← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 143 OF 238

Sashe 143

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon juna su ka yi arude suka maimaita sunan Headquarter, Sajeed Yace"me za mu yi acan ɗin"? Da alama sun ruɗe, murmushi Salsabeel yayi kafin yace"zaku gana da manyan jami'an Isod" Hankali tashe Unaisah tace"mu ɗin"? Jinjina mata kai yayi"kwarai kuwa, Lokaci yayi da zasu gana da ku, don suji daga bakin ku, Suna bukatar bayani game da rayuwarku a gidan kurkukun ƙaddara, zasuyi maku tambayoyi da suka shafi rayuwar da kukai agidan kurkukun ƙaddara da kuma shi kanshi gidan kurkukun"

 Ya fada yana duban fuskokin su sunyi shiru suna sauraronshi kowa da abunda yaƙe sakawa aranshi.

"Nazo ne don in ƙarfafa maku gwiwa, nasan akwai masu jin tsoro har yanzu acikin ku, to inaso ku aje tsoron nan gefe ɗaya da duk wani shakku da zakuji, yanzu lokaci ne da zaku bada gudummuwa ku taimaka masu gurin kawo karshen kurkukun kaddara, bayanan da zaku basu da su zasuyi amfani wurin yin binciken waɗanda suka azabtar da rayuwar ku, kada ku 6oye masu komai, duk mun ƙanƙantar abu da kuka sani ku faɗa masu zai iya zama mai amfani agare su" 

tun da salsabeel ya fara magana Danish Ya rufe idanunshi gam kamar baya atare da su, sarai salsabeel Ya lura da yanayin shi.

"Ku faɗa masu irin kuncin rayuwar da kukayi, Ku faɗamasu azabtarwar da sukayi maku da kuma wulakanta rayuwarku da su ka yi, ku kaɗai kuka san meya faru arayuwarku, tunkafin ku mallaki hankalinku kuke a kulle ba shige ba fuce, idan har kuka 6oye wani abu baku fada ma su ba, kanku zaku cuta, kwara ku tona masu asiri don uban su kowa yasan me suke aikatawa" ya faɗa tare da bugun sofa din da yake zaune akai da hannun shi.

"ku daina ganin ayanzu kun tsira kun samu rayuwar ƴanci wallahi har yanzu rayuwar ku tana acikin haɗari saboda ba zasu ƙyale ku ba, suna nan suna bibiyar rayuwarku don su salwantar daku saboda kune prisoners na farko da suka fara karya dokar kurkukun kaddara, tayaya ku ke tunanin zasu ƙyale ku? Ay ko dan kada ku tona masu asiri dole su nemi hanyar da zasu shafe babin ku"

 Maganar salsabeel ta ɗaga hankulansu, Tuni ido ya raina fata, wasu daga cikinsu har sun fara sharar kwalla,

ya faɗa masu hakanne don Ya tsoratar da su ya kuma tunzura su don su fusata su samu kwarin giwar tona masu asiri idan jami'an sirrin suka tambaye su.

"Ko ba don saboda ku ba, Ku tuna ƴan uwanku da kuka bari agidan kurkukun ƙaddara! Waɗanda basu ji ba basu gani ba kamar ku dai, suna can ana azabtar da rayuwarsu, Sun maida su kamar dabbobi sai azabtar da su sukeyi, meye ribarku idan ku kun samu jin dadin rayuwa su kuma suna awahala? Baku da burin ku dauki fansar abunda akayi maku? Sannan ku cecei rayuwar yan uwanku? Za ku ja baki ne kuyi shiru acigaba da salwantar da rayuwar kananun yara da basu ji ba basu gani ba"? Ranshi a6ace yayi maganar yana kallon su, Jiki asanyaye sajeed Ya sauko daga kan sofa, Ya dawo ƙasa ya zauna hannayen shi biyu tallabe da kan shi, Idanunshi sun ciko tab da kwalla.

Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko  Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
Shesshekar kukan su ne Ya cika falon, kalaman salsabeel sun fama raunin dake acikin zuciyar su..." 

Salsabeel bai dakata ba saida ya tabbatar sun fusata sun harzuka kafin ya tsagaita da yin maganar Yana jiran jin me zasu ce.

Cikin shesshekar kuka sajeed yace"wallahi ko ba ka fada mana ba, ba zamu raga masu ba, ni ashirya nake da duk wata tambaya da za'ayi min, nayi alkawarin zan fadi iya abunda nasani saboda nima twin sister dina tana can, bana so su kashe min yar uwata duk da bani da tabbacin tana araye kota mutu...." kuka ne Yaci karfinshi, Ya kifa kanshi saman  sofa.

Wani irin tausayin su ne Ya kama Ummi, Tuni taji hawaye sun cika idanunta, lamarin rayuwar yaran tana matuƙar tada mata hankali, har yau tana jin labarin su tamkar a mafarki saboda abun yafi karfin tunaninta.

Fashewa jemimah tayi da kuka tana fadin

"nima wlh saina tona masu asiri, mugaye azzalumai kawai, hadama wannan tsohuwar data kusa kashe mu nida su Azeeza, Inaji ina gani majnoon dina ya mutu, wlh saina daukar mashi fansa, koda zan rasa raina ne..." rai a6ace tay maganar, idanunta sunyi jawur ga ruwan hawaye dake zarya kan kuncin ta,

dafe kai Deeja tayi da hannunta tamkar zata fasa masu ihu, idanunta sun rune zuwa ja, kwata kwata bata son jin maganganun da su ke yi,

miƙewa tayi da sauri ta fuce daga falon, duk suka bi bayanta da kallo babu wanda yayi yunkurin dakatar da ita.

"Bazan ta6a manta irin azabtarwar da sukayi mana ba, wallahi rantsuwar ɗan musulmi ba gudu ba ja da baya sai mun fallasa su kwara duniya tasan me suke aikatawa, ay yaya Salsabeel ba sai ka sha wahalar yi mana bayani ba, dama mu lokaci kawai muke jira in ma takama har prison din aje damu ayi faɗan da mu, wallahi zamu bada goyan baya ɗari bisa ɗari ko da silar hakan zai ja mu rasa ran mu wlh sai inda karfin mu Ya ƙare, Kome suke son ji zamu faɗa masu...." 

tun da Unaisah ta fara zazzaga masifa, suke kallonta jikinta har jijjiga ya ke yi tsabar fusata da 6acin rai, an ta6o inda keyi mata ƙaiƙayi.." bata ƙare maganar ba, Danish Ya miƙe daga zaunan da yake kan Sofa, gaba ɗaya suka bi shi da kallo Salsabeel Yace"Danish Ina zakaje ban gama magana ba"? Ko kallo bai ishe shi ba,  Ya fuce daga falon, sam unaisah takasa karasa maganar,

Da tsantsar mamaki suka bi bayan shi da kallo har ya 6ace ma ganin su.

Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko  Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.

Haris Yace"ka gani ko ya salsabeel? Danish Ya canza kamar bashi ba, Yanzu ji muna magana mai mahimmanci Ya tashi Ya tafi kamar abun bai shafe shi ba, haka muke fama da shi baya son shiga cikin mu kuma baya son muje gurin shi..." cikin jin kunar rai Haris yayi maganar yana kallon Salsabeel.

Korafe korafe suka dinga fada mashi akan danish,

Unaisah tace"nasan ma zai yi wuya ya bamu hadin kai, kuma yafi mu sanin komai dangane da gidan kurkukun ƙaddara"

 a marairaice tay maganar,

Shiru salsabeel yayi jim yana ɗan jinjina kan shi kafin cikin sanyin murya yace"sai kun yi hakuri da shi, saboda ba yin kan shi bane,  sau dayawa wasu abubuwan da za ku ga yanayi wallahi ba shi bane"! A matuƙar ruɗe suka kalli Salsabeel, Musamman Unaisah Maganarsa Ta jefata a ruɗani, Har dai tagaza jure tace"Ya salsabeel ban fahimci me kake nufi ba! Naji kace wani lokaci ba shi bane"! Kallon ta salsabeel yayi"ina nufin wani abun da ya ke yi bayin kan shi bane, shaidanun  dake a jikin shi ne, su ne suke Controlling din shi, zai iya wuni ba acikin hayyacin shi ba, nasan baku taba lura da hakan ba, shiyasa baya son shiga cikin ku, kuma baya son wani yaje gurin shi, idan ba wanda yake son gani ba, amma abun da yakamata ku cigaba da taya shi addu'a, In sha Allah idan mukayi nasarar raba shi da evils din jikin shi, zaku sha mamaki, zai dawo ainihin wanene shi...."

"Yaya salsabeel amma dai bazai manta damu ba ko"? Batool ce tay mashi maganar,

"Taya zai manta daku? Abokan kuruciyar shi, sai dai wasu abubuwan da yake yi zai daina su, zai canza sosai fiye da yadda baku ta6a zata ba.."

 Hankalin Unaisah Ya tashi ba kaɗan ba, Aranta ta ayyana idan har maganar Salsabeel ta tabbata tabbas akwai damuwa ba kadan ba, sai dai ta hana zuciyarta gasgata maganar shi.

Buɗe trolley din gaban shi yayi duk suka kura ido
[14/10, 6:06 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite

Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe page 45 Complete by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
September 06, 2024
Sponsored Link

Takun Ƙarshe
Zama ya yi daga gefen gadon tare da kallonta Ya kashe mata ido ɗaya ya ɗage gira cike da izza yace"me kike tunani ne? Kinyi mamakin ganina ne"? Shiru tayi bata tanka mashi ba, saboda ita har yanzu bata yarda cewa dagaske shine take gani ba, kokwanto take anya bata samu ta6in hankali ba

Sarai ya fahimci Halin da take aciki, Ko ajikin shi, saima kwantar da kanshi da yai saman pillow

"Ummi!, Haƙuri na ya ƙare, bazan iya jurewa ba, sha'awar son kasance wa dake tana neman tayi min illa, kin san ke kadai ce macen da ke iya gamsar dani, shiyasa na tako da kaina nazo don in kar6i hakkina agurin ki!" ya faɗa yana bin ta da wani shu'umin kallo

"Tun zuwan karshe da ki kai gidana ban ƙara ganin ki ba, in har ba zaki dinga zuwa kina bani hakkina ba, toh ni zan dinga zuwa ina kar6a, kin riga da kin san wanene ni indai akan bukatar kaina ne bana ji bana gani"

gaba ɗaya ta ruɗe, La66anta na kerma ta furta"dagaske kai nake gani? Ɗaga mata gira yai.

"Tayaya akai ka shigo gidan nan"?

"Kin san bana son tambaya, Last time, I warned you to stop asking me questions. If you believe me, babu bukatar ki tuhumeni akan duk wani abu da zan yi"

dafe kai tayi da hannu ɗaya, lamarin shi ya fara bata tsoro ba kaɗan ba.

"I'm waiting for you, come and satisfy me." ya faɗa yana shafa sajen fuskar shi.

Girgiza kai ta yi"kayi hakuri bazan iya ba, ina jin fargaban wani yagan mu zan iya samun matsala, ko kamanta a gidan wa muke? Ta faɗa atsorace tana kallon shi.

A gadarance ya furta"gidan director general of Isod, Sai me"? Idan naga dama har gidan ubansa sai in shiga inyi abun da naga dama, bawai iya gidan sa ba, ina da ƙarfin ikon yin hakan"
Chapter 143 · 0% Book details