Sashe 72
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Marwa! Ta fada da mamaki da sauri marwa tace"am...um..barka da safiya.." bata amsa mata gaisuwar ba, sai cewa tay"ina fata lafiya? Don banta6a ganinki a ɗakina ba..." washe baki marwa tayi muryarta da alamun rashin gaskiya ta furta"dama..um inaso zan fara aikin dinner ne da wuri to na shiga kitchen din sai naga store a kulle kuma babu makulli a bakin kofar, na tambayi abla ko ta dauka shine tace min yana a wurinki" wani kallon tuhuma hajjaty take jefa mata, abun yaso bata mamaki,
Murmushin gefen fuska tayi"hmm marwa kenan, kina abu kamar wadda ta samu cutar mantau, in ba ni ba waye dama yake ruke makullin store? da har zaki tambayi abla ina Yake bayan haka wani girkine zaki fara a yanzu? Bayan breakfast da kuka kammala ko dai baki kalli agogo bane?
Sosa ƙeya tayi"wai da afara dinner din da wuri"
Kaitsaye tace mata"a'a babu bukata, kamar yadda kuka saba haka zakuyi dole sai lokaci Ya cika, sannan pls idan kinason Yin magana dani basai kinzo dakina ba! Ki kirani da landline din kitchen kamar yadda kuka saba kirana ku sanar da ni abu"! Ko amsar marwa bata jiraba, taja kofa Ta datse
Rai a6ace marwa take kallon kofar, dakin wai har ita hajjaty zata ja ma kunne kan karta kara zuwa mata daki? Lallai buri ya yi kama da mutun da alama maganar hajiya saratu zata tabbata matarnan bata da gaskiya Allah kadai Yasan makircin da take kullawa da har batason wani Yazo dakinta, dani kike magana hajjaty saina zame maki karfen ƙafa agidan nan..." acikin ranta tafada Harta fara tafiya zata koma kitchen sai kuma ta dakata tana tariyo abunda Tajiyo adakin farkon dataje tafara yin la6e a kofar, tabbas taso tajiyo muryar hajjaty kamar tana magana da wani sai dai bata kaiga shaida hakan ba
Murmushin mugunta marwa tasaki a fili ta furta"ni da ke ne" tayi maganar tare da kama hanya tabar wurin.
Bayan komawar Hajjaty dakin, a zaune ta iske pravin yana jiran ta fuskarsa a yamutse saboda Ya tsani duk wani abu da zaija asirin shi Ya tonu
"Ta fada maki abun da ya kawo ta"? Ya jefa mata tambayar, zama tayi gefen shi kafin ta sanar da shi maganar da sukai da marwa
"Ni sai nake ga kamar leƙen asiri ta zo yi min saboda babu kwanciyar hanlali atare da ita" ta faɗa tana kallon fuskarsa
Pravin yace bana tunanin haka, just ki bar komai a hannuna idan ta ƙara yi maki wani abu da hankalinki bai kwanta da shi ba ki sanar dani" ta amsa mashi da toh
___________________________ANEELERH✍️
Yau saboda da zumudin zuwan benazir ko breakfast batay ba saboda tafi son idan benazir tazo su ci abincin a tare,
Su uku ne a kitchen suke aikin girka ma bakinsu abinci, gaba ɗaya kamshin abincin Ya cika ko'ina
"Pls ku yi sauri mu kammala ta faɗa min da wuri zasu zo, dakyar ma in basu tafo ba"
"Aunty Aneelerh wacece bakuwar tamu ne"? Ana ce ta faɗa tana kallon ta yayin da take tsaye gaban gass cooker tana aikin soye soye
"Ki bari idan tazo zaki ga wacece, nafi so na baki mamaki" cikin raha ta faɗa
"Allah ya kawo su lafiya, har nakosa na ganta"
"Ameen,"
Kallon zahra tay, gaba ɗaya hankalin ta ba akan su yake ba, tana a tsaye gaban counter, inda ta ɗaura juicer ga kayan marmari shaƙe da bowl da alama ta tafi duniyar tunani, tafi karfi mintuna biyar bata ta6uka komai ba, gaba ɗaya tunaninta na akan zayn, zuciyarta sai azalzalarta ta ke yi akan son ganinsa tayi missing dinsa.
"Zahra! Zahra!!" muryar aneelerh ce ta fargar da ita lokaci ɗaya ta sauke ajiyar zuciya tare da kallon ta
"Me kike tunanine? Naga kamar wani abu na damunki"? Murmushin yake tayi"bakomai auntyna.."
"Kedai faɗa min gaskiya ko dai damuwar rashin wayarki ne"? Da sauri tace a'a wlh ba haka bane
"To menene tun ɗazu kin ƙi motsawa, Na fa faɗa miki da wuri zasu zo watakil ma sun kamo hanya,"
"I'm sorry bari na fara Yanzu zan kammala in sha Allah kafin ma su ƙaraso mun gama komai"
Har sun kusa kammala girkin Mami ta shigo kitchen din tana fadin"wai wai irin wannan kamshi haka? Tun da ga ɗaki nake shaƙo shi, lallai Yau bakin mu zasu kwashi gyara" murmushi kowan nan su Ya saki
"Mami sannu zuwa, me kikeso na zuba maki" zahra ce tay maganar
"Ni iya juice din nan Ya ishe ni, sai dai bansan ko ummi zata bukaci wani abu ba"
Zahra tace"to mami, bari na zuba maku hada snacks"
"Yawwa zahra na, adan sanya min kankara aciki zaifi dadin sha" ta amsa mata da toh
Kallon aneelerh tayi"har su nawa ne zasu zo naji dazu kamar kince hada Yayanta shureim"
"Eh hada shi tare da ɗiyar Uncle din ta"
Mami tace masha Allah, Allah Ya kawo su lafiya, bari na koma falon kada na cika ku da surutu...." har ta kusa fita ta kuma juyowa tana fadin"zahra ina jira"
"Toh mami yanzun nan zaki ganni"
Bata jima da fita ba, zahra taje ta kai masu a falo....
_____________________________✍️
ƙarfe sha biyu daidai benazir tana atsaye gaban mirror ta kammala shiryawa cikin atampha riga da skirt sun kama jikinta, ta tsara make up akan fuskarta wani irin kyawune ya ƙara bayyana ta fito ɗas balarabiyarta, ta kashe daurin dankwali bayan ta gama ta miƙe ta dauko mayafin ta dake a ninke kan mattress ta yafa shi a kafaɗa, jujjuyawa tayi gaban mirror din kafin ta sakarma kanta murmushi kyawawan dimples dinsa suka lotsa..
"Aunty benazir yaya shureim yace in baki fito ba zamu tafi mu barki agida" ta cikin mirror ta hango zeentu da tayi maganar, kamar aljanna ta ca6a uban adon lace launin blue sky mai walwali da daukar ido, ɗan ƙaramin bakinta ta shafe shi da jan baki, ga wani daurin dankwali da akayi mata mai kama da ture kaga tsiya ta sauko da gashin ta, ziririn wuyanta yana asanye da ziririyar sarƙar diamond
A sukwane Benazir ta juyo fuska adaure ta kalle ta har saida tasha jinin jikin ta
Da ƙarfi ta furta"zeenatu? meye haka? Wannan ado sai kace zamu je gidan surukan ki?
Zazzare idanu tayi"ay ni ba su nayi ma kwalliya ba, ta yaya shureim ce amma idan baki son gani na da ita sai na canza wasu kayan in goge kwalliyar"
Yamutsa fuska benazir tayi"da dai yafi saboda baki kyau ba, ko meye na shafa powder wai ke kinga fuskarki kuwa? Kamar wata fatalwa? Kina fara dole sai kin shafa powder? So kike ki zama zabayyana ne"? shiru tayi tuni annurin fuskarta ya fara daukewa muryarta da yar shagwa6a tace"Aunty benazir ay na fada maki mommy ma tana shafa powder in zatay ma daddy kwalliya, kuma kema ay fara ce sol amma kina shafa powder...." kafin ta ƙare maganar benazir tace"naji, amma ay ban kaiki haske ba, bana son jan magana kije ki canza kaya in har kinaso mu je dake"
idanunta ne suka cicciko tab da kwalla benazir dake kallonta aranta ta ce kawai daga zan kara ki mu fita sai ki fini kyau hada wata sarƙar diamond...."
Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi bazan canza kayan ba, ay yaya shureim yace nayi mashi kyau, kuma yace duk inda zaije ƙafarsa ƙafata don haka dole aje dani aunty benazir" ranta yakai makura 6aci juyawa tayi da gudu zata fuce daga dakin cikin rashin sa'a highhills din kafarda suka turguɗe gaba daya ta tafi zata kife ƙasa cikin zafin nama dr shureim Ya ruƙota ta dawo jikinsa babu wanda yasan da zuwansa a cikin su ashe yabiyo bayan zeenatu.
Wankan shadda ne a jikin shi, zeenatu na jin dumin jikinshi ta ƙankameshi tana fada masa abun da benazir tace
Murmushi yasaki yana kallon benazir dake kallon sa
Da buɗar bakinsa sai cewa yai"ke baki gane ba? Kishi take yi dake saboda kinfi ta haɗuwa, itafa tun tana ƙarama in za'aje unguwa tafi so taga tafi kowa kyau don haka kada ki damu dabi'arta ce" jin wannan maganar yasa zeenatu fashewa da dariya har hakoranta suka bayyana.
Ta6e baki benazir tayi fuskarta da dan murmushi tace"yaya shureim yanzu abun da kai ka kyauta? Agaban zeenatu kake fadin hakan? So kake ta raina ni"?
Ɗaga mata gira yai alamar eh, jinjina kai tay"bakomai, na fahimci kafi son zeenatu akaina, soyayya ta rufe maka ido ya shureim ka rasa ma wa zaka so sai wannan ifritun sa'ar ƴar ciki na" ta fada da zolaya tana nuna zeenatu
"Ahaka nakesonta" ya fada yana murmushi, zeenatu sai dadi takeji har wani ƙara maƙala hannunta acikin nasa take
"Mu munyi gaba Ki iske mu a mota" yana ƙare maganar Yaja hannun zeenatu suka fuce, da sauri benazir ta dauko mayafi ta yafa a kafaɗa, hannun ta ruƙe da yar purse ta fito
A falo suka iske su hajiya layla suna fira kamar wani abu bai ta6a faruwa ba, Yanzu ta kwantar da hankalinta tun bayan abun da Ya faru jiya
"Zamu tafi mommy asanya mana albarkar iyaye" dr shurem ne yai maganar, atare suka dago da murmushi akan fuskokinsu
Hajiya sara tace"masha Allah, tabarakallahu ahsanul khalikin kunyi kyau kamar dollars" dariya suka sanya gaba dayansu
Fuskar hajiya layla da murmushi tace"nima naso aje unguwar nan dani amma zan bari zuwa nagaba" ta fada yayin da aranta take jin fargaban abun da benazir zata juyo awurin kawarta aneelerh tasan zaiyi wuya in bata fada mata ainihin abun da ya faru da mijinta da yar ta ba, daga nan zata gane tayi mata ƙaryane, tuna wannan yasa taji jikinta yayi sanyi ji take kamar ta hana au zuwa gidan saboda batason 6acin ran benazir ko kadan, fatanta Allah Yasa aneelerh tayi hankalin boye mata gaskiya.
"Mommy layla ni da aunty benazir wayafi kyau"? Zeenatu ce tay maganar da sokana
"Ay bama haɗi kin fita kyau nesa ba kusa ba" acewar layla da sauri hajiya sarah tace"a'a bana son sonkai Allah, aiko makaho ya shafa yasan wayafi kyau, auntynki tafi ki kyau nesa ba kusa ba, itafa jinin larabawa ce" kwa6e fuska zeenatu tayi jin abun da mommynta tace, da sauri ta kalli benazir dake yi mata dariya zumbura mata baki tayi
Murmushin gefen fuska tayi"hmm marwa kenan, kina abu kamar wadda ta samu cutar mantau, in ba ni ba waye dama yake ruke makullin store? da har zaki tambayi abla ina Yake bayan haka wani girkine zaki fara a yanzu? Bayan breakfast da kuka kammala ko dai baki kalli agogo bane?
Sosa ƙeya tayi"wai da afara dinner din da wuri"
Kaitsaye tace mata"a'a babu bukata, kamar yadda kuka saba haka zakuyi dole sai lokaci Ya cika, sannan pls idan kinason Yin magana dani basai kinzo dakina ba! Ki kirani da landline din kitchen kamar yadda kuka saba kirana ku sanar da ni abu"! Ko amsar marwa bata jiraba, taja kofa Ta datse
Rai a6ace marwa take kallon kofar, dakin wai har ita hajjaty zata ja ma kunne kan karta kara zuwa mata daki? Lallai buri ya yi kama da mutun da alama maganar hajiya saratu zata tabbata matarnan bata da gaskiya Allah kadai Yasan makircin da take kullawa da har batason wani Yazo dakinta, dani kike magana hajjaty saina zame maki karfen ƙafa agidan nan..." acikin ranta tafada Harta fara tafiya zata koma kitchen sai kuma ta dakata tana tariyo abunda Tajiyo adakin farkon dataje tafara yin la6e a kofar, tabbas taso tajiyo muryar hajjaty kamar tana magana da wani sai dai bata kaiga shaida hakan ba
Murmushin mugunta marwa tasaki a fili ta furta"ni da ke ne" tayi maganar tare da kama hanya tabar wurin.
Bayan komawar Hajjaty dakin, a zaune ta iske pravin yana jiran ta fuskarsa a yamutse saboda Ya tsani duk wani abu da zaija asirin shi Ya tonu
"Ta fada maki abun da ya kawo ta"? Ya jefa mata tambayar, zama tayi gefen shi kafin ta sanar da shi maganar da sukai da marwa
"Ni sai nake ga kamar leƙen asiri ta zo yi min saboda babu kwanciyar hanlali atare da ita" ta faɗa tana kallon fuskarsa
Pravin yace bana tunanin haka, just ki bar komai a hannuna idan ta ƙara yi maki wani abu da hankalinki bai kwanta da shi ba ki sanar dani" ta amsa mashi da toh
___________________________ANEELERH✍️
Yau saboda da zumudin zuwan benazir ko breakfast batay ba saboda tafi son idan benazir tazo su ci abincin a tare,
Su uku ne a kitchen suke aikin girka ma bakinsu abinci, gaba ɗaya kamshin abincin Ya cika ko'ina
"Pls ku yi sauri mu kammala ta faɗa min da wuri zasu zo, dakyar ma in basu tafo ba"
"Aunty Aneelerh wacece bakuwar tamu ne"? Ana ce ta faɗa tana kallon ta yayin da take tsaye gaban gass cooker tana aikin soye soye
"Ki bari idan tazo zaki ga wacece, nafi so na baki mamaki" cikin raha ta faɗa
"Allah ya kawo su lafiya, har nakosa na ganta"
"Ameen,"
Kallon zahra tay, gaba ɗaya hankalin ta ba akan su yake ba, tana a tsaye gaban counter, inda ta ɗaura juicer ga kayan marmari shaƙe da bowl da alama ta tafi duniyar tunani, tafi karfi mintuna biyar bata ta6uka komai ba, gaba ɗaya tunaninta na akan zayn, zuciyarta sai azalzalarta ta ke yi akan son ganinsa tayi missing dinsa.
"Zahra! Zahra!!" muryar aneelerh ce ta fargar da ita lokaci ɗaya ta sauke ajiyar zuciya tare da kallon ta
"Me kike tunanine? Naga kamar wani abu na damunki"? Murmushin yake tayi"bakomai auntyna.."
"Kedai faɗa min gaskiya ko dai damuwar rashin wayarki ne"? Da sauri tace a'a wlh ba haka bane
"To menene tun ɗazu kin ƙi motsawa, Na fa faɗa miki da wuri zasu zo watakil ma sun kamo hanya,"
"I'm sorry bari na fara Yanzu zan kammala in sha Allah kafin ma su ƙaraso mun gama komai"
Har sun kusa kammala girkin Mami ta shigo kitchen din tana fadin"wai wai irin wannan kamshi haka? Tun da ga ɗaki nake shaƙo shi, lallai Yau bakin mu zasu kwashi gyara" murmushi kowan nan su Ya saki
"Mami sannu zuwa, me kikeso na zuba maki" zahra ce tay maganar
"Ni iya juice din nan Ya ishe ni, sai dai bansan ko ummi zata bukaci wani abu ba"
Zahra tace"to mami, bari na zuba maku hada snacks"
"Yawwa zahra na, adan sanya min kankara aciki zaifi dadin sha" ta amsa mata da toh
Kallon aneelerh tayi"har su nawa ne zasu zo naji dazu kamar kince hada Yayanta shureim"
"Eh hada shi tare da ɗiyar Uncle din ta"
Mami tace masha Allah, Allah Ya kawo su lafiya, bari na koma falon kada na cika ku da surutu...." har ta kusa fita ta kuma juyowa tana fadin"zahra ina jira"
"Toh mami yanzun nan zaki ganni"
Bata jima da fita ba, zahra taje ta kai masu a falo....
_____________________________✍️
ƙarfe sha biyu daidai benazir tana atsaye gaban mirror ta kammala shiryawa cikin atampha riga da skirt sun kama jikinta, ta tsara make up akan fuskarta wani irin kyawune ya ƙara bayyana ta fito ɗas balarabiyarta, ta kashe daurin dankwali bayan ta gama ta miƙe ta dauko mayafin ta dake a ninke kan mattress ta yafa shi a kafaɗa, jujjuyawa tayi gaban mirror din kafin ta sakarma kanta murmushi kyawawan dimples dinsa suka lotsa..
"Aunty benazir yaya shureim yace in baki fito ba zamu tafi mu barki agida" ta cikin mirror ta hango zeentu da tayi maganar, kamar aljanna ta ca6a uban adon lace launin blue sky mai walwali da daukar ido, ɗan ƙaramin bakinta ta shafe shi da jan baki, ga wani daurin dankwali da akayi mata mai kama da ture kaga tsiya ta sauko da gashin ta, ziririn wuyanta yana asanye da ziririyar sarƙar diamond
A sukwane Benazir ta juyo fuska adaure ta kalle ta har saida tasha jinin jikin ta
Da ƙarfi ta furta"zeenatu? meye haka? Wannan ado sai kace zamu je gidan surukan ki?
Zazzare idanu tayi"ay ni ba su nayi ma kwalliya ba, ta yaya shureim ce amma idan baki son gani na da ita sai na canza wasu kayan in goge kwalliyar"
Yamutsa fuska benazir tayi"da dai yafi saboda baki kyau ba, ko meye na shafa powder wai ke kinga fuskarki kuwa? Kamar wata fatalwa? Kina fara dole sai kin shafa powder? So kike ki zama zabayyana ne"? shiru tayi tuni annurin fuskarta ya fara daukewa muryarta da yar shagwa6a tace"Aunty benazir ay na fada maki mommy ma tana shafa powder in zatay ma daddy kwalliya, kuma kema ay fara ce sol amma kina shafa powder...." kafin ta ƙare maganar benazir tace"naji, amma ay ban kaiki haske ba, bana son jan magana kije ki canza kaya in har kinaso mu je dake"
idanunta ne suka cicciko tab da kwalla benazir dake kallonta aranta ta ce kawai daga zan kara ki mu fita sai ki fini kyau hada wata sarƙar diamond...."
Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"wallahi bazan canza kayan ba, ay yaya shureim yace nayi mashi kyau, kuma yace duk inda zaije ƙafarsa ƙafata don haka dole aje dani aunty benazir" ranta yakai makura 6aci juyawa tayi da gudu zata fuce daga dakin cikin rashin sa'a highhills din kafarda suka turguɗe gaba daya ta tafi zata kife ƙasa cikin zafin nama dr shureim Ya ruƙota ta dawo jikinsa babu wanda yasan da zuwansa a cikin su ashe yabiyo bayan zeenatu.
Wankan shadda ne a jikin shi, zeenatu na jin dumin jikinshi ta ƙankameshi tana fada masa abun da benazir tace
Murmushi yasaki yana kallon benazir dake kallon sa
Da buɗar bakinsa sai cewa yai"ke baki gane ba? Kishi take yi dake saboda kinfi ta haɗuwa, itafa tun tana ƙarama in za'aje unguwa tafi so taga tafi kowa kyau don haka kada ki damu dabi'arta ce" jin wannan maganar yasa zeenatu fashewa da dariya har hakoranta suka bayyana.
Ta6e baki benazir tayi fuskarta da dan murmushi tace"yaya shureim yanzu abun da kai ka kyauta? Agaban zeenatu kake fadin hakan? So kake ta raina ni"?
Ɗaga mata gira yai alamar eh, jinjina kai tay"bakomai, na fahimci kafi son zeenatu akaina, soyayya ta rufe maka ido ya shureim ka rasa ma wa zaka so sai wannan ifritun sa'ar ƴar ciki na" ta fada da zolaya tana nuna zeenatu
"Ahaka nakesonta" ya fada yana murmushi, zeenatu sai dadi takeji har wani ƙara maƙala hannunta acikin nasa take
"Mu munyi gaba Ki iske mu a mota" yana ƙare maganar Yaja hannun zeenatu suka fuce, da sauri benazir ta dauko mayafi ta yafa a kafaɗa, hannun ta ruƙe da yar purse ta fito
A falo suka iske su hajiya layla suna fira kamar wani abu bai ta6a faruwa ba, Yanzu ta kwantar da hankalinta tun bayan abun da Ya faru jiya
"Zamu tafi mommy asanya mana albarkar iyaye" dr shurem ne yai maganar, atare suka dago da murmushi akan fuskokinsu
Hajiya sara tace"masha Allah, tabarakallahu ahsanul khalikin kunyi kyau kamar dollars" dariya suka sanya gaba dayansu
Fuskar hajiya layla da murmushi tace"nima naso aje unguwar nan dani amma zan bari zuwa nagaba" ta fada yayin da aranta take jin fargaban abun da benazir zata juyo awurin kawarta aneelerh tasan zaiyi wuya in bata fada mata ainihin abun da ya faru da mijinta da yar ta ba, daga nan zata gane tayi mata ƙaryane, tuna wannan yasa taji jikinta yayi sanyi ji take kamar ta hana au zuwa gidan saboda batason 6acin ran benazir ko kadan, fatanta Allah Yasa aneelerh tayi hankalin boye mata gaskiya.
"Mommy layla ni da aunty benazir wayafi kyau"? Zeenatu ce tay maganar da sokana
"Ay bama haɗi kin fita kyau nesa ba kusa ba" acewar layla da sauri hajiya sarah tace"a'a bana son sonkai Allah, aiko makaho ya shafa yasan wayafi kyau, auntynki tafi ki kyau nesa ba kusa ba, itafa jinin larabawa ce" kwa6e fuska zeenatu tayi jin abun da mommynta tace, da sauri ta kalli benazir dake yi mata dariya zumbura mata baki tayi