Sashe 29
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Inaso ne nasan me yakamata mu fara yi don tallafa ma rayuwar ki, ko ba haka ba" cike da rashin fahimtar kalamansa take duben shi, Hajiya malikat dake kallon ta murmushi ne dauke akan fuskarta, yarinyar ta kwanta mata aranta.
Chief owais ya nutsu yana sauraron su.
"Aure ko karatu wanne kika fi so a yanzu" waro mashi gray eyes dinta tayi da sauri ta sanya tafin hannu ta rufe fuskarta alamar taji kunya, hakan da tayi ba karamin dariya ya basu ba, hatta chief saida yayi murmushin gefen fuska.
Hankalin batool gaba ɗaya baya akansu tun da ta samu abinci take ta aikin ci.
"Kinyi shiru baki ban amsa ba" ya ƙara tambayarta, ƙasa ƙasa da murya chief ya furta"dad..." dakatar da shi daddy sharafudeen yayi"no kada ka shiga tsakanina da surukata, baby Angel ke nake sauraro," tayi mamakin jin ya ambaci nickname dinta, ba tare data buɗe fuskarta ba tace"Aure zanyi kafin na cigaba da karatu"
Murmushin fuskarsa ne ya faɗaɗa da zolaya yace"ta kwana gidan sauƙi, yanzu faɗa min kina da saurayin da zaki aura ne ko babu"
da sauri hajiya malika tace"haba dan Allah, kabarta mana, miji ay ta riga da ta samu ko ba haka unaisa"? Ɗaga mata kai tay alamarh.
Duk wannan abun dake faruwa a tsakanin daddy sharafudeen da Unaisah akan idanun Nazli wadda tuni tagama cika ta batse ranta yayi mugun 6aci tamkar ta ɗaura hannu bisa kai tayi ihu, wani irin kishine Ya ziyarce ta ganin yadda chief owais yayi zaman shi a wurin yarinyar, tun zuwan su hall din bai tako yazo inda take ba, kamar ma baisan da zamanta ba.....
Bazata juri kallon su ba, miƙewa tayi da niyar tabar hall din kamar daga sama muryar Faryat ta katse mata hanzarinta.
"sister Nazli, Ina zaki je ne bayan ba'a kammala taron ba"!
Ba tare da ta kalli faryat ba tace"bazan juri zama ba, sai nake ga kamar ba don mu aka shirya dinner din nan ba, because everyone's attention is focused on them. Daddy Ya tafi da wani wanda bamusan wanene shi ba and the chief is only paying attention to that girl." ta faɗa tana nuna saitin inda unaisah ta ke da hannun ta.
Ruƙo hannunta faryat tayi a cikin nata" Sister, ba ke ya kamata ki bar hall din ba! They are the ones who should leaves"
Girgiza kai Nazli tayi"no ni bana son hatsaniya, barina shi yafi min kwanciyar hankali"
Ta faɗa tana kokarin kaucewa rukon da faryat tayi mata.
Sai dai taki bata damar tafiya
"Nasan menene ya 6ata maki rai sister, ba ke kaɗai ba, mu ma ran mu ya 6aci da zuwansu saboda babu alkhairi atattare dasu, gaba ɗaya hankali Ya koma kansu, Amma ni na maki alkawarin zan kawar da yarinyar can daga hall din nan, indai hakan zai kwantar maki da hankalin ki, amma bai kamata ki tafi ba, ba zamu ji dadi ba" shiru Nazli tayi na ɗan wani lokaci kafin ta ɗan sauke ajiyar zuciya.
"What are you going to do to her I hope you won't hurt her."?
Shu'umin murmushi faryat tasaki,
"Don't worry sister, I won't hurt her. I'll just keep her out of sight until the dinner is over."
"Bana so a samu matsala faryat!"
'kawai kibar komai a hannu na, abun da nake so dake da zarar kinga babu yarinyar kiyi kokarin jan hankalin Yaya owais"
A hankali Ta furta Okey, fasa fita tayi da sauri ta juya ta koma wurin zaman ta.
Faryat kuwa ba karamin dadi taji ba, dama ta tsani ganin unaisah, tun farkon shigowarsu taji bata yi mata ba, da sauri ta koma wurin su Yusra tana jiran ta samu damar da zata aiwatar da mummunan kudurin ta........
Bayan kammala cin abinci, Mc Ya Kira su ɗaya bayan ɗaya suke hawa saman step suna taka rawa, sautin kiɗa Ya karaɗe ko'ina na hall din, Ta ko'ina hasken camera ne ke Ƙyalli, sai daukar hotuna sukeyi, abun ba karamin burge prisoners yayi ba, Ay tuni Sajeed Ya miƙe dama ta samu tun da ya shiga filin Ya fara taka rawa hankalin kowa ya dawo kan shi, harta su baba obie da suke atsaitsaye hankalin su na akan shi, abun a jininsa yake da zarar yaji kiɗa bai iya jurewa kamar ana kada mashi mazari, In har baiyi rawa ba hankali sa bazai kwanta ba, wakar da aka sanya tana ƙarewa wakar calm down ta shiga, aiko jiki har rawa yake yi su Parveen suka shiga fili suka dinga tikar rawa, gaba ɗaya suka ja hankulan mutanan hall din, sunyi matuƙar burgesu in ka cire su Yusra dake jin haushin su badan komai ba, sai dai saboda sun hana su rawar gaban hantsi, Hankalin unaisah ba karamin tashi yayi ba, ganin yadda suke rawa da alama sun manta a ina su ke ne, daga ita sai batul ne ba su shiga filin ba, Manyan mutanan dake a wurin ne suka soma yi masu liƙin kuɗi, tamkar ana yayyafa masu ruwan sama.
Hajiya turai da Hajjaty suma suka shiga filin suna tayasu yin rawar, kusan gaba ɗaya suka shiga cikin su, cikin raha da nishaɗi suka taka rawarsu.
Jemimah ta dage duk wanda ya lika mata kuɗi sai ta kwashe su ta tura a aljihun rigarta, ta tarasu dayawa har a hammata take saƙe wasu, tayi zaton abun wasan yara ne.
Mutanan dake harin Unaisah dama jira suke ta miƙe, a lokacin chief Owais Yabar wurin su, Ya tafi amsa kiran da akayi mashi awaya.
Miƙewa ta yi tana tafiya a hankali yayin da idanunta ke akan dance floor din, da alama itama so takeyi tayi rawar ta ɗan gagije jikinta.
"Baiwar Allah sannu" jin muryar mutun abayanta yasa tayi saurin dubanta, zahara ce fuskarta dauke da murmushi, Mayar mata da martanin murmushin unaisah tayi.
"Yawwa"
"Tun ɗazu nakeson yi maki magana ban samu damar yi ba, saboda mutanan da kike atare da su...." da ɗan mamaki take kallon bakuwar fuskar da tayi mata magana.
Miƙa mata hannu zahra tayi don su gaisa, A hankali unaisah ta ɗaura hannunta a cikin nata.
"Sunana zahra ke fa"?
"Unaisah"
"Banyi tunanin zakiyi saukin kai har haka ba,"
Murmushi unaisah tayi mata.
"meyasa kikace haka"?
"Raina ne ya bani haka" girgiza kai unaisah tayi
"Kin burge ni, idan badamuwa inaso muyi hoto a tare"
Bata kawo komai aranta ba, ta amince ma zahra.
Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin curo wayarta daga cikin yar purse dinta, ta dinga daukar su hoto da unaisah, A kalla zahara ta dauki hoto sama ashirin, Tsabar iyayi na zahra harda rungumeta sukayi hoto amanne da juna kamar kanwarta....
"Kinga yanzu na samu wanda zan dinga kallo awayana," ta faɗa bayan sun gama
"Ko zan iya samun layin wayarki? Ina so mu dinga gaisawa.
"Ban haddace number dina ba, kuma wayar bata a hannuna"
Shafa gefen fuskarta zahra tayi"ba damuwa, ay ina zuwa estate din nan zamu dinga haduwa...." wayar zahra ce ta soma ringing da ɗan sauri tace ma unaisah yanzu zan dawo ana kirana" amsa mata tayi da toh, har zahra tabar wajen Unaisah bata daina bin bayanta da kallo ba, hakanan taji ta burgeta, aranta ta ayyana wato duk yadda wani yaƙi ka, to wani zai so ka ne.
Murmushi tayi, tare da juyawa da niyar tabar wurin cikin rashin sa'a ta bange ɗaya daga cikin servers din dake safa da marwa wurin raba abinci, Gaba ɗaya tray din lemun da matar ta ɗauko ya 6are a jikin abaya dinta, glass cups din suka rikito kan floor, hankalin ba karamin tashi yayi ba ganin ta 6ata mata wankanta don ma Allah yasa rigar baka ce
Muryar matar na rawa ta soma bata hakuri.
Shiru unaisah tayi tamkar bazata tanka mata ba tace"bakomai, ay ba laifin ki bane, Ni ce na bangaje ki, bansan da mutun abayana ba"
A ruɗe matar tace"akwai rest room ki zo muje ki wanke rigarki please, idan ba haka ba za'a hukunta ni ne idan wani yaga ruwan lemun nan a jikin rigar ki"
Girgiza kai unasah tayi"a'a bani buƙatar zuwa, Ki tafi kawai, ay rigar baka ce babu wanda zai gani"
Magiya matar tadinga yi mata akan tazo su tafi ta wanke mata rigarta, ganin tasa naci ne yasa ta amince mata, da sauri matar ta zukunna ta kwashe glasses din ta mayar a tray, kafin ta juya Tayi gaba unaisah tabi bayanta, babu wanda ya lura da abun da ya faru saboda sautin kiɗan daya karaɗe hall din hankalin kowa na akan dance floor,.
Wani corridor suka shiga a inda jerin rest rooms din suke ta nuna mata ɗaya daga cikin su, ki shiga zan jira ki anan" amsa mata tayi da toh.
Unaisah kamar kada ta shiga haka take ji saboda hankalin ta bai kwanta da matar ba, buɗe kofar tayi shigarta ke da wuya taji alamun an datse ƙofar, sai dai ranta bai kawo mata komai ba, agaban sink ta tsaya ta kunna tap ruwa ya shiga karanyowa ta soma wanke inda lemun ya 6ata, bayan ta gama ta tsaya tana kallon fuskarta ta cikin mirror bakomai take tunawa ba face fuskar chief Owais hakika Yaja hankalin ta, musamman a lokacin da aka so aci mutunci su ya kare masu martaban su,
Murmushi tasaki har dimple din ta ya lotsa, can kuma ta juya akalar tunanin nata ga garkuwarsu, tasan duk inda yake ayanzu yana cikin koshin lafiya don ta fahimci prime minister ba karamin kaunarsa yake yi ba, tabbas zataso taga yadda zai tarairaye shi.....
Chief owais ya nutsu yana sauraron su.
"Aure ko karatu wanne kika fi so a yanzu" waro mashi gray eyes dinta tayi da sauri ta sanya tafin hannu ta rufe fuskarta alamar taji kunya, hakan da tayi ba karamin dariya ya basu ba, hatta chief saida yayi murmushin gefen fuska.
Hankalin batool gaba ɗaya baya akansu tun da ta samu abinci take ta aikin ci.
"Kinyi shiru baki ban amsa ba" ya ƙara tambayarta, ƙasa ƙasa da murya chief ya furta"dad..." dakatar da shi daddy sharafudeen yayi"no kada ka shiga tsakanina da surukata, baby Angel ke nake sauraro," tayi mamakin jin ya ambaci nickname dinta, ba tare data buɗe fuskarta ba tace"Aure zanyi kafin na cigaba da karatu"
Murmushin fuskarsa ne ya faɗaɗa da zolaya yace"ta kwana gidan sauƙi, yanzu faɗa min kina da saurayin da zaki aura ne ko babu"
da sauri hajiya malika tace"haba dan Allah, kabarta mana, miji ay ta riga da ta samu ko ba haka unaisa"? Ɗaga mata kai tay alamarh.
Duk wannan abun dake faruwa a tsakanin daddy sharafudeen da Unaisah akan idanun Nazli wadda tuni tagama cika ta batse ranta yayi mugun 6aci tamkar ta ɗaura hannu bisa kai tayi ihu, wani irin kishine Ya ziyarce ta ganin yadda chief owais yayi zaman shi a wurin yarinyar, tun zuwan su hall din bai tako yazo inda take ba, kamar ma baisan da zamanta ba.....
Bazata juri kallon su ba, miƙewa tayi da niyar tabar hall din kamar daga sama muryar Faryat ta katse mata hanzarinta.
"sister Nazli, Ina zaki je ne bayan ba'a kammala taron ba"!
Ba tare da ta kalli faryat ba tace"bazan juri zama ba, sai nake ga kamar ba don mu aka shirya dinner din nan ba, because everyone's attention is focused on them. Daddy Ya tafi da wani wanda bamusan wanene shi ba and the chief is only paying attention to that girl." ta faɗa tana nuna saitin inda unaisah ta ke da hannun ta.
Ruƙo hannunta faryat tayi a cikin nata" Sister, ba ke ya kamata ki bar hall din ba! They are the ones who should leaves"
Girgiza kai Nazli tayi"no ni bana son hatsaniya, barina shi yafi min kwanciyar hankali"
Ta faɗa tana kokarin kaucewa rukon da faryat tayi mata.
Sai dai taki bata damar tafiya
"Nasan menene ya 6ata maki rai sister, ba ke kaɗai ba, mu ma ran mu ya 6aci da zuwansu saboda babu alkhairi atattare dasu, gaba ɗaya hankali Ya koma kansu, Amma ni na maki alkawarin zan kawar da yarinyar can daga hall din nan, indai hakan zai kwantar maki da hankalin ki, amma bai kamata ki tafi ba, ba zamu ji dadi ba" shiru Nazli tayi na ɗan wani lokaci kafin ta ɗan sauke ajiyar zuciya.
"What are you going to do to her I hope you won't hurt her."?
Shu'umin murmushi faryat tasaki,
"Don't worry sister, I won't hurt her. I'll just keep her out of sight until the dinner is over."
"Bana so a samu matsala faryat!"
'kawai kibar komai a hannu na, abun da nake so dake da zarar kinga babu yarinyar kiyi kokarin jan hankalin Yaya owais"
A hankali Ta furta Okey, fasa fita tayi da sauri ta juya ta koma wurin zaman ta.
Faryat kuwa ba karamin dadi taji ba, dama ta tsani ganin unaisah, tun farkon shigowarsu taji bata yi mata ba, da sauri ta koma wurin su Yusra tana jiran ta samu damar da zata aiwatar da mummunan kudurin ta........
Bayan kammala cin abinci, Mc Ya Kira su ɗaya bayan ɗaya suke hawa saman step suna taka rawa, sautin kiɗa Ya karaɗe ko'ina na hall din, Ta ko'ina hasken camera ne ke Ƙyalli, sai daukar hotuna sukeyi, abun ba karamin burge prisoners yayi ba, Ay tuni Sajeed Ya miƙe dama ta samu tun da ya shiga filin Ya fara taka rawa hankalin kowa ya dawo kan shi, harta su baba obie da suke atsaitsaye hankalin su na akan shi, abun a jininsa yake da zarar yaji kiɗa bai iya jurewa kamar ana kada mashi mazari, In har baiyi rawa ba hankali sa bazai kwanta ba, wakar da aka sanya tana ƙarewa wakar calm down ta shiga, aiko jiki har rawa yake yi su Parveen suka shiga fili suka dinga tikar rawa, gaba ɗaya suka ja hankulan mutanan hall din, sunyi matuƙar burgesu in ka cire su Yusra dake jin haushin su badan komai ba, sai dai saboda sun hana su rawar gaban hantsi, Hankalin unaisah ba karamin tashi yayi ba, ganin yadda suke rawa da alama sun manta a ina su ke ne, daga ita sai batul ne ba su shiga filin ba, Manyan mutanan dake a wurin ne suka soma yi masu liƙin kuɗi, tamkar ana yayyafa masu ruwan sama.
Hajiya turai da Hajjaty suma suka shiga filin suna tayasu yin rawar, kusan gaba ɗaya suka shiga cikin su, cikin raha da nishaɗi suka taka rawarsu.
Jemimah ta dage duk wanda ya lika mata kuɗi sai ta kwashe su ta tura a aljihun rigarta, ta tarasu dayawa har a hammata take saƙe wasu, tayi zaton abun wasan yara ne.
Mutanan dake harin Unaisah dama jira suke ta miƙe, a lokacin chief Owais Yabar wurin su, Ya tafi amsa kiran da akayi mashi awaya.
Miƙewa ta yi tana tafiya a hankali yayin da idanunta ke akan dance floor din, da alama itama so takeyi tayi rawar ta ɗan gagije jikinta.
"Baiwar Allah sannu" jin muryar mutun abayanta yasa tayi saurin dubanta, zahara ce fuskarta dauke da murmushi, Mayar mata da martanin murmushin unaisah tayi.
"Yawwa"
"Tun ɗazu nakeson yi maki magana ban samu damar yi ba, saboda mutanan da kike atare da su...." da ɗan mamaki take kallon bakuwar fuskar da tayi mata magana.
Miƙa mata hannu zahra tayi don su gaisa, A hankali unaisah ta ɗaura hannunta a cikin nata.
"Sunana zahra ke fa"?
"Unaisah"
"Banyi tunanin zakiyi saukin kai har haka ba,"
Murmushi unaisah tayi mata.
"meyasa kikace haka"?
"Raina ne ya bani haka" girgiza kai unaisah tayi
"Kin burge ni, idan badamuwa inaso muyi hoto a tare"
Bata kawo komai aranta ba, ta amince ma zahra.
Yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin curo wayarta daga cikin yar purse dinta, ta dinga daukar su hoto da unaisah, A kalla zahara ta dauki hoto sama ashirin, Tsabar iyayi na zahra harda rungumeta sukayi hoto amanne da juna kamar kanwarta....
"Kinga yanzu na samu wanda zan dinga kallo awayana," ta faɗa bayan sun gama
"Ko zan iya samun layin wayarki? Ina so mu dinga gaisawa.
"Ban haddace number dina ba, kuma wayar bata a hannuna"
Shafa gefen fuskarta zahra tayi"ba damuwa, ay ina zuwa estate din nan zamu dinga haduwa...." wayar zahra ce ta soma ringing da ɗan sauri tace ma unaisah yanzu zan dawo ana kirana" amsa mata tayi da toh, har zahra tabar wajen Unaisah bata daina bin bayanta da kallo ba, hakanan taji ta burgeta, aranta ta ayyana wato duk yadda wani yaƙi ka, to wani zai so ka ne.
Murmushi tayi, tare da juyawa da niyar tabar wurin cikin rashin sa'a ta bange ɗaya daga cikin servers din dake safa da marwa wurin raba abinci, Gaba ɗaya tray din lemun da matar ta ɗauko ya 6are a jikin abaya dinta, glass cups din suka rikito kan floor, hankalin ba karamin tashi yayi ba ganin ta 6ata mata wankanta don ma Allah yasa rigar baka ce
Muryar matar na rawa ta soma bata hakuri.
Shiru unaisah tayi tamkar bazata tanka mata ba tace"bakomai, ay ba laifin ki bane, Ni ce na bangaje ki, bansan da mutun abayana ba"
A ruɗe matar tace"akwai rest room ki zo muje ki wanke rigarki please, idan ba haka ba za'a hukunta ni ne idan wani yaga ruwan lemun nan a jikin rigar ki"
Girgiza kai unasah tayi"a'a bani buƙatar zuwa, Ki tafi kawai, ay rigar baka ce babu wanda zai gani"
Magiya matar tadinga yi mata akan tazo su tafi ta wanke mata rigarta, ganin tasa naci ne yasa ta amince mata, da sauri matar ta zukunna ta kwashe glasses din ta mayar a tray, kafin ta juya Tayi gaba unaisah tabi bayanta, babu wanda ya lura da abun da ya faru saboda sautin kiɗan daya karaɗe hall din hankalin kowa na akan dance floor,.
Wani corridor suka shiga a inda jerin rest rooms din suke ta nuna mata ɗaya daga cikin su, ki shiga zan jira ki anan" amsa mata tayi da toh.
Unaisah kamar kada ta shiga haka take ji saboda hankalin ta bai kwanta da matar ba, buɗe kofar tayi shigarta ke da wuya taji alamun an datse ƙofar, sai dai ranta bai kawo mata komai ba, agaban sink ta tsaya ta kunna tap ruwa ya shiga karanyowa ta soma wanke inda lemun ya 6ata, bayan ta gama ta tsaya tana kallon fuskarta ta cikin mirror bakomai take tunawa ba face fuskar chief Owais hakika Yaja hankalin ta, musamman a lokacin da aka so aci mutunci su ya kare masu martaban su,
Murmushi tasaki har dimple din ta ya lotsa, can kuma ta juya akalar tunanin nata ga garkuwarsu, tasan duk inda yake ayanzu yana cikin koshin lafiya don ta fahimci prime minister ba karamin kaunarsa yake yi ba, tabbas zataso taga yadda zai tarairaye shi.....