← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 238

Sashe 27

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Abun da ɗaure kai, amma ya ya akai su ke bala'in kama har haka? Kamar an yi photo copy din fuskar Hateem, ko ma ince Nazli" his exellency Deen ne yayi maganar, Yazrin sam takasa samun nutsuwa Sai kallon shi take yi ko ƙyaftawa babu, wato danish ya girgiza su da kyawun shi, Hankulan su Faryat ya tashi haikam tsabar yadda su ke kallon shi kamar za su haɗiye shi, yadda kasan irin kura taga naman nan.

Haƙiƙa sun rudu da prisoners, babu wanda bai yi mamakin sanyin kyan su ba, da al'ajabin kamanceceniyar su da ƴan uwan su yadda kasan ya'yan cikin wasu daga cikin su tsabar yadda kamannin su ya bayyana da juna...

Ganin kallon nasu ba mai ƙarewa ba ne gashi sunbar yara atsaitsaye, da sauri Ziyad ya ce

"Lokaci yana tafiya, yakamata acigaba da shagali"

kafin Ya ƙare maganar sautin waƙa mai ratsa zuciya ya karaɗe cikin hall din, Ɗaya bayan ɗaya Suka juya suna nufar wurin zaman su kowa da abun da yake saƙawa a cikin zuciyar shi.

Hateem kamar jira yake yi a samu maslaha, jiki na rawa ya nufi danish ya ruƙo hannun shi acikin nashi, burin shi su haɗa ido don su kalli juna dakyau amma yaƙi bashi damar hakan, murmushi ne dauke akan fuskar sharafudeen sai faman kallon su ya ke yi, yaji dadin ganin hateem a irin wannan yanayin.

Da zolaya yace irin wannan kallo haka? Ka da fa ka lashe mana yaro" ƴar dariya hateem yayi,

Chief owais da ke kallon su ba karamin kwanciyar hankali ya samu ba ganin ya faranta ran uncle din sa

"Uncle ka tafi da shi, zaman shi anan bazai yiwu ba, saboda baya son hayaniya, kuma baya son ana kallon sa, From now until nightfall, I entrust him to your care" wani irin farin ciki ne ya ƙara lullu6e prime minister, kamar wanda akayima albishir da gidan Aljanna, cikin sanyin murya yake fadin"nagode owais, wlh ka gama min komai, bazan ta6a manta alkhairin ka a gare ni ba, Allah ya faranta maka kamar yadda ka faranta min" addu'o'i ya dinga zuba mashi, bai manta da sheikh imam ba wanda ke atsaye tun dazu murmushine akan fuskar shi.

"shukran jazeelan Ya sheikh, Allah ne kadai zai iya biyan ka, saboda babu wasu kalmomi da zan iya yin amfani da su wurin yi maka godiya" ya faɗa yana ruƙo hannun sheikh imam gaba ɗaya wani irin annurin farin ciki ne akan fuskokin su.

Unaisah da ke ta sauraron su aranta Allah Allah take Danish ya amince da buƙatar chief yabi prime minister don tasan halin shi da kafiya ba kowa ke iya tankwara shi ba.

Kafin ta ƙare zancen zucin nata ba, da mamaki taga danish yabi prime minister hannun su ruƙe cikin na juna suka nufi hanyar fita daga hall din ko irin ya waigo ya kalle su baiyi ba, ajiyar zuciya ta sauke, sarai ta fahimci masu satar kallon ta.

gimbiya mujeedat sai bin su da kallo take yi, tarasa ma wani irin tunani zatayi game da bawon Allan nan mai tsantsar kama da Nazli, kasa jurewa tayi da sauri ta bi bayan su, ita ma Yazrin ta bi su, Nazli ce kaɗai ba tayi yunkurin bin su ba, kwata kwata babu annuri akan fuskarta, Ita bakomai ne damuwarta ba face abu biyu, na farko yaron da ke kama da ita! arayuwarta ta tsani ace wani yana kama da ita, saboda izzarta, tafi so mai nata ya kasance ita kadai ke da shi, bayan wannan sai Unaisah! Hankalin ta bai kwanta da ita ba, saboda wani kallo da taga sun jefa wa juna a tsakanin ta da chief owais nan take taji bata son ganin yarinyar, Nazli tana da zafin kishi, izzarta ce ke hanata bayyanawa.

Fuskarta babu annuri ta kai hannu ta dauki wayarta dake kan floor, da wani irin takun qasaita ta juya tabar wurin su.

Mom turai da ke ta kallon su tun ɗazu take son tunkararsu ganin babu dama ne yasa ta yi shiru tana kallon badaƙalar da ake yi, yanzu kuwa da ta samu dama, Da sauri ta nufi wurin Azeeza saboda sun bata tausayi da suna kuka, hanky ta zaro daga purse dinta, ta zuƙunna agaban ta tare da sanya shi kan fuskarta ta shiga share mata hawaye

Cikin kulawa tace "Stop crying kin ji ko? everything is over now, we are welcoming you to our family" wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyoyinsu har sun fara ɗan sakin jikin su.

A hankali Sir mubarak Ya nufi Jemimah dake a maƙale da Angel ta cukuikuiye mata rigarta zukunna yayi agabanta, ya ruƙo hannayenta a cikin nashi yana rarrashinta ganin har yanzu tana shesshekar kuka.

"Sorry baby girl, share hawayen ki...."

muryarta na rawa ta furta"wlh baku son mu, shiyasa ku ke korar mu, ni dai gida zan koma Allah" a fadace ta faɗa tana faman zabga masu harara, ƴan kumatunta sunyi jawur da su.

Ba zato ba tsammani Taji Sir mubarak Ya dauketa dungurum Ya daurata kan kirjin shi, wuƙi wuƙi tayi da idanunta.

"Sai mu ga da wasu kafafun zaki koma gida, ay tun da ki ka shigo wurin nan sai mun ci abinci dake, idan kuma mutun yace zaiyi min rigima zan sanya bindiga ne in har be mashi tsakiyar kan shi"

Ya fada Yana daura yatsan shi akanta, Murmushi kowan nan su ya dan saki.

"Bismillah ku shiga daga ciki mu zauna, ko baku gaji da tsayuwa bane"

Zaki ne yayi maganar Yana nuna masu cikin hall din, su kansu so suke su zauna kafafuwansu har sun fara ruƙewa kawai suna fargaban shiga ne.

Ganin hakan yasa zaki matsawa ya ruƙo hannun Sajeed Dana Naufal Ya shiga da su cikin hall din, Da sauri Dr Jazz Ya matsa Cikin su ya ruƙo hannun javed dana haris yayi ciki da su.

Bayan mom turai ta gama sharewa azeeza hawayenta, ruƙo hannun ta tayi suka nufi table din su.

babu wanda yayi tsammanin Hajiya malikat zata tanka, don tunda aka fara rikicin bata sanya baki ba, sai yanzu data matso kusa da su ta ɗan saki fuskarta tana fadin"naga kowa dan uwansa yake dauka nima bari na dauki nawa" ta fada tare da ruƙo hannun Unaisah, ta haɗa dana batool dake a gefenta"mu shiga ciki Ƴan mata," wani irin farin ciki ne ya lullu6e su, da sauri suka bi bayan ta, chief owais dake atsaye ya goya hannayensa kan kirjinsa sai kallon su ya ke yi, hankalin ya kwanta babu sauran damuwa.

"Toh, ni ma dai bari na dauki nawa ƴan matan" hajiya madina ce tayi maganar da fara'a akan fuskarta ta ruko hannun Parveen da na hannah, ta nufi wurin zaman su da su, gaba daya sun koma ciki, hatta su Hajiya saratu kowa Ya koma mazaunin su wasu suna daga tsaye har yanzu hankalin wasun su bai kwanta da yaran ba, Abunne ya daure masu kai sun gaza samun sukuni a fakaice su ke satar kallon su.

Tuni Daddy sharafudden yayiwa sheikh Imam mazauni a wurin su, umarni aka bawa servers din dake awurin akan su kawo masu abin da zasu ci, nan fa suka fara aikin jera masu abinci kala kala da abin sha shaƙe da table...

Wata irin nauyayyar zuciya jemimah take ta faman saukewa, mom turai da sir mubarak sun tasa su agaba sai faman tarairayarsu su ke yi, kamar ƴa'ƴan cikin su.

"Me ku ke son ci"? Cikin kulawa tayi masu maganar.

Jemimah ce tai kokarin bude baki tace"komai ma muna ci" murmushi mom turai tayi, ba karamin burgeta su ke yi ba,

"Ko kin lura yaran nan suna kama da ke? Kamar ƙannan Jazz saboda sunyi kama da shi kan shi" murmushi tayi tana kallon Sir mubarak da yayi maganar.

"Nima nayi mamakin kamannin mu" ta fada idanunta akan fuskar Jemimah da azeeza, wadan da tuni suka fara cin abincin da aka kawo masu.

6angaren Su Hajiya saratu kuwa, sun kasa sun tsare sai jifar Parvin take yi da wani kallo mai wuyar fassaruwa, dama su biyune hajiya madina takai su tebur din su, ita da hannah wadda jikin ta keta kerma

"Baki da lafiya ne"? Hajiya laurane ta jefa mata tambayar fuskarta a yamutse, girgiza kai Hanna tayi, ta6e baki tayi"to meye kike ta kermar jiki! Tun da kun riga da kun samu wurin zama, ay sai ku saki jiki kuma ku kwashi arziki" ta fada tana hura hanci.

"Please ni ban kawo su nan da agaya masu magana ba!" Hajiya madina ce ta fada tana mai nuna 6acin aranta, kafin ta mayar da dubanta ga su parveen

"Ku ci abinci mana" da sakin fuska tayi masu magana, parvenn kamar jira takeyi aikuwa ta dauki glass of juice ta fara sha, tana shanyewa ta soma cin fruit salat, bayan ta gama ta koma tana cin spring rolls, ɗan zaro idanu hajiya saratu tayi tana kallon ikon Allah, yadda kasan irin kwancen yunwar nan,

Hajiya laurat tace"ba banza ba naga tayi kama dake ashe itama din acici ce" ta fada da zolaya tana yar dariya, parveen dai ko kallo basu ishe ta ba, ta dage damtse komai ci take, har kwara hannah a hankali take dan cakura tana ci

"Wai ni ka ɗai ce nake mamakin kamannin yaran nan da family din nan"? Hajiya madina ce tayi maganar,

Hajiya saratu tace"hmmm, ay ni abun ya gama ɗaure min kai, har yanzu zuciyata ta gaza samun nutsuwa, na ruɗe musamman dana ga yaron nan mai kama da hateem" lumshe ido Hajiya laurat tayi tunawa da surar shi don ba karamin tafiya yayi da imaninta ba.

Hajiya muhibbat tace"na girgiza da ganin shi, lokacin da mujeeda ta cire masa mask din fuskarshi araina sai da nace wannan kyau haka kamar ɗan sarkin aljanu? Dariya su kayi gaba dayan su

"Ay tun da nayi mashi kallo ɗaya na kau da ido, saboda wannan kyan nashi kadai ya isa yasa mace fadawa ga halaka" acewar Hajiya laurat

"Ina kananun Yaran nan ƴan mata masu kama da tagwaye, wlh yadda kukasan Hajja turai tayi kakin su, Ƙaramar fuskarta da komai kalar nasu ne, sai kuma wani mai kama da hajjaty kamar anyi photo copy din fuskarta acewar Hajiya mudeena.
Chapter 27 · 0% Book details