← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 104 OF 238

Sashe 104

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Numfashi Yaja kafin a hankali ya buɗe idanunshi a acikin nata, har saida gabanta ya fadi ganin yadda suka kaɗa jawur tamkar an watsa mashi barkono a cikin su, kyakkyawar fuskarshi ta 6aci da ruwan hawayen shi har cikin ranta tana jin kamar bata kyauta mashi ba.

Cikin rauni na murya yace"na amince in har hakan zaisa ki yafe min, bazan ƙara takura maki ba" dakyar ya kare maganar, kafin ya kifa kanshi saman laps dinshi

"Danish! Ta ambaci sunan shi bai amsa mata ba,

"Bana so wani yaji abunda ya faru atsakaninmu! Koda chief ne! Duk da bansan ko ka riga da ka faɗa masa ba" muryarshi kasa kasa yace"ban fada masa ba" ajiyar zuciya ta ɗan sauke, da sauri ta share hawayen ta kafin ta kuma cewa"don na yanke alakar dake atsakaninmu hakan ba yana nufin bana sonka ba! Kawai bana son ka akusa dani ne, sannan bana son hukuncin da na yanke ya shafi rayuwarka! kada ka hana idon ka bacci saboda dani, kuma kada ka ƙi cin abinci, idan kayi hakan bazan ji dadi ba..." tana magana hawaye na kara wanke fuskarta, kasan hijab din jikinta ta sanya ta share hawayen kafin ta daidaita nutsuwarta.

Kafin Takai hannu ta zuge window glass ɗin motar, tayi ma chief magana don ya buɗe mata car door ɗin da ta gaza buɗe wa, dagangan Ya datse kofar motar shiyasa ta gaza buɗe, yanzu daya tabbatar sun gama magana, da kanshi ya buɗe mata, ta fito idanunta cike tab da kwalla dakyar ta haɗiye kukan da take ji, haɗa ido sukayi cikin na juna, muryarta ƙasa ƙasa ta furta"mun gama magana inaso zan tafi" bata san hawayen da take 6oyewa sun fara sintiri kan fuskarta ba, hanky ya zaro mika mata"ki share hawayenki"! Kar6a tayi a hankali ta fara share kwallar

Iphone dinta dake a hannun shi ya miƙa mata"na sa maki card, zan kira anjima zamu yi magana, ki koma ciki yanzu" amsa mashi tayi da toh nagode, kamar karta tafi haka take ji tana tafiya tana waiwayon motar zuciyarta cike fal da tunanin shi....

*AFTER SOME DAYS*

(Bayan wasu kwanaki)

tun daga ranar da chief Ya kawo danish asibitn bai ƙara matsa mashi akan ya kawo shi ba, daga shi har ita unaisah din sunji jiki ba kaɗan ba daurewa kawai sukeyi, sauƙin su ɗaya kowannansu Ya samu abunda Yake ɗebe mashi kewa, chief ya zama tamkar abokinshi baya barin shi acikin damuwa, sai da yasan ta yadda yai harya samu kar6uwa a wurin danish, kullum suna atare abinci ma atare suke cin shi, abu uku ke raba su lokacin sallah, lokacin zuwan chief wurin aiki da kuma lokacin bacci, wani lokaci har ƙarfe shabiyu na dare suna kaiwa adakin danish harya fara koya mashi yadda zaiyi rubutu da yadda zaiyi amfani da waya harma da laptop, saboda yana son su fara making phone call da prime minister hateem, su big guy har mamaki sukeyi idan suka ga chief da danish suna magana cos basu ta6a tsammanin yaron zai iya sakar ma wani jiki acikin su har haka ba, bawan Allah Danish dannewa kawai yakeyi ba dan chief yana kokarin lallashinsa da debe mashi kewa ba da tuni ya jima da zaucewa, saboda rashin ganin unaisah ba karamin illa yakeyi mashi ba, duk daren Allah sai ya farka da radadin rashin ta, shi kadai yake haukanshi kafin Allah ya kawo mashi sauƙi, bai ta6a bari chief yaga gazawarshi ba tun da ya fahimci mutumin baya son damuwarshi kuma yana bashi kyakkyawar kulawa...

Idan muka koma 6angaren Benazir jikinta yayi sauƙi sosai, tana samun kulawa a wurin mutane ukun nan da suka tsaya mata, dr jzz, hajiya layla da kuma unaisah, cikin ƴan kwanakin nan ta dawo hayyacin ta sai dai babu wanda Ya lura da hakan kuma bata nunama kowa ba, ita kanta tasan dalilin ta nayin hakan, dagangan take yin pretending, kusan kullum ne sai su anila sunzo dubata, haka zalika Alhaji ubaid da shureim basa gajiya da zarya wurin zuwa asibitin, har ila yau Alhaji ubaid bai haɗu da unaisah ba, ba su ta6a cin karo ba, duk lokacin da zaizo tana a toilet, ko tana bacci, itama Hajiya sarah tana kokarin zuwa asibitin duk da ayyukan office da suke yi mata yawa, sau ɗaya suka ta6a haɗuwa da unaisah har suka gaisa da junan su wani abu daya daurema unaisah kai muryar matar tayi shige data cousin din aunty pretty da ta ta6a kira, aikuwa aranar har jaraba kiran layin aunty pretty tayi saboda ta tuna da ita, sai dai kash ba'a ɗaga kiran ba, saboda wayar ta koma hannun zeenatu dr shureim ne ya bata donsu dinga gaisawa, ita kuma dama bata cika ruke waya a hannunta ba, sai ta wuni bata dauketa ba sai in ta tashi kiran dr shureim tukunna take daukarta..

Alhaji musa tun zuwan da yayi sau ɗaya, bai ƙara zuwa asibitin ba, ko awaya baya kira balle har yasan wani hali suke a ciki, gashi har dr ya fara tunanin sallamar su saboda taji saukin jikin ta sosai..

*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE✍️*

*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*

Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:05 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite

Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe chapter 34 Complete
by
Novels Elite Admin
August 30, 2024
Sponsored Link

Takun Ƙarshe
✍️

EPISODE 33

Kwance take tana sharar bacci cikin kwanciyar hankali, cikin bacci ta yi kwakkwaran juyi zata gyara kwanciyarta kwatsam tayi arba da fuskar mutun wani irin firgita tayi a haukace ta zabura zata mike da sauri Benazir ta cafko hannun ta ta ruƙe shi gam, suka ƙurawa juna ido batare da ƙyaftawa ba, Hankalin Unaisah ba ƙaramin tashi yayi ba, ta rasa gane meyasa cikin ƴan kwanakin nan matarke tsareta da ido kamar zata lashe ta, aranta ta ayyana kodai ta6in hankalin nata ne Ya motsa? Kada fa ta hau ta da bugu tun ba hankaline da ita ba..tuni tasha jinin jikin ta, tana faman haɗiyar yawu kutt murya na rawa ta furta"am..um.. mamana! Tun yaushe kika farka"? Dakyar ta kare maganar ganin yadda Benazir tayi mata rumfa kamar zata danne ta, babu alamun zata tanka mata tayi shiru tanata kallon ta...babban tashin hankalin unaisah hajiya layla bacci takeyi balle ta kawo mata ɗauki, tuni ido ya raina fata.

"Dan Allah na roƙe ki, ki daina kallona haka, babaynki ce fa, ki na bani tsoro. .." sai da tay wannan maganar, Benazir ta saki murmushin gefen fuska har dimple

dinta ya lotsa...

"Babyna ne"? La66an unaisah na kerma tace"ni ce, dan Allah kada kiyi min komai..." ƴar dariya benazir tayi, wani irin nishadi take ji..

Shafa sumar kanta tayi har wani kyafkyafta idanu take Yi kamar wata mara gaskiya

Unexpected ta ji ta manna mata sumbata kan kuncinta, kafin tayi wani yunkuri ta kara mata wani kan la66anta, runtse idanu tayi kamar zata fasa ihu ta furta"na shiga uku, tawa ta same ni"! dariya benazir tayi kafin ta janye jikinta daga na unaisah ta koma kan gadonta ta kwanta idanunta na fuskantar ceilling..." wasu zafafan hawayene suka wanke fuskarta da sauri ta cusa kanta jikin pillow,

Satar kallon ta unaisah tayi, ta rasa gane meke damun matar, ta fara tsorata da lamarinta, kwanakin nan ta canza mata, ba kamar farkon da tafara jinyarta ba, ko meyasa❓

Ajiyar zuciya ta sauke, kafin ta sauko daga kan gadon, ta lalla6a cikin sanɗa take tafiya, backpack dinta ta buɗe ta curo wayarta ta nufi toilet ta shige ciki,

Text message ta tura ma daddynta

"Daddy, barka da dare, daddy ni dai nagaji da zaman asibiti, gida nakeso in dawo" tana tura mashi text din jim kaɗan saiga kiran shi, tayi mamaki saboda batasa rai zai bata amsa ba kusan karfe shabiyu na dare, tayi zaton yayi bacci.

Picking call din tayi tare da kara wayar a kunne"My daughter! Me kike yi har yanzu baki kwanta bacci ba? Wani abu ya faru ne"?

Cikin muryar raɗa ta furta"ba abun da ya faru, kawai bana jin dadin yawan kallona da matar takeyi, duk in na farka tsakar dare saina ganta akaina ta tsare ni da idanunta"

Sautin dariyar shi ce ta ratsa kunnanta aiko ta haɗe fuska kamar tana agabanshi tace

"Daddy dariya kake yi min?

"Sorry daughter, maganarki ce ta bani dariya, but ki ƙara hakuri Anila ta fada min next tomorror za'a sallame ta"

Shagwa6e fuska tayi, ko tsoro bata ji ita kadai a toilet

"daddy ina yan uwana? Yau banji muryoyin su ba"

"Suna nan cikin koshin lafiya, basu da wata damuwa"

Shiru sukayi na wani lokaci, zuciyar ta sai azalzalarta takeyi akan ta tambaye shi ina Danish amma ina takasa furtawa...
Chapter 104 · 0% Book details