Sashe 140
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Juyawa yai ya nufi closet dinta ya dauko mata abaya ya miƙa mata, hannunta na kerma ta kar6a tasaka a jikin ta.
"Kin ci abinci"
"Bana jin yunwa ɗazu da safe na cika kina"
"Okey, ki zauna ki jira ni"
make mashi kafada tay"dan Allah kada ka tafi kabarni ni kadai"
"Ba tafiya zanyi ba, ruwa zan dauko" amsa mashi tay da toh ta zauna gefen gadon tana jiran shi, badajimawa ba ya dawo hannun shi ruke da Cup din ruwa ya zauna ya taimaka mata tasha maganin ganin yadda hannunta ke kerma bayan ta kammala sha, yasa Yace ta kwanta ta huta, marairaice mashi fuska tay da shawaga6a tace"so kake inyi bacci donka tafi kabarni ko"
Yanayin yadda takeyi mashi magana ba karamin kashe mashi jiki ya ke yi ba, ba zai juri kallon ta ba.
"Ba tafiya zanyi ba, zan koma falo," miƙewa tay"nima zanje falon"
"Pls ki kwanta ki huta, babu lafiya a jikinki"
Kuka ta saka mashi"haba ya shureim nagaji da zama ni kadai, ya kake so nayi da raina? nasan tafiya zakai kabarni..." lallashinta ya farayi"ya isa haka ki daina zubda hawayenki bana so, Idan saboda ni ne muje falon tare saiki kwanta kan sofa, in har hakan zai kwantar maki da hankali" ajiyar zuciya ta sauke ya zaro hanky daga aljihu ya share mata tears din fuskarta, ya ruƙo hannunta suka fito daga dakin
________________________________✍️
A bangren su Aneeleerh har wuraren biyu na rana suna agidan, Sun Mori lokacin su tare da su Unaisah sallah kadai ta tadasu, sun sha fira da su kamar ƙawayansu, sun ɗebe masu kewa ba kadan ba, musamman Aneelerh taji dadi tayi farin cikin ganin yadda Junaid Ya saki Jiki da Unaisah in a short time su ka shaku da junan su, wasan doki suka dinga yi mashi ita da Batool, akan bayanta ta ɗaura shi ta dinga rarrafe tana zagaye sitting room din batare da gajiyawa ba, Sai murna yake yana fadin doki sukuta sukuta.
Aneelerh tasha ruwan mamaki Ganin Yadda Yake tiƙar dariyar, yaushe rabon da ta ga dariyar Junaid tun ranar da Ana ta 6ace ko murmushi bayayi ga ƙiwuya amma yau ya sake kamar bashi ba, har ta fara tunanin in suka koma gida zata lalla6a shi cikin lallami ta tambaye shi meya faru da ana aranar watakil ya fada mata tun da taga bakin shi ya buɗe.
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
har video Benazir ta ɗauke su da wayarta saboda sun burgeta taji daɗin walwalwar da su ke yi cikin nishaɗi bayan sun gama yi mashi wasan dokin, Unaisah ta daure idanunta da mayafinta ta dinga zagaye dakin tana neman su, Batool taja hannun junaid suka dinga garata sai da suka wahalar da ita dakyar ta cafko baby junaid ya dinga ihu Yana tsalle yace mata shima ta ɗaure mashi ido yayi wasan, ta cire mayafin ta ɗaure mashi idanunshi yadda bazai ji zafi ba, kamar makaho haka ya rinƙa miƙa hannu ya na laluban su da gangan Unaisah ta je gaban shi ta tsaya don kada su wahalar da shi, cafko rigarta yai da hannayen shi ya ƙankameta yana fadin ya kama ya kama.
Duba agoga Aneelerh tayi kafin ta kalli Benazir"yakamata mu tafi, kada mami taji na dade" sai lokacin Benazir tace"yanzu abun hawa zamu hau mu koma? nasan ko na kira dr shureim ba lallai yazo ba saboda rashin lafiyar zeenatu..." ta fada tare da ta6e baki
Murmushi Aneelerh tay saboda ta gano me take mawa
"Pls ki kira mijina ya maida mu gidajen mu" cike da zolaya tace"ki dai iya bakinki, Kada babyn naki taji kina kiran sunan ubanta da sunan mijinki, Yanzu ki tada mana 6alli" murmushi Benazir tay tare da kallon su Unaisah dake a zaune kan rug sun gaji da wasan hutawa suke.
Waya ta curo ta danna ma Taj kira tana fara ringing yai picking,
Tunkafin tay magana Yace"Aneelerh ykk ya su Unaisah, Ina fata kunji dadin kasancewa da su"
"Alhamdulillah, gasu nan zaune sun gama shan wasa da baby junaid, shima yau yaji dadin ganin yar uwarsa"
ta fada tana kallon su
"Masha Allah, Naji dadin jin hakan, Yanzu nake kokarin, kiranki,yakamata su koma yan uwansu sun fara neman su"
"Allah sarki, Nima abun da yasa na kiraka kenan, mun shirya tafiya kuma dr shureim bayanan Ya tafi ɗasu aka kira shi daga gida har yanzu bai dawo ba, mun kira layin shi baya shiga" ta faɗa tana kallon Benazir data tsare ta da ido fatanta Allah yasa ya amince yazo ya dauke su.
Shiru yayi jimm na ɗan wani lokacin kafin yace"Okay, Naso na maida ku gida amma bana a kusa, zansa jami'en mu ya kai ku" haɗe fuska Benazir tay tuni idanunta suka ciko tab da kwalla, gani take kamar ya ɗago su ne shiyasa yace zai turo jami'en su ya kaisu amaimakon shi
"Shikenan, Mun gode ssai," tay mashi sallama,
Kallon juna su ka yi ita da Benazir
"Nasan saboda ni ne yace bazai maida mu ba" ruko hannun ta Aneelerh tay"pls ki yi hakuri kamar yadda na fada maki, bana so yaran nan su fahimci wani abu kwara mu rabu lafiya, ki daure idan muka shiga mota zamuyi magana, nayi maki alkawarin zan taimaka maki mu shawo kan shi"
A hankali Benazir ta share hawayen ta, har ga Allah bata son tafiya tabar gidan ji take kamar su kwana anan sai dai tasan ba abune mai yiwuwa ba.
Suna azaune jami'en da taj ya turo yayi masu sallama Yace su fito Yana jiran su.
Hankalin Unaisah ba karamin tashi yayi ba ganin za'a rabata da baby junaid, bawan Allah sai ƙara kankameta ya ke yi duk don kada su raba shi da ita, bayan sun fito abakin motar suka tsaya, Aneeleeh ta kar6i junaid yana kukan rabuwa da Angel tace mashi yai hakuri za ta zo har gida ta same shi, dakyar tayi mashi wayau ya hakura.
"Toh Mu zamu wuce, zamu tafi mu bar ku da kewar mu" Anila ta fada tana kallon su, duk sun ɗaure fuska saboda basu son su tafi
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Dan Allah yaushe zaku dawo"? Cikin sanyin murya batool ta yi maganar, Benazir tace"in dai mune kusha kuruminku, har sai kun gaji da ganinmu" dadine ya lullu6e su, miƙa masu hannu tay da sauri suka matsa kusa da ita ta haɗa su duka ta rungume su, Cikin kunne ta yi ma Unaisah raɗa"zan kar6i contact dinki a gurin Aneelerh, Ki kula min da kanki, Ina kaunarki sosai" murmushi unaisah tasaki"nima zanyi kewarki mommyna"
Bayan sun raba jikin su daga na juna ta dubi Batool ta shafa gefen fuskarta da tafin hannun ta
"zanyi kewarki, Yau na fara ganinki amma kin kwanta min araina, kamar yadda Babyna ta sace zuciyata, Ina kaunarki, Ki kula min da kanki" dariyar farin ciki batool tayi"in sha Allah, nagode sosai aunty Benazir, nima ina sonki, " taso ta tambaye su dr shureim amma saita kasa saboda kunyarta da take ji.
Miƙa masu hannu Aneelerh tay, itama tay hugging dinsu baby junaid ya haɗe rai Idanunshi sun ciko tab da kwalla.
Sumbatar kumatun shi Unaisah tay, cikin sigar lallashi tace"I'm sorry my little bro, Zanzo har gidan ku, Aunty aneelerh pls ki kwantar masa da hankali bana so yayi kukan rashi na" ta fada tana kallon fuskar junaid
"Kada ki damu bazan bari yai kuka ba, ku gaida mana mutanan gidan" atare suka amsa masu da toh
Akan idonsu Motar su ta fuce daga gidan, fitar su keda wuya Ummi ta fito daga kofar falon har bayan motar saida ta gani yayin da take karasa fucewa daga gate din
Sun yi tsaye cike da jimamin tafiyar su, baby junaid Ya tsaya masu aransu.
Kwata kwata basu lura da ummi ba har saida ta ambaci sunayen su da sauri suka dube ta
"Daga ina kuke? Motar waye naga ta fita yanzu? Kallon ta su ka yi ba tare da sun furta kalma ba
"Ba ku ji Ina magana bane"?
Ajiyar zuciya suka sauke atare Unaisah tace"bamu san motar wanane ba, muma yanzu muka fito"
"Daga ina"? Kallon juna su ka yi
"Kamar baku da gaskiya, ku fada min mana daga ina kuke" ta fada tana jifansu da kallon tuhuma.
"Mun je part din daddyna ne, daga can muke" ba dan ta yarda da su ba tace"shine ko ku fadamin ay dana shirya mun je tare, gaskiya baku kyauta min ba" ta fada tana jifar su da harara dariya sukai atare..
"Ku wuce mu shiga ciki," gaba tay suka bi bayan ta hannun su ruke cikin na juna
*💋BOSS BATURE✊*
Da marece tana a zaune gaban mirror chair tana yin wani makeup ɗin akan fuskarta, saboda kwalliyar da ta yi ɗazu ta goge.
gown ɗin ɗazu ce a jikinta da alama bata gama gayun ba, ko kuma wanda akayi dominsa bai gani ba, ita kaɗai ce a ɗakin, sai ƴan shafe shafe take ma fuskarta, cikin ƙanƙanin lokaci ta gama tayi matuƙar yin kyau, ta nutsu tana kallon fuskarta ta cikin mirror, pink lips dinta sun jiƙu da lip gloss sai shinning su ke.
Knocking ɗin kofar da akai ne Yasa ta ɗan juya ta kalli room door ɗin su.
Jemimah ce ta shigo jikinta sanye da Overall, ta ɗaure blonde hair ɗinta da ribbon ta fito ɗass Farar fatar ta gwanin sha'awa.
"Little Sis halan dalili ne Ya shigo dake dakin mu"?
Ta faɗi hakanne don tasan bai wuci chocolate tazo roƙo a gurin ta ba.
murmushi tayi"Aunty ummi ce tace In kiraki, kizo mu yi dinner, in ba zaki ci ba sai mu cinye naki" dariya Unaisah tay"su acici mala'ikun tauna, Ku da baku gajiya da Cin abinci, Har wani fadi kike zaku cinye abinci na ai ko dana karanta maku Charman dudu cikin kowa ya kumbure"
waro idanu Jemaimah tay"Wlh wasa nake maki fa" miƙewa Unaisha tay daga kan chair din"oho in ma dagaske ne bismillah, ku ci ku ga abun da zai biyo baya"
"Kin ci abinci"
"Bana jin yunwa ɗazu da safe na cika kina"
"Okey, ki zauna ki jira ni"
make mashi kafada tay"dan Allah kada ka tafi kabarni ni kadai"
"Ba tafiya zanyi ba, ruwa zan dauko" amsa mashi tay da toh ta zauna gefen gadon tana jiran shi, badajimawa ba ya dawo hannun shi ruke da Cup din ruwa ya zauna ya taimaka mata tasha maganin ganin yadda hannunta ke kerma bayan ta kammala sha, yasa Yace ta kwanta ta huta, marairaice mashi fuska tay da shawaga6a tace"so kake inyi bacci donka tafi kabarni ko"
Yanayin yadda takeyi mashi magana ba karamin kashe mashi jiki ya ke yi ba, ba zai juri kallon ta ba.
"Ba tafiya zanyi ba, zan koma falo," miƙewa tay"nima zanje falon"
"Pls ki kwanta ki huta, babu lafiya a jikinki"
Kuka ta saka mashi"haba ya shureim nagaji da zama ni kadai, ya kake so nayi da raina? nasan tafiya zakai kabarni..." lallashinta ya farayi"ya isa haka ki daina zubda hawayenki bana so, Idan saboda ni ne muje falon tare saiki kwanta kan sofa, in har hakan zai kwantar maki da hankali" ajiyar zuciya ta sauke ya zaro hanky daga aljihu ya share mata tears din fuskarta, ya ruƙo hannunta suka fito daga dakin
________________________________✍️
A bangren su Aneeleerh har wuraren biyu na rana suna agidan, Sun Mori lokacin su tare da su Unaisah sallah kadai ta tadasu, sun sha fira da su kamar ƙawayansu, sun ɗebe masu kewa ba kadan ba, musamman Aneelerh taji dadi tayi farin cikin ganin yadda Junaid Ya saki Jiki da Unaisah in a short time su ka shaku da junan su, wasan doki suka dinga yi mashi ita da Batool, akan bayanta ta ɗaura shi ta dinga rarrafe tana zagaye sitting room din batare da gajiyawa ba, Sai murna yake yana fadin doki sukuta sukuta.
Aneelerh tasha ruwan mamaki Ganin Yadda Yake tiƙar dariyar, yaushe rabon da ta ga dariyar Junaid tun ranar da Ana ta 6ace ko murmushi bayayi ga ƙiwuya amma yau ya sake kamar bashi ba, har ta fara tunanin in suka koma gida zata lalla6a shi cikin lallami ta tambaye shi meya faru da ana aranar watakil ya fada mata tun da taga bakin shi ya buɗe.
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
har video Benazir ta ɗauke su da wayarta saboda sun burgeta taji daɗin walwalwar da su ke yi cikin nishaɗi bayan sun gama yi mashi wasan dokin, Unaisah ta daure idanunta da mayafinta ta dinga zagaye dakin tana neman su, Batool taja hannun junaid suka dinga garata sai da suka wahalar da ita dakyar ta cafko baby junaid ya dinga ihu Yana tsalle yace mata shima ta ɗaure mashi ido yayi wasan, ta cire mayafin ta ɗaure mashi idanunshi yadda bazai ji zafi ba, kamar makaho haka ya rinƙa miƙa hannu ya na laluban su da gangan Unaisah ta je gaban shi ta tsaya don kada su wahalar da shi, cafko rigarta yai da hannayen shi ya ƙankameta yana fadin ya kama ya kama.
Duba agoga Aneelerh tayi kafin ta kalli Benazir"yakamata mu tafi, kada mami taji na dade" sai lokacin Benazir tace"yanzu abun hawa zamu hau mu koma? nasan ko na kira dr shureim ba lallai yazo ba saboda rashin lafiyar zeenatu..." ta fada tare da ta6e baki
Murmushi Aneelerh tay saboda ta gano me take mawa
"Pls ki kira mijina ya maida mu gidajen mu" cike da zolaya tace"ki dai iya bakinki, Kada babyn naki taji kina kiran sunan ubanta da sunan mijinki, Yanzu ki tada mana 6alli" murmushi Benazir tay tare da kallon su Unaisah dake a zaune kan rug sun gaji da wasan hutawa suke.
Waya ta curo ta danna ma Taj kira tana fara ringing yai picking,
Tunkafin tay magana Yace"Aneelerh ykk ya su Unaisah, Ina fata kunji dadin kasancewa da su"
"Alhamdulillah, gasu nan zaune sun gama shan wasa da baby junaid, shima yau yaji dadin ganin yar uwarsa"
ta fada tana kallon su
"Masha Allah, Naji dadin jin hakan, Yanzu nake kokarin, kiranki,yakamata su koma yan uwansu sun fara neman su"
"Allah sarki, Nima abun da yasa na kiraka kenan, mun shirya tafiya kuma dr shureim bayanan Ya tafi ɗasu aka kira shi daga gida har yanzu bai dawo ba, mun kira layin shi baya shiga" ta faɗa tana kallon Benazir data tsare ta da ido fatanta Allah yasa ya amince yazo ya dauke su.
Shiru yayi jimm na ɗan wani lokacin kafin yace"Okay, Naso na maida ku gida amma bana a kusa, zansa jami'en mu ya kai ku" haɗe fuska Benazir tay tuni idanunta suka ciko tab da kwalla, gani take kamar ya ɗago su ne shiyasa yace zai turo jami'en su ya kaisu amaimakon shi
"Shikenan, Mun gode ssai," tay mashi sallama,
Kallon juna su ka yi ita da Benazir
"Nasan saboda ni ne yace bazai maida mu ba" ruko hannun ta Aneelerh tay"pls ki yi hakuri kamar yadda na fada maki, bana so yaran nan su fahimci wani abu kwara mu rabu lafiya, ki daure idan muka shiga mota zamuyi magana, nayi maki alkawarin zan taimaka maki mu shawo kan shi"
A hankali Benazir ta share hawayen ta, har ga Allah bata son tafiya tabar gidan ji take kamar su kwana anan sai dai tasan ba abune mai yiwuwa ba.
Suna azaune jami'en da taj ya turo yayi masu sallama Yace su fito Yana jiran su.
Hankalin Unaisah ba karamin tashi yayi ba ganin za'a rabata da baby junaid, bawan Allah sai ƙara kankameta ya ke yi duk don kada su raba shi da ita, bayan sun fito abakin motar suka tsaya, Aneeleeh ta kar6i junaid yana kukan rabuwa da Angel tace mashi yai hakuri za ta zo har gida ta same shi, dakyar tayi mashi wayau ya hakura.
"Toh Mu zamu wuce, zamu tafi mu bar ku da kewar mu" Anila ta fada tana kallon su, duk sun ɗaure fuska saboda basu son su tafi
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Dan Allah yaushe zaku dawo"? Cikin sanyin murya batool ta yi maganar, Benazir tace"in dai mune kusha kuruminku, har sai kun gaji da ganinmu" dadine ya lullu6e su, miƙa masu hannu tay da sauri suka matsa kusa da ita ta haɗa su duka ta rungume su, Cikin kunne ta yi ma Unaisah raɗa"zan kar6i contact dinki a gurin Aneelerh, Ki kula min da kanki, Ina kaunarki sosai" murmushi unaisah tasaki"nima zanyi kewarki mommyna"
Bayan sun raba jikin su daga na juna ta dubi Batool ta shafa gefen fuskarta da tafin hannun ta
"zanyi kewarki, Yau na fara ganinki amma kin kwanta min araina, kamar yadda Babyna ta sace zuciyata, Ina kaunarki, Ki kula min da kanki" dariyar farin ciki batool tayi"in sha Allah, nagode sosai aunty Benazir, nima ina sonki, " taso ta tambaye su dr shureim amma saita kasa saboda kunyarta da take ji.
Miƙa masu hannu Aneelerh tay, itama tay hugging dinsu baby junaid ya haɗe rai Idanunshi sun ciko tab da kwalla.
Sumbatar kumatun shi Unaisah tay, cikin sigar lallashi tace"I'm sorry my little bro, Zanzo har gidan ku, Aunty aneelerh pls ki kwantar masa da hankali bana so yayi kukan rashi na" ta fada tana kallon fuskar junaid
"Kada ki damu bazan bari yai kuka ba, ku gaida mana mutanan gidan" atare suka amsa masu da toh
Akan idonsu Motar su ta fuce daga gidan, fitar su keda wuya Ummi ta fito daga kofar falon har bayan motar saida ta gani yayin da take karasa fucewa daga gate din
Sun yi tsaye cike da jimamin tafiyar su, baby junaid Ya tsaya masu aransu.
Kwata kwata basu lura da ummi ba har saida ta ambaci sunayen su da sauri suka dube ta
"Daga ina kuke? Motar waye naga ta fita yanzu? Kallon ta su ka yi ba tare da sun furta kalma ba
"Ba ku ji Ina magana bane"?
Ajiyar zuciya suka sauke atare Unaisah tace"bamu san motar wanane ba, muma yanzu muka fito"
"Daga ina"? Kallon juna su ka yi
"Kamar baku da gaskiya, ku fada min mana daga ina kuke" ta fada tana jifansu da kallon tuhuma.
"Mun je part din daddyna ne, daga can muke" ba dan ta yarda da su ba tace"shine ko ku fadamin ay dana shirya mun je tare, gaskiya baku kyauta min ba" ta fada tana jifar su da harara dariya sukai atare..
"Ku wuce mu shiga ciki," gaba tay suka bi bayan ta hannun su ruke cikin na juna
*💋BOSS BATURE✊*
Da marece tana a zaune gaban mirror chair tana yin wani makeup ɗin akan fuskarta, saboda kwalliyar da ta yi ɗazu ta goge.
gown ɗin ɗazu ce a jikinta da alama bata gama gayun ba, ko kuma wanda akayi dominsa bai gani ba, ita kaɗai ce a ɗakin, sai ƴan shafe shafe take ma fuskarta, cikin ƙanƙanin lokaci ta gama tayi matuƙar yin kyau, ta nutsu tana kallon fuskarta ta cikin mirror, pink lips dinta sun jiƙu da lip gloss sai shinning su ke.
Knocking ɗin kofar da akai ne Yasa ta ɗan juya ta kalli room door ɗin su.
Jemimah ce ta shigo jikinta sanye da Overall, ta ɗaure blonde hair ɗinta da ribbon ta fito ɗass Farar fatar ta gwanin sha'awa.
"Little Sis halan dalili ne Ya shigo dake dakin mu"?
Ta faɗi hakanne don tasan bai wuci chocolate tazo roƙo a gurin ta ba.
murmushi tayi"Aunty ummi ce tace In kiraki, kizo mu yi dinner, in ba zaki ci ba sai mu cinye naki" dariya Unaisah tay"su acici mala'ikun tauna, Ku da baku gajiya da Cin abinci, Har wani fadi kike zaku cinye abinci na ai ko dana karanta maku Charman dudu cikin kowa ya kumbure"
waro idanu Jemaimah tay"Wlh wasa nake maki fa" miƙewa Unaisha tay daga kan chair din"oho in ma dagaske ne bismillah, ku ci ku ga abun da zai biyo baya"