← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 126 OF 238

Sashe 126

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Takun Ƙarshe
Shigowa dakin hajjaty yayi bakin shi dauke da sallama, tsayawa yayi ganin bata a cikin ɗakin har ya juya zai fita ya jiyo saukar ruwa a toilet, ajiyar zuciya ya ɗan sauke ya nufi gefen gadon ta har ya yunkura zai zauna idanunsa suka hango mashi plastic bottles dake ajiye kan mirror drawer, miƙewa yayi tare da nifar mirror din ya tsaya yana kallon robobin kamar na ruwa haka suke, rubutun larabci ya gani a jikin su baisan me aka rubuta ba saboda baya jin harshen, zuciyar shi bata kwanta da su ba, ɗaya ya ɗauka ya buɗe murfin ta yakai hancin shi zai shinshina da sauri ya kawar da shi gefe ya yamutsa fuska haɗi da ta6e baki yana ɗan jan numfashi..

Motsin buɗe kofar toilet ne yaja hankalin shi ga kallon ta, fitowa tayi daga ciki, tayi ɗaurin gaba da towel, ta naɗe black hair din ta da wani towel ɗin

Suna haɗa ido da juna ta sakar mashi murmushi.

"mere pyaar, sai yanzu zan sanyaka a idanuna? Ina ka shiga ne ka barni da kewarka"?

Lumshe idanun shi yayi a hankali ya buɗe su yana bin ta da kallo mai cike da jin shaukin ta.

Ta baya tayi hugging din shi ta kwantar da kanta saman shoulder dinsa, ta ɗaura hannayenta kan chest din shi.

"Wifey, i'm sorry wani kira akai min mai mahimmanci shiyasa ban samu damar zuwa gurin ki ba, amma kina araina" kwanto da kanta tayi kan shoulder din shi, nuna mata robar hannun shi yayi"menene wannan?

Fuskarta dauke da murmushi tace"maganin da sheikh imam Ya bada ne don adinga ba marwa tana sha, yace in sha Allah zataji sauƙi nan bada jimawa ba..." ta fada tare da manna mashi kiss kan cheek dinsa, gogan ya haɗe fuska sam bata kula da yanayin shi ba, taci gaba da cewa"

"Nayi ma sheikh imam alkawarin zancigaba da kula da ita, har zuwa lokacin da zata ji sauƙi"

ajiye robar yayi tare da janyota ta dawo ta gaban shi

Saurari Littafin Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.

"Meye alakarki da marwa ne"? Fuskar shi adaure yayi mata maganar

"Yar uwata ce musulma, kuma tana bukatar taimakonmu saboda mune danginta ayanzu..." bata ƙare maganar ba ya rufe mata baki da yatsan shi

Calmy yace "Kingane ni bazan hanaki yin aikin lada ba, kawai bana so kina shisshige mata ne, ke ko kyamarta ba ki ji? kuma baki gudun ta goga maki lalurarta"? Zame hannun shi tayi daga kan bakinta

"Haba pravin, meya kawo wannan maganar? Ita ma fa ba ita ta daura ma kanta ba, bayan haka sheikah imam ya fada mana hanyoyin da zamu kare kanmu daga sharrin aljanu...." bata ƙare maganar ba yai saurin janyota kan kirjinshi yakai bakin shi saitin kunnanta, in a low voice ya furta"ni dai hankalina bai kwanta ba, kinsan bana son duk wani abu da zai cutar min dake, pls ki taimaka min ki aje aikin kula da marwa..." yanayin yadda yakeyi mata magana ba karamin kashe mata jiki yayi ba.

cike da shagwa6a tace"dan Allah kabarni inyi aikin nan, indai kayi imani da cewa Allah shi yake tsare bawansa, nayi maka alkawarin zan kula da kaina, amincewarka kadai nake bukata..."

Badan yaso ba ya amsa mata da toh.

ƙara matseta yayi a jikin shi, a hankali ya fara manna mata hot kisses kan wuyanta har ya zuwa kan kirjin ta..tuni ta fara jan numfashi tana lumshe idanunta, daukarta yai gaba ɗaya ya kwantar kan mattress ya zame kayan jikin shi ya rage daga shi sai short, ya fada kanta yaja bargo ya lullu6e su...romancing dinta ya cigaba da yi, gaba ɗaya ya rikitata, tsawon mintuna shabiyar kacal, wani irin kasalallan bacci ya yi awon gaba da hajjaty.

Fitowa pravin yayi daga cikin bargon ya sauko daga kan gadon Ya haɗa uban gumi a jikin shi, shu'umin murmushin gefen fuska ya saki tare da kallon hajjaty dake bacci...A hankali Ya furta"I'm sorry, zan yi maki laifi, saboda bazan bari kiyi silar tona min asirina ba," ya faɗa tare da juyawa ya nufi robobin maganin ya kwashe su, Ya shige toilet da su, Allah kadai Yasan meya yi masu, jim kaɗan Ya fito da robobin a hannun shi yana faman sakin shu'umun murmushi ya ɗaura su kan mirror.

Kafin ya fita daga dakin saida ya fara hawa gadon Ya sumbaci la66anta kafin ya sauko shaf shaf ya maida kayan jikin shi ya juya cikin takun tantirai Ya fuce daga dakin.

Fitar shi keda wuya hajjaty ta fara mutsu mutsun farkawa daga bacci, wata irin kasalace ta mamaye jikinta dakyar ta lalla6a ta miƙe ganin babu sutura ajikinta yasa tayi saurin kai hannu ta janyo towel dinta ta lullu6e jikinta, muryarta adisashe ta fara ambaton sunan shi shiru taji bai amsa mata ba alamar baya adakin, lumshe idanu tayi tare da jingina kanta jikin headboard, A hankali take tariyo abunda ya shiga tsakaninta da pravin wani irin shaukin son shi take ji, dai dai da minti ɗaya bata ta6a gajiya da shi ba, saboda soyayyar gaskiyace a tsakaninsu, bata ta6a haɗa son shi da wani ba.

Tunawa da marwa yasa tay saurin saukowa daga kan gadon ta shiga toilet, donta tsarkake jikin ta, bayan ta fito ta shirya cikin riga da skirt na atamfa ta feshe jikinta da turare, ta yafa mayafi akanta, da sauri ta dauki robobin maganin ta tura su cikin ledar da aka kawo su, ta fito ta nufi dakin marwa, da sallama ta shiga dakin fuskarta dauke da murmushi take kallon marwa dake akwance kan mattress ta rufe idanunta.

Zama hajjaty tay gefen katifar ta ajiye jakar agaban marwa.

"Sannu marwa ya jikin naki? a hankali ta buɗe idanunta waɗanda suka kaɗa jawur ta dubi hajjaty, dakyar ta kakaro murmushi tana kallon ta

tayi kyau abunta, ɗazu da safe hajjaty ta taimaka mata tay wanka har kaya ta canza yar doguwar rigace a jikin ta, jikinta sai kamshin turaren da hajjaty ta fesa mata yakeyi.

"Sheikh imam ya aiko da maganin ki,"

ta fada tare da ruƙo kafadun marwa ta taimaka mata ta zauna tare da jingina bayanta jikin pillow

"Kina jin yunwa" girgiza mata kai tay alamar a'a,

"Dama nasan ba lallai kiji yunwa ba, saboda dazu kin cika cikin ki da abinci" ta fada yayin da take bude murfin robar farko mai ɗauke da sunan zam zam..

"Kiyi bismilla ki sha, kur6a ɗaya zakiyi" ɗaga mata kai tay alamar toh

Lokacin data kurbi maganin kiris ya rage ta amayar da shi saboda zaurin da ya buso hancin ta.

Lura da yanayin ta yasa hajjaty cewa"am sorry halan maganin bai da dadi? Ɗaga mata kai tay alamar eh

Saurari Littafin Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Eyyah sai kin daure,kinsan yadda magungunan gargajiya suke akwai ɗaci, wani zakiji shi da bauri wani kuma tsami" ta faɗa tana yamutsa fuska, bayan ta kammala bata magungunan, tace"wannan ɗayan daya rage, a cikin ruwan wanka za'a ɗiga maki shi, zuwa anjima in sha Allah zan sake dawowa, sannan pls kada ki manta kiyi evening azhkar"

tun da ta fara magana marwa keta kallonta so take ta faɗa mata wani abu tarasa taya zatai mata magana daga ta yunkuro zatai magana sai ta kasa saboda muryarta babu dadin ji

Hajjaty sam bata lura da hakan ba, bayan ta maida robobin maganin a cikin ledar, ta ajiye gefen katifar marwa"ni zan tafi, da anjima zan shigo kawo maki dinner" ta fada tare da sakar mata murmushi ta mike ta tafara tafiya har ta kusa fita kunnuwanta suka jiyo mata marwa dake ta kokarin yi mata magana.

Juyowa tay tare da kallonta da alamun rudani akan fuskarta, da hannu take yi mata alama, hajjaty ta kasa gane me taje nufi, ita dai taga marwa sai nuna mata dunkulallun yatsun hannunta takeyi

"Marwa akwai wani abu da kike bukata ne"? Ɗaga mata kai tay alamar eh, komawa tayi gaban katifar ta zukunna tana kallonta, ruwan hawaye tagani kwance akan fuskarta"pls ki daina zubda hawayenki dan Allah, ki fadamun abunda kike so zanyi maki" da hannu marwa ta dinga goga floor tana kokarin kwatanta mata abunda take so ta dauko mata sai dai takasa fahimtarta

Saurari Littafin Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Marwa kiyi hakuri, wallahi bansan me kike nufi ba" buɗe baki marwa tayi ta fara mata gura gura.. tsoron maganarta hajjaty take ji nan take ta tuna da maganar pravin dayace mata ita bata tsoron marwa ta goga mata lalurarta, tuna wannan yasa tay saurin mikewa gabanta na faduwa ta fara ambaton sunan Allah acikin zuciyarta.

Cikin rawar murya tace"marwa sai anjima zan dawo in sha Allah" da sauri ta fuce daga dakin, marwa ta kifa kanta cikin pillow ta fashe da kuka mai tsuma zuciya tamkar ranta zai fita 💔

________________________________✍️

*(AFTER 3 DAYS BAYAN KWANA UKU)*

A kalla yau kwana uku kenan da zuwansu Anila gidan hajiya adama, har ila yau ba su ƙara jin duriyar Ana ba, babu ita babu labarin ta, abun ya ɗaga hankulan mutanan gidan sun damu da rashin ta, kusan kullum sai anila da mahboob sun kira layinta a switched off suke samun shi, Lamarin ya ɗaure masu kai, basu da wata hanya da zasu Iya tuntu6ar wani nata, saboda ba su ta6a kar6ar layin yan uwanta dake a joss ba, abu biyu ya haɗe ma Aneelerh ga damuwar halin da junaid yake a ciki, kwata kwata baya sakin jiki da kowa ga ƙiwuya bai yarda da kowa na gidan ita kadai yake manne mawa, kuma har yau yaƙi buɗe baki ya tanka mata ya zama kamar kurma sai dai yabi ta da ido ko in yana jin yunwa sometimes yana bude baki ya furta kalmar yunwa, wani abu daya fi daure mata kai idan dare yayi zasuyi bacci ta rungume shi a jikin ta, sai ya dinga firgita yana sambatu kwata kwata bata gane me yake cewa.
Chapter 126 · 0% Book details