Sashe 50
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ga hanya nan ki tafi, Allah Ya raka taki gona" bayan ya furta hakan Ya juya azafafe Ya nufi bedroom dinsa Yana shiga ya dauki wayarsa, Call Ya danna tana fara ringing akayi picking
Muryarsa akausashe Yace"kada ku bar kowa ya fita daga gidan nan Idan Har bani na baku umarni ba"!
On the other hand Muryar wani basamuden mutun ta amsa mashi da cewa "Angama Yalla6ai" sauke wayar yayi
"Haba dear, why ba zaka bari su tafi ba, na fa ji kiran wayar da kayi, meyasa zaka rike su? Tun da matar nan ta nuna bata son tafiya to ka ƙyale su su tafi mana," muryar mom sarah a kule tayi maganar tana duban bayan shi...
Tamkar tayi magana da bango, babu alamun zai juyo ya fuskance ta balle harya amsa mata, Rai a6ace ta dawo ta gaban shi ta tsaya idanunta cike tab da kwalla ta furta"magana fa nake yi maka....."
da buɗar bakinsa sai cewa yai"Toh Uwata Ina sauraron ki" ya fada yana ruƙe qugunsa, Idanunsa akan fuskarta, bata san ya akai ta tsinci kanta da jin shakkarshi, sam takasa cigaba da yin maganar.
Gefen wuyanta ya shafa da tafin hannun sa"sau nawa zan ja maki kunne akan ki daina shiga abun da ya shafi dangina!" cikin sanyin murya tace"bazan ƙara ba"
Jinjina kanshi yai, kafin ya ƙara furta wata maganar, Muryar zeenatu ta karaɗe kunnan su.
Shigowarta kenan dakin ko sallama babu, Muryarta da shesshekar Kuka take fadin"daddy dan Allah kada ka bari su tafi, ni ban gaji da ganin su ba, ko kuma ka bari na bi su mu tafi a tare"
Juyawa yayi tare da daura idonsa akan ta, fuskarta tayi jawur hawaye na sintiri kan kuncinta.
Miƙa mata hannu yai da sauri ta nufe shi, hugging dinta yai tare da ɗaura hannunsa kan bayanta yana dan bubbuga shi cikin sigar lallashi.
"Ya isa, Ki daina kuka My daughter, ko dan saboda ke bazan bari su tafi ba, dolensu ne su zauna gidan nan ko suna so ko basa so" sauke ajiyar zuciya zeenatu tayi jin abunda yace, Hankalin ta ba karamin kwanciya yai ba, Hajiya Sarah ta kasa furta komai, Jikin ta yai mugun sanyi musamman yadda Taji Alhaji musa Yana magana da gadara babu ɗa'a a kalamansa....
A fusace Layla Ta nufi dakin ta, bayan tace da benazir taje ta haɗo kayanta su tafi, bin bayan ta Alhaji ubaid yayi kamar zai rufeta da bugu sai faɗa yake yi mata, Ko kallo bata isheshi ba, trolley din kayanta ta ɗauko Ta fara kwashe kayanta dake a cikin closet tana jerawa a akwatin.
Dawowa dr shureim yayi aɗan rude yake kallon dining din ganin babu kowa, da sauri Ya nufi dakin Benazir Yana shiga ya sameta, zuƙunne gefen gadon ta tana kuka, ga trolley din kayanta da ta gama haɗawa.
a ruɗe ya furta Benazir? Lafiya? Meya faru naga hawaye akan fuskarki"?
Jiki asanyaye ta mike tare da kallon shi, fuskarta tayi jawur da ita.
"Yaya shureim bayan kaje amsa kira, mommy ta fara faɗa akan ita bazata cigaba da zama gidan nan ba, shine tace min inzo in hada kayana mu tafi, ni kuma bana son tafiya saboda ban cimma burina ba, na ganin na haɗu da Aneelerh...."
Share mata hawayen ta ya somayi da hannayensa cikin sigar lallashi Yace"kiyi hakuri ki daina zubar da hawayen ki, bana so kina sanya damuwa aranki, amma ni kaina na goyi bayan ku tafi benazir! Ko dan saboda abunda ke faruwa dake agidan nan, Ina jin tsoron na rasa ki, kwata kwata hankalina bai kwanta da zamanki ba'
"Yaya shureim idan na tafi tayaya zan haɗu da Aneelerh"?
Harya buɗe baki zaiyi magana, kwatsam Wayarsa ta fara ringing, a hanzarce Ya duba sunan mai kiran nashi, wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskarshi, arude benazir tace yaya shureim lafiya naga kana murmushi"
"Alhamdulillah, Kiran da muke ta jira ne sai yau Allah Ya nufa zamu gana da su, kar6i kuyi magana, abban Aneelerh ne Yake Kiranki...." Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin picking call din kamar zata zauce tsabar murna
Muryarta da zumuɗi ta furta"Assalamu alaikum Abie Ina kwana...."
Kafin ta ƙare maganar unexpected Muryar Aneelerh ta ratsa kunnanta da wani sauti mai karfi ta furta"BENAZIR!! Mafarki nake ko gaske"? Fashewa da kuka benazir tayi jin muryar aminiyarta da kunnuwanta sukai maraicin ji na tsawon shekaru.
Cikin shesshekar kuka tace"Wallahi nice Aneelerh, nice benazir din da kika sani..."
Kafin ta ƙare maganar, Itama Aneelerh ta fashe da matsanancin kuka tana fadin"Benazir baki kyauta ma kanki ba! Meyasa? Meyasa? Meyasa kika gudu na tsawon shekaru? Idan wani abu ke damunki ba zaki faɗa mana ba? Kinsan irin kunci da radadin da muka ji bayan tafiyarki? Kin kama hanya kin gudu kin bar jinjira acikin kwamin wanka, Da ranki da lafiyarki baki ta6a kira kinji awani hali Yarki take a ciki ba, wai dan Allah meyasa kikayi haka benazir meyasa.....?" kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya sarƙe makoshin ta.
Tsananin tausayin su ne Ya kama dr shureim, tun dazu yana atsaye yana kallon Banazir kuma yana sauraran komai da suke tattaunawa.
"Dan Allah Aneleerh Ki nutsu inyi maki bayani..." Aneelerh bata bari tayi mata bayanin ba rai a6ace tace"me zaki faɗa min benazir? Ni meyasa ma kika kirani ne? lokacin da yakamata ki kira baki kira ba sai yanzu da lokaci ya kure...." hankali atashe benazir ta ke sauraron ta idanunta sun kaɗa jawur da su la66anta na kerma ta furta"meyasa kikace haka"?
Ɗuff taji Aneelerh ta kashe kiran, hawaye na sintiri ta dago tana kallon shureim wanda tuni jikin shi ya gama yin sanyi.
"Yaya shureim ta kashe kiran, dama nasani ba lallai ta kula ni ba..." tsananin tausayinta ne Ya kama shi, hannu yasa ya kar6i wayar, Ya sake Kiran Aneelerh taƙi ɗagowa.
Text message Ya tura mata
_Aneelerh ki ɗaga kiran, Ba benazir bace yayanta dr shureim ne Ina son Yin magana dake_
A 6angaren Aneelerh, Jiki amace ta sulale kan carpet ta zauna dirshan sai kuka takeyi, bakomai take tunawa ba face Angel da tajuddeen, Taji takaicin yadda Benazir tayi watsi da rayuwarsu gashi Yanzu ita benazir din ta dawo su kuma sun 6ata babu su a doron duniya
Muryar Angel ta soma tariyowa kalaman da saba fada mata tuntana yar ƙanƙanuwarta
_Aunty aneelerh wai meyasa Mommyna bataso na? gani yar kyakkyawa dani kowa rububina yakeyi amma ita, bata damu dani ba, shine ma ta haifeni ta bar ni acikin kwamin ka, idan bata sona to meyasa ta haife ni ay da ta sani ta kashe ni acikin ta_
Ƙarar shigowar sakon ne Ya fargar da ita daga zurfin tunanin da ta shiga, zuciyartace ta dinga tunzurata akan kada ta duba wayar ta ƙyale ta kawai, saboda ta bata haushi, Taji zafin abunda tayi.
Wayar sai ringing takeyi taki dubawa, kasa jurewa tayi, saboda ita kanta tayi kewar aminiyartata, bazata taba mantawa da ƙawancensu ba, duk da taci wahalar banezir saboda rashin jin maganarta.
Yatsun hannunta na kerma ta ruƙo wayar ta duba sakon, bayan ta gama karantawa, a kagare ta soma kokarin bin kiran don taji me dr shureim zai faɗa mata, aranta tana mai mamakin bayyanarsu lokaci ɗaya.
Video Call ta kirasu don ta ƙara tabbar da cewa su dinne, bayan sunyi picking call din kallon kallon suka soma jefawa junansu, kowa yasha kuka, hakika sunyi mamakin canzawar da sukayi, duk sun fara manyanta...
Cikin sanyin murya ta furta"ya shureim! Dama kana nan"!
Jinjina mata kai yai alamar eh, kafin Ya soma magana cikin nutsastsiyar muryar shi.
"Aneelerh, inaso ki nutsu ki saurari abun da zan fada maki" amsa mashi tayi da toh, saboda tana ganin girma dr shureim.
"Abun da Ya faru da banezir bayin kanta bane, mu kanmu bamu san da hakan ba sai lokacin da ta dawo, bata a cikin hayyacinta gaba ɗaya alamomin da muka gani ajikinta ya tabbatar mana da cewa Kurciya akayi mata, shiyasa ta gudu tabar yarinyarta batare data tuntu6i kowa nata ba......" atsanake shureim ya fayyace mata komai, Ita kanta benazir din batasan da abun da suke zargin anyi mata ba sai yanzu da taji abakin dr shureim, hankalinta ba karamin tashi yayi ba, aneelerh kuwa jikinta yagama mutuwa, cikin tashin hankali take ambaton inna lillahi wa'inna ilahirraji'un.
Dr shureim Yace"hakuri zamuyi da abunda Ya riga ya faru, bana so muna tuna ba....." nasiha ya cigaba dayi masu har saida Yaga hankalin su Ya kwanta, kafin Ya bar wayar a hannun benazir Ya basu wuri don su gana da junansu
Kamar yau ce rana ta farko da suka fara haɗuwa, sai bin kansu suke yi da kallon kurulla, Allah ne kaɗai Yasan irin kewar juna da su ka yi.
"Benazir bansan yadda zan misalta maki farin cikin da nake a ciki ba, Allah shine shaidata, Naji dadin ganinki da ranki da lafiyarki"
Cikin sanyin murya tace"nima haka Aneeleerh, ashe da rabon zamu gana bayan tsawon lokaci"? Ta fada tana matse kwallar da ta cike idununta.
"Aneelerh, Ina Yarinyata dana bari? Ina mijina Yake? Mommy ta fada min basa kasar nan amma ni ban yarda da maganarta ba, dan Allah ki fada min gaskiya, saboda nasan ke kadaice zaki fada min"
Fuskar Aneelerhh ɗauke da matsananciyar damuwa take kallon benazir dama sai da tayi fargaban tambayar da zatai mata, tuni taji zafafan hawaye sun cika mata idanunta.
"Aneelerh kinyi shiru baki ce komai ba? Pls ki yi min magana wlh ji nake kamar zan zauce saboda ƙagarar da nayi na son ganin su ..." ta faɗa tana dubanta
"Kada ki ji komai, Ki faɗamin kawai ko da ace sun mutune zan rungumi ƙaddara..." cikin karfin hali ta faɗa, tun da tafara maganar Aneeleeh ke kallonta gwanin ban tausayi.
bata jin zata Iya sanar da ita a yanzu, ko dan gudun kada zuciyarta ta buga, ƙwara ta kwantar mata da hankalin ta.
Ƙaƙaro murmushi tayi akan fuskarta
"Abun da mami ta faɗa maki gaskiya ne, suna nan cikin koshin lafiya, sun yi tafiya zuwa south korea inda Uncle dinsa abdalla ke zaune, amma ina ji araina sun kusa dawowa"
Tsabar farin ciki yasa banezir sakin dariya har fararen hakoranta suka bayyana, Aneelerh dake kallonta tsantsar tausayintane Ya ƙara kamata.
Muryarsa akausashe Yace"kada ku bar kowa ya fita daga gidan nan Idan Har bani na baku umarni ba"!
On the other hand Muryar wani basamuden mutun ta amsa mashi da cewa "Angama Yalla6ai" sauke wayar yayi
"Haba dear, why ba zaka bari su tafi ba, na fa ji kiran wayar da kayi, meyasa zaka rike su? Tun da matar nan ta nuna bata son tafiya to ka ƙyale su su tafi mana," muryar mom sarah a kule tayi maganar tana duban bayan shi...
Tamkar tayi magana da bango, babu alamun zai juyo ya fuskance ta balle harya amsa mata, Rai a6ace ta dawo ta gaban shi ta tsaya idanunta cike tab da kwalla ta furta"magana fa nake yi maka....."
da buɗar bakinsa sai cewa yai"Toh Uwata Ina sauraron ki" ya fada yana ruƙe qugunsa, Idanunsa akan fuskarta, bata san ya akai ta tsinci kanta da jin shakkarshi, sam takasa cigaba da yin maganar.
Gefen wuyanta ya shafa da tafin hannun sa"sau nawa zan ja maki kunne akan ki daina shiga abun da ya shafi dangina!" cikin sanyin murya tace"bazan ƙara ba"
Jinjina kanshi yai, kafin ya ƙara furta wata maganar, Muryar zeenatu ta karaɗe kunnan su.
Shigowarta kenan dakin ko sallama babu, Muryarta da shesshekar Kuka take fadin"daddy dan Allah kada ka bari su tafi, ni ban gaji da ganin su ba, ko kuma ka bari na bi su mu tafi a tare"
Juyawa yayi tare da daura idonsa akan ta, fuskarta tayi jawur hawaye na sintiri kan kuncinta.
Miƙa mata hannu yai da sauri ta nufe shi, hugging dinta yai tare da ɗaura hannunsa kan bayanta yana dan bubbuga shi cikin sigar lallashi.
"Ya isa, Ki daina kuka My daughter, ko dan saboda ke bazan bari su tafi ba, dolensu ne su zauna gidan nan ko suna so ko basa so" sauke ajiyar zuciya zeenatu tayi jin abunda yace, Hankalin ta ba karamin kwanciya yai ba, Hajiya Sarah ta kasa furta komai, Jikin ta yai mugun sanyi musamman yadda Taji Alhaji musa Yana magana da gadara babu ɗa'a a kalamansa....
A fusace Layla Ta nufi dakin ta, bayan tace da benazir taje ta haɗo kayanta su tafi, bin bayan ta Alhaji ubaid yayi kamar zai rufeta da bugu sai faɗa yake yi mata, Ko kallo bata isheshi ba, trolley din kayanta ta ɗauko Ta fara kwashe kayanta dake a cikin closet tana jerawa a akwatin.
Dawowa dr shureim yayi aɗan rude yake kallon dining din ganin babu kowa, da sauri Ya nufi dakin Benazir Yana shiga ya sameta, zuƙunne gefen gadon ta tana kuka, ga trolley din kayanta da ta gama haɗawa.
a ruɗe ya furta Benazir? Lafiya? Meya faru naga hawaye akan fuskarki"?
Jiki asanyaye ta mike tare da kallon shi, fuskarta tayi jawur da ita.
"Yaya shureim bayan kaje amsa kira, mommy ta fara faɗa akan ita bazata cigaba da zama gidan nan ba, shine tace min inzo in hada kayana mu tafi, ni kuma bana son tafiya saboda ban cimma burina ba, na ganin na haɗu da Aneelerh...."
Share mata hawayen ta ya somayi da hannayensa cikin sigar lallashi Yace"kiyi hakuri ki daina zubar da hawayen ki, bana so kina sanya damuwa aranki, amma ni kaina na goyi bayan ku tafi benazir! Ko dan saboda abunda ke faruwa dake agidan nan, Ina jin tsoron na rasa ki, kwata kwata hankalina bai kwanta da zamanki ba'
"Yaya shureim idan na tafi tayaya zan haɗu da Aneelerh"?
Harya buɗe baki zaiyi magana, kwatsam Wayarsa ta fara ringing, a hanzarce Ya duba sunan mai kiran nashi, wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskarshi, arude benazir tace yaya shureim lafiya naga kana murmushi"
"Alhamdulillah, Kiran da muke ta jira ne sai yau Allah Ya nufa zamu gana da su, kar6i kuyi magana, abban Aneelerh ne Yake Kiranki...." Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin picking call din kamar zata zauce tsabar murna
Muryarta da zumuɗi ta furta"Assalamu alaikum Abie Ina kwana...."
Kafin ta ƙare maganar unexpected Muryar Aneelerh ta ratsa kunnanta da wani sauti mai karfi ta furta"BENAZIR!! Mafarki nake ko gaske"? Fashewa da kuka benazir tayi jin muryar aminiyarta da kunnuwanta sukai maraicin ji na tsawon shekaru.
Cikin shesshekar kuka tace"Wallahi nice Aneelerh, nice benazir din da kika sani..."
Kafin ta ƙare maganar, Itama Aneelerh ta fashe da matsanancin kuka tana fadin"Benazir baki kyauta ma kanki ba! Meyasa? Meyasa? Meyasa kika gudu na tsawon shekaru? Idan wani abu ke damunki ba zaki faɗa mana ba? Kinsan irin kunci da radadin da muka ji bayan tafiyarki? Kin kama hanya kin gudu kin bar jinjira acikin kwamin wanka, Da ranki da lafiyarki baki ta6a kira kinji awani hali Yarki take a ciki ba, wai dan Allah meyasa kikayi haka benazir meyasa.....?" kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da ya sarƙe makoshin ta.
Tsananin tausayin su ne Ya kama dr shureim, tun dazu yana atsaye yana kallon Banazir kuma yana sauraran komai da suke tattaunawa.
"Dan Allah Aneleerh Ki nutsu inyi maki bayani..." Aneelerh bata bari tayi mata bayanin ba rai a6ace tace"me zaki faɗa min benazir? Ni meyasa ma kika kirani ne? lokacin da yakamata ki kira baki kira ba sai yanzu da lokaci ya kure...." hankali atashe benazir ta ke sauraron ta idanunta sun kaɗa jawur da su la66anta na kerma ta furta"meyasa kikace haka"?
Ɗuff taji Aneelerh ta kashe kiran, hawaye na sintiri ta dago tana kallon shureim wanda tuni jikin shi ya gama yin sanyi.
"Yaya shureim ta kashe kiran, dama nasani ba lallai ta kula ni ba..." tsananin tausayinta ne Ya kama shi, hannu yasa ya kar6i wayar, Ya sake Kiran Aneelerh taƙi ɗagowa.
Text message Ya tura mata
_Aneelerh ki ɗaga kiran, Ba benazir bace yayanta dr shureim ne Ina son Yin magana dake_
A 6angaren Aneelerh, Jiki amace ta sulale kan carpet ta zauna dirshan sai kuka takeyi, bakomai take tunawa ba face Angel da tajuddeen, Taji takaicin yadda Benazir tayi watsi da rayuwarsu gashi Yanzu ita benazir din ta dawo su kuma sun 6ata babu su a doron duniya
Muryar Angel ta soma tariyowa kalaman da saba fada mata tuntana yar ƙanƙanuwarta
_Aunty aneelerh wai meyasa Mommyna bataso na? gani yar kyakkyawa dani kowa rububina yakeyi amma ita, bata damu dani ba, shine ma ta haifeni ta bar ni acikin kwamin ka, idan bata sona to meyasa ta haife ni ay da ta sani ta kashe ni acikin ta_
Ƙarar shigowar sakon ne Ya fargar da ita daga zurfin tunanin da ta shiga, zuciyartace ta dinga tunzurata akan kada ta duba wayar ta ƙyale ta kawai, saboda ta bata haushi, Taji zafin abunda tayi.
Wayar sai ringing takeyi taki dubawa, kasa jurewa tayi, saboda ita kanta tayi kewar aminiyartata, bazata taba mantawa da ƙawancensu ba, duk da taci wahalar banezir saboda rashin jin maganarta.
Yatsun hannunta na kerma ta ruƙo wayar ta duba sakon, bayan ta gama karantawa, a kagare ta soma kokarin bin kiran don taji me dr shureim zai faɗa mata, aranta tana mai mamakin bayyanarsu lokaci ɗaya.
Video Call ta kirasu don ta ƙara tabbar da cewa su dinne, bayan sunyi picking call din kallon kallon suka soma jefawa junansu, kowa yasha kuka, hakika sunyi mamakin canzawar da sukayi, duk sun fara manyanta...
Cikin sanyin murya ta furta"ya shureim! Dama kana nan"!
Jinjina mata kai yai alamar eh, kafin Ya soma magana cikin nutsastsiyar muryar shi.
"Aneelerh, inaso ki nutsu ki saurari abun da zan fada maki" amsa mashi tayi da toh, saboda tana ganin girma dr shureim.
"Abun da Ya faru da banezir bayin kanta bane, mu kanmu bamu san da hakan ba sai lokacin da ta dawo, bata a cikin hayyacinta gaba ɗaya alamomin da muka gani ajikinta ya tabbatar mana da cewa Kurciya akayi mata, shiyasa ta gudu tabar yarinyarta batare data tuntu6i kowa nata ba......" atsanake shureim ya fayyace mata komai, Ita kanta benazir din batasan da abun da suke zargin anyi mata ba sai yanzu da taji abakin dr shureim, hankalinta ba karamin tashi yayi ba, aneelerh kuwa jikinta yagama mutuwa, cikin tashin hankali take ambaton inna lillahi wa'inna ilahirraji'un.
Dr shureim Yace"hakuri zamuyi da abunda Ya riga ya faru, bana so muna tuna ba....." nasiha ya cigaba dayi masu har saida Yaga hankalin su Ya kwanta, kafin Ya bar wayar a hannun benazir Ya basu wuri don su gana da junansu
Kamar yau ce rana ta farko da suka fara haɗuwa, sai bin kansu suke yi da kallon kurulla, Allah ne kaɗai Yasan irin kewar juna da su ka yi.
"Benazir bansan yadda zan misalta maki farin cikin da nake a ciki ba, Allah shine shaidata, Naji dadin ganinki da ranki da lafiyarki"
Cikin sanyin murya tace"nima haka Aneeleerh, ashe da rabon zamu gana bayan tsawon lokaci"? Ta fada tana matse kwallar da ta cike idununta.
"Aneelerh, Ina Yarinyata dana bari? Ina mijina Yake? Mommy ta fada min basa kasar nan amma ni ban yarda da maganarta ba, dan Allah ki fada min gaskiya, saboda nasan ke kadaice zaki fada min"
Fuskar Aneelerhh ɗauke da matsananciyar damuwa take kallon benazir dama sai da tayi fargaban tambayar da zatai mata, tuni taji zafafan hawaye sun cika mata idanunta.
"Aneelerh kinyi shiru baki ce komai ba? Pls ki yi min magana wlh ji nake kamar zan zauce saboda ƙagarar da nayi na son ganin su ..." ta faɗa tana dubanta
"Kada ki ji komai, Ki faɗamin kawai ko da ace sun mutune zan rungumi ƙaddara..." cikin karfin hali ta faɗa, tun da tafara maganar Aneeleeh ke kallonta gwanin ban tausayi.
bata jin zata Iya sanar da ita a yanzu, ko dan gudun kada zuciyarta ta buga, ƙwara ta kwantar mata da hankalin ta.
Ƙaƙaro murmushi tayi akan fuskarta
"Abun da mami ta faɗa maki gaskiya ne, suna nan cikin koshin lafiya, sun yi tafiya zuwa south korea inda Uncle dinsa abdalla ke zaune, amma ina ji araina sun kusa dawowa"
Tsabar farin ciki yasa banezir sakin dariya har fararen hakoranta suka bayyana, Aneelerh dake kallonta tsantsar tausayintane Ya ƙara kamata.