← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 142 OF 238

Sashe 142

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

gaba ɗaya jikinsu Ya mutu, wata irin kasalace ta mamaye sassan jikinsu, hatta yanayin bugun zuciyar su saida Ya canza.

Kasa ƙarasa cin abincin ta yi A hankali Ta jingina bayanta jikin kujerar batare da ta daina kallon shi ba, waƙar ba karamin shagalar da su tayi ba, sun shagala da kallon juna, sun kasa ta6uka komai, kowa na cin abinci ban da su..."

Cigaba waka tay sun nutsu suna sauraran baitin

Dani dake soyayya ta ginu

A zuciya ta ke na saka kin sanu

Kice dani kin barni na banu

Shine kadai zai sanya ayi mini duren kunu

Kiji ni dai zama dake daram dam-dam

Na rike ki ta kam kam-kam

Makiyan mu suje chan

Banda son ki bansan komai ba...

Lumshe idanunta ta yi a hankali ta dan numfasa ba tare da buɗe idanun ba, wani irin bakon abu take ji a jikin ta, mara misaltuwa, sai taji tamkar saboda su aka yi waƙar saboda yadda wakar take shigarta.

yatsun hannunta sai kerma suke, gaba ɗaya ta shiga yanayi ba zata iya jurar cigaba da kallon shi ba.

Danish dake kallonta wata irin nutsuwa ce ke shigar shi, musamman data rufe idanunta hakan ya bashi damar kallon ta son ran shi, farar fatar dogon wuyanta yabi da kallo Silver necklace ɗin data sanya tayi matuƙar ƙawata wuyanta, moving eyes dinsa yai slowly izuwa kan kirjin ta sam ta manta bata ɗaure boobs ɗinta ta ciki ba kamar yadda ta sa6a, yau yaga abun da take boye mashi, duk da ƙarantar su nipples dinta ba karamin girma ne da su ba.

hannun shi na dan kerma ya dauki milkshake din data ajiye mashi ya fara shan shi ba dan yana jin dadin shi ba, saboda kallonta da ya ke yi yafi mashi komai.

Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko  Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
baitin Wakar ne Ya ƙara rikirkita tunanin shi ya ɗan runtse idanun shi yana sauraron daddadar muryar da kunnuwan shi ke jiyo mashi sai yaji kamar Angel dinsa ce ke raira mashi ita.

Na rike ka hannu biyu baby na

Kai kazam fitila annuri na

Ko ana fizgemin nama na

Zan yabe ka da karfin harshe na

Sai da kai

Ba ya kai

Ka sarkafe mini a zuciya ta

Ba ya kai

Ummi tasan takan tsiya, dagangan take maimaita wakar saboda ta ƙara rikitar da su, yau taga abun da Ya ɗaure mata kai, tun daga kan yanayinsu ta fahimci irin tsantsar kaunar da suke ma junan su, don ita abun da tagani ma ya wuce A kira shi da so hada shaukin junansu da suke ji, yar wakar da ta kunna masu kadai ta jefa su awani hali dama da biyu ta kunna ta

Kasa jurewa yayi da wata irin kasala Ya miƙe zai bar dining din gudun kada yayi wani abu ba dai dai ba da zaisa su sake samun sabani da ita, da sauri ummi ta dakatar da wakar ta dube shi.

"Danish Ina zakaje? Naga ko abincin baka fara ci ba" tamkar baisan furta magana yace"bana jin yunwa" marairaice mashi fuska su Haris sukayi"pls danish, kada ka tafi ka zauna ka ci abinci" girgiza kai yai, Shi kadai yasan me yake ji ajikin shi, In har ya cigaba da zama Yana kallon Unaisah komai zai iya faruwa a yanzu haka jikin shi sharkaf Yake Ga gumi da ya wanke shi duk da sanyin a.c din dake a dining room din, su basu lura ba amma ita Ummi tasan me yake ji a wayance tace"ko dai kana da uziri ne"? ya ɗaga mata kai alamar eh.

Shu'umun murmushi Tasaki Okay, Muna jiranka idan ka gama uzirin naka, ka dawo kaci abincin" bai kula ta ba Ya fuce daga dinning din ba don ya gaji da zaman shi ba, sai don bayason yaja ma kan shi bala'e.   

Fitarshi keda wuya Unaisah ta buɗe idanunta da suka kaɗa jawur da su, ga wani zafi da temperature din jikinta ya dauka kamar mai fama da zazzabi.

ta rasa gane meke mata dadi, fitar Danish daga ɗakin yasa taji batasan cin komai, mineral water kadai ta sha ta miƙe jikinta na tsuma ta nufi hanyar fita daga dakin muryar aunty Ummi ta katse ta"Wai lafiya? Shi ya fita baici komai ba, kema kin miƙe zaki fita? Meke damunku ne"? Ta tambaya kamar batasan meke wakana ba.

Yamutsa fuska Unaisah tay tare da kallon Ummi datay maganar

"Wayata zan dauko adaki, yanzu zan dawo" ta fadi hakanne don kada su zargi wani abu.

kumshe dariya ummi ta yi abakinta, tana lura da yadda jikinta ke tsuma.

"Okay, muna jiranki" fucewa tayi daga dining din tana tafiya da nawa kamar wadda kwai ya fashe mawa, tana shiga dakin su ta faɗa toilet taja ƙofa ta datse, zama tay akan toilet seat tayi shiru tana tariyo abunda ya faru a dining room.

Ta rasa gane dalilin dayasa take tsintar kanta awani yanayi duk idan tagan shi ko taji muryarshi! Batasan menene ba, ta kasa ganewa.

bata gama zancen zucin ba, zatayi tsarkin fitsarin da tayi taga wannan farin ruwan mai yauƙi wani irin kyankyami da kyamane suka kamata, da sauri tayi tsarkin ta fito ta tsaya abakin kofar toilet tana faman sauke ajiyar zuciya, bayanin aunty Umminsu ta fara tariyowa a lokacin da take faɗa mata dalilin dake kawo shi, abun da ya daure mata kai kallon juna kawai sukayi ba wani abu ba amma sai gashi ta gan shi, dole ta nemi ƙarin bayani agurin Aunty ummin su.

Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko  Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
ga yunwa tana ji sai dai bata jin zata iya komawa dining room din, faɗawa tayi kan bedmattress ta janyo pillow ta rungume shi a kirjinta, wani sanyine ke ratsa zuciyarta, ga wani dadi da take ji a jikin ta.

ta shafe tsawon mintuna shabiyar a kwance ba tare data motsa ba.

"Sister, Aunty Ummi tace kizo wai" muryar hawwa ce ta katse mata zancen zucin ta, ba tare da ta bude idanunta ba tace"okay, gani nan zuwa" bayan fitar hawwa daga dakin ta sauko daga kan gadon ta, ta gyara mayafinta, tana ƙokarin fitowa daga dakin kamar daga sama taji Sallamar Salsabeel da sauri ta juya ta dubi kofar falon, a tsaye yake ya ɗauki wankan shadda kamar ba shi ba, hannun shi ruƙe da trolley, kwata kwata bai lura da ita ba.

"Yaya salsabeel," muryar ta ce ta fargar da shi, murmushi yayi tare da nufarta yana jan trolley ɗin.

"Unaisah ykk"

da fara'a tace"lafiyalou, ya salsabeel kwana biyu baka leko mu ba, munyi fushi" 

ta fada tana haɗe fuska yar dariya yayi"i'm really sorry, wlh kuna araina, yanzu hakama da kika ganni saboda ku nazo"

 Miƙa mashi hannu tayi"kawo na ruƙe maka trolly din" miƙa mata yai tasa hannu ta ruƙe handle din"Menene aciki? Ko kayanka ne"? Girgiza kai yai" mu karasa ciki, zan nuna maki abunda ke a cikin shi" amsa mashi tayi da toh suka nufi cikin falon akan sofa Ya zauna, Ta aje trolley din agaban shi Yace mata ta kira sauran yan uwanta ya faɗa yana hangen su a dining room suna cin abinci sam basu lura da shi ba, da sauri ta juya ta nufi dining room din ta shiga ta kira su, tun da suka ji ta ambaci ya salsabeel ya zo kowa ya ajiye spoon din hannun shi, Cike da zumudin son ganin shi suka fito daga dakin su dukan su hada Ummi.

Kafin su karaso ya mike fuskanshi dauke da fara'a ya gaishe da ummi ta amsa mashi da fara'arta,  kallon su Haris yayi daya bayan ɗaya aranshi yana tariyo lokacin da suke a prison, rayuwa ta canza sun wadatu da kwanciyar hankali

Hannu ya miƙa ma mazan sukayi musaba, Ya dubi Yan matan dake ta faman hade rai

Dariya yayi"fushi kuke dani"? Khadeeja tace"eh mana, tun yaushe rabon da kazo gurin mu, ka manta damu.."

Mubeen Yace"kullum sai munsa ran zuwanka amma saika ki zuwa"

gaba daya suka rufe shi da korafe korafen su dakyar Ya samu ya shawo kan su, har suka hakura da fushin da sukeyi da shi bayan sun gama gaisawa da junansu yace su zauna zasuyi magana mai muhimman ci.

Bayan Kowan nan su Ya samu guri Ya zauna kan Sofas suka nutsu suna jiran jin me zaice masu.

"Ya salsabeel, Wannan akwatin fa? Ko tsaraba ne ka kawo mana" parveen ce tay maganar tare da nuna akwatin da hannu

"Eh tsaraba ce amma bata abun ci ba, Kayan sawa ne" kallon juna su kayi da mamaki akan fuskokin su.

"Ina Danish"? Ya tambaya yana kallon su

"Yana a daki" suka haɗa baki gurin bashi amsa"

Yace"okay, wani ya kira min shi" Haris ne Ya mike da sauri Ya je kiran shi.

falon yayi tsit baka jin hayaniyar komai, duk sun ƙagara da son ganin menene acikin trolly din me kuma ya Salsabeel zai fada masu mai mahimman ci'? 

Jim kaɗan saiga Haris Ya dawo tare da Danish, Har ya canza kayan jikin shi yanzu silk pyjama ne a jikin shi na bacci.

Tun shigowarsu Falon, Unaisah take satar kallon shi, bayan sun rungume juna da salsabeel a amutunce suka gaisa da junan su kafin daga bisani kowan nan su Ya zauna suka nutsu suna kallon salsabeel

Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko  Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Mu farayiwa Annabi salati" suka amsa mashi da toh, bayan sun gama yayi shiru yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya kamar mai nazarin wani abu, Azeeza da Jemimah sai faman kumshe dariya su ke yi kamar wasu zautattu.

Ɗaya bayan ɗaya ya fara kiran sunayen su, duk wanda ya kira sunan shi sai ya amsa mashi da Na'am, ummi dai tayi shiru tana jiran jin me zaice ma su

Numfasawa yayi kafin ya fara magana cikin nutsuwa

"Gobe Idan Allah Ya kaimu da rai da lafiya, za'a tafi daku Isod headquarter...." 
Chapter 142 · 0% Book details