← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 182 OF 238

Sashe 182

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wani ƙasƙantaccen Kallo Ya wurga mata mai tattare da ƙyama, cike da ƙwarin gwiwa ya furta, "Na dawo, amma ba a matsayin Garkuwarku ba, a matsayin garkuwar fursinoni." jikinta na kerma kamar mazari kafin ta furta wani abu ta jiyo sautin takalmansu ɗaya bayan ɗaya suke shigowa cikin Hall ɗin, ba zaka ta6a gane ba giants din kurkuku bane saboda kayan jikinsu sak irin Na giants ne.

Ɗaya bayan ɗaya suka soma cire mask din fuskarsu, waro idanu waje tsohuwa Inno tayi Ganin baƙin Fuskoki a gidan Kurkukun Ƙaddara.

Kallo ɗaya Chief Owais ya yi ma Prisoners din dake a gurin ya yi saurin kawar da idanun shi, Haka shima Big guy kasa jurewa yayi ganin babu sutura a jikin su, Taj da zuciyarshi ta gama karaya da tausayinsu ji yayi kamar ya fashe da kuka, a ranshi ya ayyana wai anan yarsa Angel tayi rayuwa har na tsawon shekaru, Ya salam!!!.

Salsabeel kuwa tun shigowarshi idanun shi na akan Inno wani irin kallo mai cike da tsana yake jefa mata....

"Su wanene ku!.." bata ƙare maganar ba, sakamakon wani zazzafan Mari da Chief Owais Ya kwasa mata har saida wuyanta ya nemi jirkicewa, Kafin ta ɗago Ya daddage ya sakar mata mahangulba kan mummuƙenta...gaba ɗaya ta kife ƙasa a susuce ta furta,"kai, kai, kai, kai....."

Prisoners din dake a gurin gaba ɗaya sun ruɗe sun rasa gane su wanene wadannan baƙuwar fuskar? shin sun zo ne da niyyar taimakonsu? ko kuwa suma mugaye ne..?

"Kai ku maida Kayan ku" Big guy ne ya faɗa ba tare da ya kai idonshi kan su ba, jikinsu na kerma suka ɗauki uniforms dinsu dake yashe kasa suka shiga zirasu a jikin su.

Ƙululun baƙin ciki ne Ya tokare makoshin tsohuwa inno, tun da take wani ɗan adam bai ta6a gigin ta6ata ba da sunan bugu sai yau da Allah Ya haɗata da Chief, yunƙurawa tayi ta miƙe tana layi ta soma rarraba idanunta akan Salsabeel da Danish.

Tana huci ta ce, "Maciya amana! saina tona maku asiri gurin Elders"

Ta faɗa tana kokarin Yin sihiri don ta 6ace sai dai wani iko na Allah kamar an ɗauke mata sihirinta, A ruɗe take kallon hannayenta ganin sun ƙi tasiri.

"Kina mamaki ne?" Danish ne ya faɗa tare da ɗaga mata gira, takaici ya ishe ta..

"Wai dama haka matsafan suke, munana, gasu ƙazamai, gwanin ban ƙyama." Fuska a yamutse Big Guy ya faɗa tare da watsa mata yawu kan fuskarta ya ce, "Daƙiƙiya, dama karfin naki na sihiri ne, yanzu da babu shi taya zaki faɗa ma Elders dangane da zuwan mu? Bayan mun riga da mun mamaye gidan kurkukun da dakarun sojojinmu, munyi basaja mun saje da Giants ɗinku, Yanzu haka ɗaya bayan daya sojojinmu suke bi suna yi masu kisan mummuke batare da sanin ku ba."

Dafe kai tsohuwa inno tayi da hannayenta ta fara jijjiga jikinta tana kokarin ta rikiɗa nan ma dai abun ya ci tura.

Batai aune ba Sai dai taji safkar wuƙa a makoshinta, Big guy ne ya farke ta har saida ya dire ƙasa, Jini ya dinga tartsatsi kamar pipe din ruwa ya fashe, gaba ɗaya gangar jikinta ta zube ƙasa tana bullayi ta dinga sakin wata irin kururuwar azaba har rai ya yi halin sa....

"Har yanzu nagaza yarda da abunda idanuna suke nuna min! Ina jin abun kamar a mafarki ashe dagaske komai ke faruwa!" cikin jin ƙunar rai Chief Ya faɗa kafin Ya dubi Sojojin dake a bayansu ya ce, "Ku tafi da yaran!" Cike da bada Umarni Chief Ya faɗa.

Kuka suka fara Yi masu jikinsu sai kakarwa yake yi, sun yi zaton cutar da su zasu yi, fahimtar hakan yasa Taj yi masu bayani ya ce sun zo ne don su taimakesu su ba masu cutarwa bane.

Waro idanu waje suka yi, wlh alƙalamina bazai Iya mistalta irin yadda suka yi mamaki da al'ajabin jin za'a taimaki rayuwarsu ba, batare da 6ata lokaci ba, huɗu daga cikin Isod soldiers dinsu suka tafi da yaran..

Duk wannan abun dake faruwa Babu wanda Ya san da zuwan su cikin kurkukun, sai mutun ɗaya wato tsohuwa Khala.

Saboda sautin bugun gangunan da makaɗa suke yi Ya hana Matsafan su jiyo sautin abun da ke faruwa..

Ajiyar zuciya suka sauke batare da jin fargaba ba, suka fito daga Hall din cikin tafiyar sanɗa suka nufi wata doguwar hanya mai kwana-kwana..

Duk Giant din da ya ankara dasu kafin yayi wani yunƙuri tuni suke fille kanshi da adda, Kisan Gilla su ke yi masu...

(SHIN TAYAYA AKAI SUKA SHIGO GIDAN KURKUKUN ƘADDARA?)

Bata nufi ko'ina ba sai hall ɗin da madubban tsafinsu suke, tana shiga ta iske giants din dake kan duty, tasan muddin Su garkuwa suka ƙaraso sune na farko da zasu fara kawo masu cikas saboda suna kallon komai dake wakana a cikin kurkukun ƙaddara da kuma dajin evil forest, gyaran murya tayi masu, cikin girmamawa suka gaishe da ita, tace meya hanasu shiga filin taro? Bayan yau rana ce mai mahimmanci da buƙatar kowa dake a kurkukun ya halacci wurin shagalin, Giants din su ka bata amsa da ba'a basu umarnin subar aikin su ba, tsohuwa khala tace a matsayinta na matar Elder tana mai umartarsu da su aje aikinsu, suje suma ayi shagalin da su, ba suyi mata musu ba, saboda sun san wacece ita, kuma Elder ya gargaɗesu akan suyi mata biyayya sau da ƙafa, in har ta buƙaci wani abu kada suyi mata jayayya su dauka kamar shi ne ya basu umarni, tuna wannan yasa Giants din suka bar bakin aikin nasu.

Murmushi Tsohuwa khala tayi, tana ganin fitarsu, ta bi madubban tsafin ɗaya bayan daya ta jefar da su gaba ɗaya suka faffashe.

Fitowa tayi daga hall din tana cikin tafiya cike da fargaba, kwatsam ta hango wasu gungun matsafa a cikin baƙinsu kusan su takwas sun nufo wurin kamar dai suna ƙarewa ginin kallo ne, gyaran murya ta yi masu da sauri suka dubeta, fuskarta da fara'a ta nufe su bayan sun gaisa ta gabatar masu da kanta a matsayin Matar Elder, sai faman washe baki suke yi suna ƙara gaishe da ita tace masu in ba damuwa su biyota zata nuna masu wasu bangarori na kurkukun tasan zasu so su gani.
Basu kawo komai a ransu ba, suka bi bayanta ta nufi wani ɗaki da su, suna shiga ta datse ƙofar a ruɗe suka kalle ta ganin ta rufe ƙofa, kamar sun fara zargin wani abu, sai dai kafin su gano hakan Tsohuwa Khala ta yi hanzarin zare ƙaramar wuƙarta gaba ɗaya ta kashesu, ta zuƙunna ta cire kayan dake a jikinsu dama shine abun da take so..

6acewa tayi, bata dira a ko'ina ba sai a cikin ɗakinta, ta jefar da kayan saman gadonta kafin ta kuma 6acewa ta bayyana a wani ke6a66an guri inda Danish ya faɗa mata ta nan zasu biyo idan suka ƙaraso.

Tana tsaye hannunta ruƙe da sandar ta, zuciyarta cike fal da zullumi, Allah Allah take su ƙaraso kamar ta fashe da kuka saboda bugun barazanar da zuciyarta ke yi mata, ta aikata 6arna ba kaɗan ba, har ta fidda rai da zuwansu zuciyarta ta fara raya mata ta kashe kanta kawai tun kafin Elders su ankara da 6arnar da tayi masu.

A lokacin da bata yi tsammani ba, ta fara jin motsi ta saman ceilling din da take, A hanzarce ta kalli silin din ta sauke idanunta kan wasu tsofaffin tagogine dake a kulle jikin shi.

Cike da sa rai take kallonsu, Unexpectedly taga Murfin windows din na motsi wlh tsabar farin ciki bata san sa'adda takai goshinta ƙasa tay sujjada domin nuna godiyarta ga Allah, tunkafin ma ta tabbatar in su ɗinne, Kafin ta ɗago daga sujjadar kunnuwanta suka jiyo mata ƙarar 6allewar murfunan tagogin, a zabure ta miƙe tana kallon kafafuwansu, ɗaya bayan ɗaya suka fara dirowa ƙasa, kamar ana jeho su.

Dariyar farin ciki ta saki duk da mask din dake akan fuskar Danish hakan bai hana ta gane shi ba, shima yana ganinta ya nufeta gaba ɗaya ta rungumeshi kamar zata maida shi cikinta, kai ƙarshe ma sai ta fashe mashi da kuka, cikin shesshekar murya ta ce,"Alhamdulillah, nagode ma Allah da ya nuna min wannan ranar da raina, har na fidda rai da zuwanku.."

Ta faɗa tare da raba jikinta daga na Danish ta dubi sauran sojojin dake atsaitsaye ga wasu dake ta durowa ƙasa.

"Khala" Salsabeel ne ya ambaci sunanta, bata gane shi ba saboda mask din da ya rufe fuskarshi, cikin sauri ya matsa kusa da ita, ta rungumeshi nan ma ta kuma fashewa da wani kukan farin ciki, Allah abun godiya..

Bayan ta raba jikinta daga na Salsabeel, Danish ya gabatar mata da Chief Owais, wanda tun da ya duro hankalinsa ke akan ginin yana mai jinjina girmansa, amma lokacin da kunnuwansa suka jiyo mashi muryar Khala da ruɗu ya tsayar da idanunsa akanta, kamar yadda take kallon shi haka shima yake kallonta, muryarta na rawa ta furta, "Owais, kaine ka girma haka?" Tayi zaton a cikin zuciya ta yi maganar, gaba ɗaya sojojin sun ɗan ruɗe da jin yadda tayi maganar kamar tasan shi, shi kanshi Chief din ya ruɗe da jin muryarta kamar yasanta, sai dai ya kasa gane wacece saboda ta rufe fuskarta da tukunkumi.

Idanunta kaɗai suke iya gani...
Bai aune ba, yaji ta cakume shi da hannayenta biyu ta rungume shi sosai fiye da yadda ta rungume su Salsabeel...Allah kaɗai yasan me take ji acikin zuciyarta..

Idanunta cike tab da kwalla, ta ɗago tare da kallon su,

"Ku kaɗai ne"? Ta faɗa ganin kamar sun gama shigowa kuma duka basu fi su hamsin ba,

Salsabeel ya ce, "Ba mu kaɗai bane, akwai sauran sojoji sama da ɗari biyar, suna akan hanyar shigowa." Ajiyar zuciya ta sauke, still idanunta akan Chief Owais, duk yasha jinin jikinshi da ganin irin kallon da tsohuwar take yi mashi,

"Ina yi maku barka da zuwa Gidan Kurkukun ƙaddara, a yanzu haka sun fara gudanar da shagalin Black Night basu san komai dake faruwa ba, saboda na toshe duk wata hanya da zasu iya ganinku ta madubin tsafin su, sannan akwai tanadi da nayi maku, ku biyo ni."
Chapter 182 · 0% Book details