← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 238

Sashe 73

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Shureim zata bata maku lokaci, Ku tafi ku kyaleta, dama daddynta dakyar ya amince ta biku," yana murmushi yace"toh mommy mu zamu wuce" atare suka hada baki wurin firta"Allah yakaiku lafiya, ku gaida mutanan gidan"

"Zasuji in sha Allah"

Har sun kusa fita falon hajiya layla ta ce"idan kun isa gidan Benazir ki kirani awaya inason yin magana da aneelerh" amsa mata tayi da toh kafin suka fuce, su zeenatu sai rawar kai akeyi za'aje unguwa...

Abakin motar Dr shureim suka tsaya benazir ta fara daukar su hotuna da wayarta har kusan kala takwas bayan sunyi atare tayima zeenatu tare da dr shureim kafin taba zeenatu wayar tayi mata ita kadai sai kuma tayi atare da shureim......

Shiga motar sukai, Dr shureim yana a driver's seat zeenatu na zaune gefensa, benazir kadai suka bari a backseat.

"yau ni za'a nunawa wariyar, wato zeenatu ce ta gaban mota, ni kuma ta baya babu komai nima idan mijina ya dawo zan koma ta gaban motarsa ne" dariya sukayi gaba dayansu,

Bayan yai wa motar key ya fara driving a hankali Ya nufi gate din gidan babu wanda ya dakatar da su saboda an basu umarnin su barsu su fita.

Bayan motarsu ta haura kan titi kowa Ya nutsu, zeenatu sai satar kallon benazir takeyi ta mirror din motar har gwalo take mata saboda ansanyata agaban mota

Murmushi benazir tayi tare da ɗan girgiza kanta aranta ta ayyana bayan sangarta hada ƙuruciya ke damun ki

"Aunty benazir masu number din nan ba su ƙara kiran layin ba"?

"Namanta ban fada maki ba, me layin ta kirani awaya, yarinya ce kamar ki, ashe ta sanya wrong number ne, ko jiya na kirata awaya mun gaisa saboda ta kwanta min araina"

*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*

Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS
ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer
Privacy Policy
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 25 Complete
by
Novels Elite Admin
July 05, 2024
Sponsored Link

Novels Elite English Gyaran Nono
"Nima tunkafin naji muryarta har naji ta kwanta min araina, idan muka dawo gida ki kira min ita mu gaisa pls" a ƙagare tay maganar

"Kamar kinsani, farko da muka fara waya da ita sai da tace min idan ina da ƙanwa kamarta in haɗata da ita, kinga shikenan sai ku ƙulla ƙawance" wani irin daɗi ne Ya lullu6e Zeenatu har ta fara imagining haɗuwarta da yarinyar tunkafin ma su fara magana a waya abunka ga me son ƙawaye,

Gaba ɗaya firar da suke Yi akan kunnan Dr shureim, wanda Hankalinsa ke akan driving din da Yake yi,

Basu sha wahalar gane gidan ba, ta hanyar amfani da address da Aneelerh ta basu har bakin gate din gidan suka iso, da sauri mai gadin gidan Ya buɗe masu gate motar su ta kunna kai ciki,

Tunkafin Dr shureim Yayi parking Aneelerh ta fito da sauri ta nufi motar su tsabar son takai garesu har tuntube takusa yi, kafin ta ƙaraso Benazir tai saurin fitowa da gudun gaske ta nufi Aneelerh suka rungume juna kamar za su koma mutun ɗaya,

Fuskar Dr shureim ɗauke da murmushi ya fito tare da zagayawa other side ɗin motar Ya buɗe ma Zeenatu, fitowa tay daga ciki ta soma bin ko'ina na gidan da kallo kafin ta sauke idanunta kan su Benazir dake a rungume da juna,

"Yaya Shureim wannan itace ƙawar Aunty Benazir ɗin?"

ɗaga mata kai yai alamar eh,

Tsawon mintuna kafin suka raba jikin su daga na juna, fuskokin su sharkaf da hawaye saboda kukan da suka sha,

Cikin shesshekar kuka Benazir tace"A.. Aneelerh! Ashe da rabon zamu ƙara ganawa da junan mu?

Itama Aneelern da muryar kuka tace "Benazir kinga yadda kika koma? Nayi maraicin ganinki, nayi kewarki aminiyata sosae, wlh bakiji dadin da nake ji ba..." daƙyar suke magana saboda kukan da suke yi har lokacin,

Zeenatu sarkin tausayi har ta fara matsar ƙwalla, shi kanshi Dr shureim dauriya ce kawai Yake Yi, amma ba ƙaramin tausayi suka bashi ba, bazai ta6a manta shaƙuwar da ke atsakaninsu ba,

Fitowa Zahra tayi daga gidan karaf idanunta suka sauka akan su Dr shureim da Zeenatu Har saida taji gabanta Ya faɗi ganin irin kyawun mutumin da kamalarsa daƙyar ta janye idanunta daga kansu ta mayar da dubanta ga su Aneelerh,

Murmushi Zarah ta saki saboda taji daɗin ganin aminnan atare,

"Ki daina kuka bana son ganin hawayen ki," Aneelerh ce tai maganar idanunta jawur Benazir tace "Idan kinaso In daina kema ki daina, taya bazanyi kuka ba Aneelerh? Nayi babban rashin da har abada bazan Iya ta6a yafewa kaina ba, laifina ne gani nake kamar nice silar da zumuncinmu ya tarwatse..." da sauri Aneelerh ta sanya hannu ta toshe mata bakinta "ki daina ɗaurawa kanki laifi, saboda bayin kanki bane tafiyar da kikai, kema bada son ranki aka raba ki da danginki damu kanmu ba...." lallashinta taci gaba da yi Zeenatu har ta fara gajiya da tsayuwa dama ita bata saba da wahala ba,

Tana faman jan ajiyar zuciya ta juya ta dubi su Shureim cikin sanyin murya tace"Aneelerh ga Yaya Shureim da Zeenatu ɗiyar Uncle ɗina" da sauri Aneelerh ta nufe su fuskarta da fara'a ta gaishe da Yaya shureim "sannunku da zuwa Yaya shureim ku shigo daga ciki" tay maganar tare da hugging ɗin Zeenatu tace "Yan mata sannunki kuyi haƙuri mun barku atsaye"

Kamar bata son haɗa ido da shureim saboda girman shi da take gani, tun fil azal tana matuƙar jin nauyinshi kuma tana girmama shi,

"Yawwa anaeelerh mun same ku lafiya",

"Lafiyalou Yayanmu" tay maganar tare da ruƙo hannun Zeenatu suka yi gaba Shureim Yabi bayansu tare da Benazir da sauri Zahra ta koma falo tana jiran su shigo don su gaisa,

Lokacin da suka shigo falon Mami da Ummi suna atsaye suna jiran shigowarsu don su tarbesu, koda Benazir tayi arba da Mami wani irin nauyinta da kunyarta ne suka kamata, Mami kuwa fara'a tasaki da sauri ta janyo Benazir ta rungumeta tana ɗan bubbuga bayanta "marhabun lale ƴata, tsawon lokaci munyi kewar rashin ki" lokaci ɗaya Benazir taji hawaye sun sake wanke mata fuska

Muryarta da shessheka ta furta"Ma..mi " sam takasa ƙarasa maganar,

"na fahimce ki basai kinyi min bayani ba, Aneelerh ta sanar dani komai, ki kwantar da hankalinki ba kuka yakamata kiyi ba, godiya yakamata mu yiwa Allah daya dawo mana dake cikin ƙoshin lafiya" Mamin ta faɗa tare da raba jikinsu ta sa tafin hannunta tana share mata hawaye

Kafin ta ɗago ta dubi Dr shureim wanda tun da ya shigo ya sunnar da kanshi ƙasa saboda nauyin Mami da yaji gani yake kamar har yanzu tabon da yai ma kansa zaisa su guje shi,

Daƙyar ya motsa labbansa zai gaishe da ita Mami tayi saurin katseshi da cewa "Allah sarki Shureim kaine ka koma haka? Gaba ɗaya kun canzamin, Shureim Ka yada zumunci ƙiri ƙiri Ka guje mu ka koma Egypt ban ta6a zaton zakai mana haka ba"

Cikin sanyin murya yace"Mami ay min afuwa nima bada son raina ba nayi nesa daku, zaman ƙasar ne Ya gagareni saboda abun da Ya faru, amma wallahi ko bayan da na tafi kuna araina..." bai ƙare maganar ba Mami ta katse shi da cewa "bakomai Shureim, duk abun da Ya faru mukaddari ne daga Allah, bawa bai isa Ya guje ma ƙaddararsa ba, naji dadin ganin ku cikin koshin lafiya sosae..."

"Ku mu zauna" ta faɗa tare da nuna masu sofas, Bayan kowa Ya zauna Ummi da Zahra suka yi masu barka da zuwa

"Muyiwa Annabi salati" acewar Mami gaba ɗaya suka yi atare kafin daga bisani Mami ta dubi Zeenatu dake ta faman zare blue eyes ɗinta, gaba daya tarasa sukuni saboda bata saba shiga mutane ba kamar tana jin tsoron su,

"Tabarakallahu ahsanul khaliqin, Ƴata wacece wannan bakuyi min bayani ba, gata dai masha Allah daga gani ba jinsin ƙasar mu bane" murmushi Zeenatu tayi,

Ummi tace"kin riga ni faɗa, tun da suka shigo ta tsole min ido, kamar in sace ta" dariya sukai cikin raha,

"Sunanta Zeenatu, ɗiyar Uncle ɗina ce" waro idanu Mami tayi haɗi da jinjina kai,

"Masha Allah, sannu Zeenatu" amsa mata tay da "yawwa"

"Dan Allah ki saki jikinki, ki ɗauka kamar kina agidanku ne, don na fahimci kamar kin takura"

Murmushi Zeenatu tayi har dimples dinta suka lotsa,

"Ina su Maminku ina fata duk suna lafiya" cikin kulawa tayi Maganar tana kallon benazir"

"Suna nan lafiya, sunce mu gaishe daku, taso mu zo tare amma tace sai zuwa na gaba",

Murmushi Mami tayi "Allah Ya kawo ta Lafiya in ma batazo ba ni na fidda lokaci inje gidan naku"

Shiru sukayi na wani lokaci, kowa da abunda Yake saƙawa aranshi, Benazir ta ƙosa su ke6e da Aneelerh don su ƙara jajantama junansu.
Chapter 73 · 0% Book details