← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 127 OF 238

Sashe 127

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Har su mami ta sanar ma abunda yakeyi suka ce taci gaba dayi mashi addu'a in sha Allah zaiji sauki, ita dai hankalinta bai kwanta da yanayin shi ba, ranta yana bata wani abu ba dai dai ba agidan dole akwai wani abu daya faru wanda yayi silar guduwar Anah da kuma rikicewar baby junaid! Kwana biyu da baije school ba sai ga kira daga class master din su junaid, bayan sun gaisa da anila ta ta tambayeta meyasa kwana biyu junaid baizo school ba, tace mata baida lafiya ne amma idan yaji sauki zai cigaba da zuwa

Saurari Littafin Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
Cikin kwana uku anila duk ta fita hayyacinta har faɗawa tayi saboda damuwar rashin Ana da kuma halin da baby junaid yake a ciki, abie har kiranta yayi shi da uncle dan iya da su ummu suka taru akanta suka yi mata nasiha cikin lallami da lallashi donta kwantar da hankali saboda kowa ya fahimci bata acikin nutsuwarta, ko abinci sai zahra tayi dakyar take samu ta ci ta zama abun ban tausayi daga ita har junaid din harma kwara ita akan shi saboda ya takura kan shi ya kuma takura mata ya hanata sukuni ko toilet zata shiga sai ya sanya rigima zai bita, dakyar take samu ta lalla6a shi da wayarta don yayi game kafin ta samu ya kyale ta, idan salla zatayi sai dai ta goya shi abayanta, har yau babu abunda ya canza, yanzu girkin gidan ya dawo hannun mami da ummi saboda rashin Ana, zahra kuma ba azaune take ba, tana zuwa aiki, ita kuma anila kota nemi su bata ta tayasu aiki sai suce taje taji da junaid zasu kula da komai...💔

________________________✍️

Shin Ya labarin Benazir? Ay tun ranar da suka dawo gida ta kasa ta tsare tana jiran taj da Angel su dawo daga kasuwa, shiru shiru taji basu dawo ba har marece ya nutsa hankali atashe tace ma hajiya layla ta kira mata layin taj awaya taji meya hana su dawo! Hajiya layla tana yan kame kame tace mata ta manta bata da layin taj, kuma dayazo asibitin daukar Angel bata kar6a ba, sai dai ko dr shureim watakil shi yana da layin shi, ko da ta yi ma dr shureim magana akan ya kira mata taj cikin rashin kwanciyar hankali ya kira wrong number da gangan saboda ta tsare shi da ido tana jiran shi ya kira mata mijin ta, a dole yayi pretending ya ci gaba da magana yana fadin pls taj marece yayi ga benazir tana jiran ku, dan Allah ku dawo hakanan okey toh sai anijima Allah ya dawo daku lafiya, bayan ya katse kiran yace mata tayi hakuri ta kara jira suna akan hanya, baiwar Allah jiki asanyaye ta zauna kan sofa tana jiran dawowarsu, hankalinta kwata kwata ba a kwance yake ba, gani take kamar bazata sake ganin angel din ta ba...

Abu kamar wasa har dare yayi babu taj ba angel, hankalinta ba karamin tashi yayi ba, lokacin da zasu yi dinner bayan su tani sun kammala shirya masu abinci a dining hajiya layla tace tazo su ci abinci, tace mata bazata iya ci ba, in har taj bai kawomata Angel din ta ba

hankulansu ba karamin tashi yayi ba, gaba ɗaya suka taru akanta suka fara lallashinta suna bata baki duk don su samu su taci abincin amma taƙiya, babu wanda baiji tausayinta ba musamman da karfe goma sha ɗaya ta buga na dare, a lokacin ta gama gane karya sukeyi mata, zuciyarta ta karaya a karshe ta fashe da kuka tace su daina boye mata gaskiya, kawai su fada mata ina yarta Angel? Saboda tana ji aranta ba taj bane ya dauke ta, babu wani siyayyar da suka je yi mata duk plan ne .." gaba daya aka rasa wanda zai faɗa mata gaskiya saboda fargaban halin da zata shiga, ranta yayi mugun 6aci zuciyarta ta hasala ganin sun zuba mata ido an rasa me magana a cikin su, idanunta suka kaɗa jawur, zafafan hawaye suka wanke fuskarta, tsabar fusata jikinta har kerma yakeyi tana faman jan numfashi tace"mami! Ya shureim, aunty sarah ku fadamin gaskiya ina babyna take? Wanene Yake son rabani da ita? Yarinyar nan ƴata ce fa halak malak, akan me zaku yi min karyar taj ya dauke ta sunje shopping mall? Meyasa har yanzu basu dawo ba? Kusan karfe goma sha ɗaya na dare, wlh idan har baku dawo min da babyna ba, komai zai iya faruwa..." dakyar ta kare maganar tare da sanya tafukan hannayenta ta dafe kanta kamar yadda take yi idan zatay pretending ta fara yi masu kuka na fitar hayyaci kamar zata rotsa dodon kunnuwansu, gaba ɗaya tabi ta furgita su, zeenatu tsabar tsoro daki ta shige ta kulle dama tunda Benazir din ta dawo ko gaisuwa bata hada su ba, bayan ta shiga dakinne ta fara tariyo fuskar Unaisah yarinyar data kira sunanta da Unaizah, har cikin aranta tana son ta kara haduwa da ita kuma tana son tasan wacece Unaizar su data mutu? ya akai komai nasu yazo iri ɗaya? Tabbas tana son tasan komai dangane da ita bayan haka tana son su kulla kawance da Unaisah saboda ta kwanta mata aranta tun a kallo na farko da idanunsu suka shiga cikin na juna.

Daga cikin falo ta dinga jiyo sautin muryoyinsu Hajiya layla suna ta kokarin lallashin Benazir, hada alhaji ubaid a lokaci baijima da shigowa gidan ba, gaba daya mutanan gidan suka taru akanta, in ka cire Alhaji musa saboda baya nan baisan budurin da sukeyi ba

Adaren ranar dakyar suka samu bacci ya ɗauketa, jikinta hada zazza6i.

har ila yau tana akwance ba lafiya, saboda rashin Angel dinta, tayi kukan harta gaji, kowa na gidan tausayinta yake ji, yau kwana uku kacal da rabuwarsu da unaisah tana jinyar zuciyarta bata son cin abinci ko wanka ta dainayi ta zama kamar mahaukaciya, kusan kullum sai hajiya layla ta matsa ma shureim akan ya kira anila yayi mata magana ta fada masu ina ne gidan iyayen yarinyar, dr shureim yace tayi su yi hakuri bazai iya ba, bayaso ya takura ma anila bayan haka babu amfanin suje gidan iyayen yarinyar tun da ko sunje yarinyar fa ba yar benazir bace ganinta bazai amfani benazir da komai ba saima ya ƙara ɗaga mata hankali tunda ba basu ita za'ae ba, adole hajiya layla ta hakura da yi mashi maganar Azeezaty

_________________________✍️

Idan muka koma bangaren Marwa, jikinta ya ƙara tsauri babu wani cigaba a lafiyarta, yatsun hannunta sai ƙara matsewa sukeyi ga wasu kananun kuraje da suka fara feso mata akan fuskarta, baiwar Allah ita kadai tasan halin da take a ciki, wani lokaci idan hannunta suka fara mata radadi kamar zata zauce, duk da halin da take aciki kokari take ta fallasa asirin wanda yai silar ɗaura mata ciwon, sau uku hajjaty ke xuwa dubata kuma tana kokarin kiyaye duk wasu sharudda nayin amfani da maganin da sheikh imam ya bata sai dai takasa gane an canza ruwan maganin rashin sani ya fi dare duhu batasan tana ƙara wa marwa ciwon ta ba takasa lura da yanayin ta, gashi duk in ta shigo daki sai marwa tayi mata alama da hannu har yau takasa fahintar me take nufi, idan tayi yunkuri takura kanta akan tay magana wani irin radadi take ji a makoshin badan taso ba ta hakura, wani lokaci idan tayi ma hajjaty alama da hannu ta kasa ganewa saita buga kanta jikin pillow tayi ta kuka kamar ranta zai fita, dakyar hajjaty take samu ta lallasheta har ta shawo kanta.

Saurari Littafin Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
A cikin yan kwanakin nan hajiya saratu bata bari hanya ta haɗata da hajjaty saboda tsoranta da take ji, hajjaty harta fara lura da ita, ranar da ta shiga kaima baba obie abinci hajiya saratu tana adakin, tun da taji sallamar hajjaty da sauri ta mike ko sallama batayi mashi ba ta fuce daga dakin, tun daga nan hajjaty ta fara lura da ita, abun ya ɗaga hankalin ta, tarasa gane laifin me tayi mata? Duk da dama tasan ba sonta take yi ba akwai tsanarta a zuciyarta amma yanzu abun ya karu fiye da lokacin baya

Idan muka koma bangarensu twins tun ranar da suka ga iftila'in daya faɗawa marwa basu ƙara marmarin komawa gidan ba, saboda kyankyami da kyama suke ji, a hotel suka koma da kwana, daga bisani da hajiya saratu takira zayn awaya ta fara zazzaga mashi masifa akan rashin dawowarsu gida yace mata su fa bazasu dawo ba in har ba an fidda mai aikin nan daga gidan su ba, bata musa masu ba, saima cewa tayi su bata lokaci zatayi magana da baba obie akan a maida marwa garin su indai hakan zai kwantar masu da hankali, sunji dadin maganarta hada yi mata godiya

✊Boss Bature💋: ________________________✍️

A kishingiɗe yake saman lallausan rug din dakin baba obie ya ɗaura head dinsa kan pillow, jikinshi na sanye da jallabiya fara kyal, fragrance dinsa ya haɗe da sanyin A.c din dakin, ba su jima da dawowa daga sallar asuba ba yabiyo baba obie dakin shi...A hankali yake danna phone dinsa Kira ne ya shigo ganin sunan commender james yasa shi picking call din tare da kara wayar a kunne, cikin girmamawa suka gaishe da junansu kafin daga bisani commender james ya sanar da shi sun samu izni daga manyan su, za su shigo Nigeria da shi da sauran sojojin da suka tsinci su Angel a dajin evil forest

Chief yace"I'm very happy to hear that, I can't wait to see you"

Commender james yace"I'm also very happy, this is the first time I'll be coming to Nigeria because of the children we found in the forest.

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.
Chapter 127 · 0% Book details