6acin ran da take a ciki amma sai ta waske ta ƙaƙaro murmushi tana fadin Allah sarki benazir ashe dama zaki ne ya taimake ta? Alhamdulillah wlh nayi murna ziyad, sai dai abun da ya daure min kaina babu wanda Ya kirani daga gidan Ya fadamin cewa anganta amma in sha Allah zan fidda lokaci inje can gidan da kaina don in tabbatar ta dawo in yaso daga bisani zan tuntu6i shi zaki din...." akan haka suka ƙare magana ziyad yai mata godiya kafin suka rabu.
A hankali Zaki ya buɗe idanunsa Yana kallon ceilling din falon, duk don saboda son haɗuwa da ita, ya ɗaga tafiyarsa canada.
Yayi zurfi a zancen zucin nasa muryar turai ta ratsa kunnansa
"First born barka da hutawa" ta faɗa tare da daura masa mug din coffee kan table, murmushi ya sakar mata, yana ɗaya daga cikin abun da yake burge shi da mommyn nasu in har zata ganshi zaune yana aiki akan laptop sai ta kawo mashi coffee .
"Mom har yanzu baki yi bacci ba"? ya faɗa yana kallon ta.
"Tayaya zan iya runtsawa Jazz bai dawo ba, daddynku bai dawo ba shima, su nake jira su dawo sai in kwanta" tayi maganar tare da ɗaura gwiwowin hannunta bisa ga hand sofa din da zaki yake zaune idanunta akan fuskarsa
"Ko akwai wani abu dake damun ka ne"? Ta fada cikin kulawa
"Babu komai" ya bata amsa atakaice tare da kai hannu ya dauki mug din Ya soma kurbar coffee
"My son, tayaya zaka 6oye min damuwarka, bayan ni mahaifiyarka ce, ta ido kadai ina gane damuwarka, tun lokacin da ka shigo ƙasar nan na lura da damuwa aranka"
Sauke mug din yai kan table kafin ya dubi hajiya turai"nagode da kulawarki agare ni, amma ki kwantar da hankalin ki ba abun da ke damuna"
Gyaɗa kai tay"haka nakeson ji" ta faɗa ne ba dan ta yadda da maganarsa ba tasan baya son taji ne
"Bari na shiga ciki, ka kula min da kanka" amsa mata yai da toh
Bayan tafiyarta ajiyar zuciya ya sauke, bawai baya son fada mata bane yafi son ya fara jin halin da take a ciki in har ta isa gida lafiya, kuma iyayen ta sun kar6eta ba abun da zai hana shi sanar da nashi iyayen labarin ta.
Ƙarfe goma da rabi, jazz da sir mubarak suka dawo gidan lokacin da suka shigo falon tuni Zaki Ya koma room dinsa ba su taras da shi ba,
Hajiya turai na kwance kan gado tajiyo sautin sallamar sa, jikinta har rawa yakeyin wurin saukowa daga kan gadon da sauri ta nufe shi yana atsaye cikin shiga ta kakinsa
"Sannu da dawowa, tun dazu nake ta jiranka nayi kewarka yau kayi dare " cikin nuna kulawa tayi maganar tare da ruko hannunsa suka shiga dakin
"I'm sorry bansanar da ke zan kai dare ba, wani aiki ne mai muhimman ci Ya ruƙe ni" ya faɗa Yana kallon cikin idonta,
"Ba nace ki daina jirana ba? daga kinga nayi dare to ki kwanta kiyi bacci"
Maƙe masa kafaɗa tayi"kai ma kasan bazan iya jurewa ba...." murmushi ya ɗan saki"kinsan me na tuna"? Girgiza mashi kai tay alamar a'a"
"Waɗannan twins din na wurin Owais, ko da yake yace min ba twins bane, ɗaya ta girmi ɗaya" da mamaki hajiya turai tace"ikon Allah, amma nayi mamakin jin hakan komai nasu fa iri ɗaya kamanninsu sun 6ace"
"Zai iya yiwuwa yan gida ɗayane" jinjina kai tay alamar eh
"Yaran sun kwanta min araina, kinsan ni da son ƴa'ƴa mata, duk family dinmu ni kadai ne nake da ya'ya maza ina alfahari da hakan amma inason ya'ya mata, ga hateem nan shi mazan yake so Allah bai bashi ba"
shiru mom turai tayi kamar ta dan shiga damuwa, sam bai lura da halin da ta shiga ba, ya nufi toilet Ya shige jin ƙarar rufe kofar shi Yasa jiki asanyaye ta koma gefen gadonsu ta zauna idanunta sun ciko tab da kwalla..
Ceilling ta ƙurawa ido tana tunano wani abu da ya ta6a faruwa acan lokacin baya shakeru da suka gabata, ta ta6a haihuwa ya'yan suna mutuwa wanda silar hakan Yaja har sir mubarak Ya hanata haihuwar gaba ɗaya gudun kada itama tarasa ranta kamar yadda ya'yan da take haihuwa suke rasa ransu da zarar sun dira a duniya, Allah kadai yasan halin da ta shiga awannan lokacin saboda ta kwallafa rai akan son taga ta haihu da sir mubarak sai dai Allah bai bata ba shiyasa har su hajiya saratu suke yimata gorin sai dai taci ta kasayar
Yunkurawa tayi jiki ba kwari ta mike ta futo daga ɗakin nasu ta nufi bedroom din jazz sai da ta matse kwallar da ta taru a idanunta kafin tayi mashi sallama shiru ba'a amsa mata ba, har ta fara tunanin ko yayi bacci ne, shigarta ke da wuya kwatsam taci karo da wayarsa dake yashe kan floor ga dukkan alamu wurgo da ita yayi, hatta lap coat dinsa anan ya jefar da ita, hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, a razane ta kalli gadonsa a zaune ta same shi tsakiyar mattress, Ya kifa kansa bisa gwiwowin sa, lokaci ɗaya ta rasa sukuninta da sauri ta nufi kayan nashi ta kwashe su ta je ta ajiye masa kafin ta dauko wayar ta nufin gadon nashi ta hau sama ta zauna tana fuskantar shi
"Jazz meke faruwa dakai ne"? ta fada fuskanta dauke da matsananciyar damuwa
Shiru babu alamun zai tanka mata
"Nasan kana ji na jazz, ka ɗago ka kalle ni sannan ka fadamin meke damunka" A hankali Ya ɗago da fuskarsa wadda ta jiƙe sharkaf da hawaye idanunsa sun kaɗa jawur, wani irin bugu taji zuciyarta tai muryarta na rawa ta furta"jazz kuka kake? Meke damunka ne? Ko bakada lafiya ne? Aruɗe ta fada tana shafa fuskarsa
"Jazz dan Allah ka fadamin ko hankalina Ya kwanta" daƙyar Ya iya motsa la66ansa Ya furta sunan faryat, lokacin ɗaya annurin fuskar hajiya turai Ya ɗauke ɗuff, saboda ta fahimci silar shigarshi halin da yake aciki, batasan ya zatai da jazz ba, tayi fama da shi akan ya rabu da faryat amma yaƙiya saboda tasan bazata ta6a auran shi ba, hasalima ma yarinyar bata kwanta mata aranta ba, saboda fitsararta da rashin kunyarta..
"Jazz yaushe ne zaka daina yaudarar kanka akan yarinyar nan? sau nawa ina maka gargadi akan ka fita sabgarta? Na fada maka ba sonka takeyi ba yakamata ka hakura ka nemi wata ay ba ita kadai bace mace a duniya....." kafin ta ƙare maganar ya tarin numfashin ta da cewa"bazan iyaba mommy, Allah ne ya jarabce ni da sonta, wallahi nayi kokarin cireta araina amma na kasa ki tayani da addu'a Allah ya yaye min sonta in ba haka ba zatai silar da zan rasa raina..."
har saida gaban turai Ya fadi jin abun da yace, ta fahimci mahaukacin son da yakema faryat ba lallai Ya fahimce ta ba
"Me tayi maka ne"? labari Ya fara bata na abun da Ya faru tsakaninsu lokacin da ya je wurinta bai 6oye mata komai ba, har nemansa da tayi don ya bata hadin kai,
"Mom kullum na kirata sai ta ci mutuncina, tace wai ni ba namiji bane tunda bazan iya biya mata bukatarta ba, sannan bazata ta6a auran mara asali dan tsohuwar mai aikin gidan su ba...." ya faɗa idanunsa cike tab da kwalla
Ita kanta hajiya turai hawayen ne ke sintiri kan kuncinta, ta tsani taji ana yi mashi gorin asali kamar kanshi farau, ta rasa gane meke damun wasu mutanan sun manta cewa bawa bashi ke daurawa kansa ba? Allah ne Yake kaddara masa rayuwarsa?
"Jazz ta yi kuskure A kalamanta, wallahi sai tayi danasani, saboda ka fi karfinta nesa ba kusa ba, kuma kaine cikakken mai asali tunda kana jin tsoron Allah kuma ka tsare mutuncinka, ni in banda kaddarar so ina kai ina Faryat"? ta faɗa ranta amatuƙar 6ace
"Tafi ni komai tun da tana da asali"
"Kaima kana da asali jazz" da sauri Ya kalle ta
"Mom bangane me kike nufi ba, ke da kanki kika fada min baki da kowa a danginki mahaifina Ya rasu" girgiza kai tayi"na fada maka hakanne saboda ka fidda rai da kowa nawa, bana son maganar jazz ka cigaba da hakuri in sha Allah komai ya kusa zuwa karshe" tun da tafara magana jazz Yake kallonta har yau ya rasa gane dalilin dayasa bata son tayi maganar abun da Ya shafi danginsa, shi dama yasan dole tana da family dinta akwai dai wani abin da take 6oye masa, duk da yana neman ƙarin bayani daga gareta sai dai ya hakura yabarwa zuciyarsa zai cigaba da hakuri kamar yadda ta ce har zuwa lokacin da zata sanar da shi komai....
Shiru sukayi na wani lokaci babu mai magana a cikin su,
"Ina ibad"? ya tambaya yana kallon ta
"Tun bayan sallar Isha' Yai bacci, ya yi jiran dawowarka har fadamin yai ya kira layinka bakai picking ba"
murmushi yayi"Allah sarki ɗan uwana, dama nasan dole ya neme ni, na sanya wayar a silent ne saboda aiki da nakeyi"
A hankali Zaki ya buɗe idanunsa Yana kallon ceilling din falon, duk don saboda son haɗuwa da ita, ya ɗaga tafiyarsa canada.
Yayi zurfi a zancen zucin nasa muryar turai ta ratsa kunnansa
"First born barka da hutawa" ta faɗa tare da daura masa mug din coffee kan table, murmushi ya sakar mata, yana ɗaya daga cikin abun da yake burge shi da mommyn nasu in har zata ganshi zaune yana aiki akan laptop sai ta kawo mashi coffee .
"Mom har yanzu baki yi bacci ba"? ya faɗa yana kallon ta.
"Tayaya zan iya runtsawa Jazz bai dawo ba, daddynku bai dawo ba shima, su nake jira su dawo sai in kwanta" tayi maganar tare da ɗaura gwiwowin hannunta bisa ga hand sofa din da zaki yake zaune idanunta akan fuskarsa
"Ko akwai wani abu dake damun ka ne"? Ta fada cikin kulawa
"Babu komai" ya bata amsa atakaice tare da kai hannu ya dauki mug din Ya soma kurbar coffee
"My son, tayaya zaka 6oye min damuwarka, bayan ni mahaifiyarka ce, ta ido kadai ina gane damuwarka, tun lokacin da ka shigo ƙasar nan na lura da damuwa aranka"
Sauke mug din yai kan table kafin ya dubi hajiya turai"nagode da kulawarki agare ni, amma ki kwantar da hankalin ki ba abun da ke damuna"
Gyaɗa kai tay"haka nakeson ji" ta faɗa ne ba dan ta yadda da maganarsa ba tasan baya son taji ne
"Bari na shiga ciki, ka kula min da kanka" amsa mata yai da toh
Bayan tafiyarta ajiyar zuciya ya sauke, bawai baya son fada mata bane yafi son ya fara jin halin da take a ciki in har ta isa gida lafiya, kuma iyayen ta sun kar6eta ba abun da zai hana shi sanar da nashi iyayen labarin ta.
Ƙarfe goma da rabi, jazz da sir mubarak suka dawo gidan lokacin da suka shigo falon tuni Zaki Ya koma room dinsa ba su taras da shi ba,
Hajiya turai na kwance kan gado tajiyo sautin sallamar sa, jikinta har rawa yakeyin wurin saukowa daga kan gadon da sauri ta nufe shi yana atsaye cikin shiga ta kakinsa
"Sannu da dawowa, tun dazu nake ta jiranka nayi kewarka yau kayi dare " cikin nuna kulawa tayi maganar tare da ruko hannunsa suka shiga dakin
"I'm sorry bansanar da ke zan kai dare ba, wani aiki ne mai muhimman ci Ya ruƙe ni" ya faɗa Yana kallon cikin idonta,
"Ba nace ki daina jirana ba? daga kinga nayi dare to ki kwanta kiyi bacci"
Maƙe masa kafaɗa tayi"kai ma kasan bazan iya jurewa ba...." murmushi ya ɗan saki"kinsan me na tuna"? Girgiza mashi kai tay alamar a'a"
"Waɗannan twins din na wurin Owais, ko da yake yace min ba twins bane, ɗaya ta girmi ɗaya" da mamaki hajiya turai tace"ikon Allah, amma nayi mamakin jin hakan komai nasu fa iri ɗaya kamanninsu sun 6ace"
"Zai iya yiwuwa yan gida ɗayane" jinjina kai tay alamar eh
"Yaran sun kwanta min araina, kinsan ni da son ƴa'ƴa mata, duk family dinmu ni kadai ne nake da ya'ya maza ina alfahari da hakan amma inason ya'ya mata, ga hateem nan shi mazan yake so Allah bai bashi ba"
shiru mom turai tayi kamar ta dan shiga damuwa, sam bai lura da halin da ta shiga ba, ya nufi toilet Ya shige jin ƙarar rufe kofar shi Yasa jiki asanyaye ta koma gefen gadonsu ta zauna idanunta sun ciko tab da kwalla..
Ceilling ta ƙurawa ido tana tunano wani abu da ya ta6a faruwa acan lokacin baya shakeru da suka gabata, ta ta6a haihuwa ya'yan suna mutuwa wanda silar hakan Yaja har sir mubarak Ya hanata haihuwar gaba ɗaya gudun kada itama tarasa ranta kamar yadda ya'yan da take haihuwa suke rasa ransu da zarar sun dira a duniya, Allah kadai yasan halin da ta shiga awannan lokacin saboda ta kwallafa rai akan son taga ta haihu da sir mubarak sai dai Allah bai bata ba shiyasa har su hajiya saratu suke yimata gorin sai dai taci ta kasayar
Yunkurawa tayi jiki ba kwari ta mike ta futo daga ɗakin nasu ta nufi bedroom din jazz sai da ta matse kwallar da ta taru a idanunta kafin tayi mashi sallama shiru ba'a amsa mata ba, har ta fara tunanin ko yayi bacci ne, shigarta ke da wuya kwatsam taci karo da wayarsa dake yashe kan floor ga dukkan alamu wurgo da ita yayi, hatta lap coat dinsa anan ya jefar da ita, hankalin ta ba karamin tashi yayi ba, a razane ta kalli gadonsa a zaune ta same shi tsakiyar mattress, Ya kifa kansa bisa gwiwowin sa, lokaci ɗaya ta rasa sukuninta da sauri ta nufi kayan nashi ta kwashe su ta je ta ajiye masa kafin ta dauko wayar ta nufin gadon nashi ta hau sama ta zauna tana fuskantar shi
"Jazz meke faruwa dakai ne"? ta fada fuskanta dauke da matsananciyar damuwa
Shiru babu alamun zai tanka mata
"Nasan kana ji na jazz, ka ɗago ka kalle ni sannan ka fadamin meke damunka" A hankali Ya ɗago da fuskarsa wadda ta jiƙe sharkaf da hawaye idanunsa sun kaɗa jawur, wani irin bugu taji zuciyarta tai muryarta na rawa ta furta"jazz kuka kake? Meke damunka ne? Ko bakada lafiya ne? Aruɗe ta fada tana shafa fuskarsa
"Jazz dan Allah ka fadamin ko hankalina Ya kwanta" daƙyar Ya iya motsa la66ansa Ya furta sunan faryat, lokacin ɗaya annurin fuskar hajiya turai Ya ɗauke ɗuff, saboda ta fahimci silar shigarshi halin da yake aciki, batasan ya zatai da jazz ba, tayi fama da shi akan ya rabu da faryat amma yaƙiya saboda tasan bazata ta6a auran shi ba, hasalima ma yarinyar bata kwanta mata aranta ba, saboda fitsararta da rashin kunyarta..
"Jazz yaushe ne zaka daina yaudarar kanka akan yarinyar nan? sau nawa ina maka gargadi akan ka fita sabgarta? Na fada maka ba sonka takeyi ba yakamata ka hakura ka nemi wata ay ba ita kadai bace mace a duniya....." kafin ta ƙare maganar ya tarin numfashin ta da cewa"bazan iyaba mommy, Allah ne ya jarabce ni da sonta, wallahi nayi kokarin cireta araina amma na kasa ki tayani da addu'a Allah ya yaye min sonta in ba haka ba zatai silar da zan rasa raina..."
har saida gaban turai Ya fadi jin abun da yace, ta fahimci mahaukacin son da yakema faryat ba lallai Ya fahimce ta ba
"Me tayi maka ne"? labari Ya fara bata na abun da Ya faru tsakaninsu lokacin da ya je wurinta bai 6oye mata komai ba, har nemansa da tayi don ya bata hadin kai,
"Mom kullum na kirata sai ta ci mutuncina, tace wai ni ba namiji bane tunda bazan iya biya mata bukatarta ba, sannan bazata ta6a auran mara asali dan tsohuwar mai aikin gidan su ba...." ya faɗa idanunsa cike tab da kwalla
Ita kanta hajiya turai hawayen ne ke sintiri kan kuncinta, ta tsani taji ana yi mashi gorin asali kamar kanshi farau, ta rasa gane meke damun wasu mutanan sun manta cewa bawa bashi ke daurawa kansa ba? Allah ne Yake kaddara masa rayuwarsa?
"Jazz ta yi kuskure A kalamanta, wallahi sai tayi danasani, saboda ka fi karfinta nesa ba kusa ba, kuma kaine cikakken mai asali tunda kana jin tsoron Allah kuma ka tsare mutuncinka, ni in banda kaddarar so ina kai ina Faryat"? ta faɗa ranta amatuƙar 6ace
"Tafi ni komai tun da tana da asali"
"Kaima kana da asali jazz" da sauri Ya kalle ta
"Mom bangane me kike nufi ba, ke da kanki kika fada min baki da kowa a danginki mahaifina Ya rasu" girgiza kai tayi"na fada maka hakanne saboda ka fidda rai da kowa nawa, bana son maganar jazz ka cigaba da hakuri in sha Allah komai ya kusa zuwa karshe" tun da tafara magana jazz Yake kallonta har yau ya rasa gane dalilin dayasa bata son tayi maganar abun da Ya shafi danginsa, shi dama yasan dole tana da family dinta akwai dai wani abin da take 6oye masa, duk da yana neman ƙarin bayani daga gareta sai dai ya hakura yabarwa zuciyarsa zai cigaba da hakuri kamar yadda ta ce har zuwa lokacin da zata sanar da shi komai....
Shiru sukayi na wani lokaci babu mai magana a cikin su,
"Ina ibad"? ya tambaya yana kallon ta
"Tun bayan sallar Isha' Yai bacci, ya yi jiran dawowarka har fadamin yai ya kira layinka bakai picking ba"
murmushi yayi"Allah sarki ɗan uwana, dama nasan dole ya neme ni, na sanya wayar a silent ne saboda aiki da nakeyi"