Sashe 168
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wata irin karyayyar murya mai cike da 6acin rai ya furta"Angel, mafarki nake ko gaske? Da kanki kike jifana da waɗannan munanan kalaman? ni Angel? Your Shield"? numfashi ya ɗan ja kamar bazai iya karasa maganar ba yace"meyasa zaki min haka? Lafin me nayi maki da cancani cin mutunci daga gareki? Angel kema Kina min kallon jahili? Mara asali? Kuma kika kira ni da matsafi"?
ɗaga mashi gira tai"Hell fucking yeah, ko nayi ƙarya ne"? Kasa magana yayi,
"abu ɗaya ne zakayi wanda zai wanke ka daga gareni, shine Ka cire tsoro, Ka basu haɗin kai akai farmaki gidan kurkukun kaddara, ta hakanne kaɗai zan yarda dakai in kuma har ka bijire min kaki bin Umarnina, wlh na rantse da wanda raina yake a hannunsa muddin baka bada goyon baya ba, na kwammace in mutu da ciwon sonka, akan in aure ka"! Da sauti mai karfi tayi maganar tare dakai hannu ta daki handrail..
duk abunda ke faru tsakanin su babu wanda ya sani
"In kuwa har ka bari Chief yayi nasarar ruguza kurkukun ƙaddara batare da taimakonka ba, zan mallaka mashi kaina..." bata kare maganar ba sakamakon zazzafan marin daya kwasa mata wanda shi kanshi bada sanin shi ba, a karo na farko data fara jin tafin hannunsa akan fuskarta da sunan mari, wa'iyazubillah wani azababben radadi taji ya ratsa sassan jikin ta kamar an watsa mata wuta jirine Ya kwashe ta, ta tafi zata kife ƙasa cikin zafin nama Ya taro ta da hannunshi ya dawo da ita kan kirjin shi, yayi hanzarin daukarta kan kafadarshi Ya nufi bedroom dinshi da ita gudun kada wani ya riskesu a halin da suke a ciki.
Yana shiga ɗakin Ya kwantar da kan gadon shi, kamar matatta, da alama suma tayi saboda azabar da taji.
Hankalin shi idan yai dubu toh ya tashi, Jikinshi sai kerma yake kamar wanda sanyi Ya kama, zafin Kishi Yaja mishi bala'e..
Duk da sanyin A.c din dakin hakan bai hana gumi tsastsafo mashi kan fuskarshi ba, zukunnawa yayi daga bakin gadon yana kallon gefen fuskarta, shi kanshi Ya tsorata da ganin yadda fatar gurin tayi ja sosai, shatun fingers in shi ya fito ruɗu ruɗu.
Yatsun hannayen shi Ya zuba ma Idanun shi Yana kallon su cike da danasanin marin da yayi mata, ya san yadda marin Evil giant yake da zafi, zata Iya kai Sati da radadin dafin marin a jikin ta.
cike da takaici ya dinga bugun kanshi da hannayen shi kamar zai zauce saboda zafin abun da ya yi mata
Tuni hawayen da suka taru cikin idanunshi suka fara Yar tseral kan kuncin shi, abu biyu ya haɗe mashi ga zafin munanan kalaman data jefe shi da su ga takaicin marin da yayi mata.
Cikin karyayyar murya ya furta"ba laifina bane, ke ce kika bata min rai, gashi kinja na mareki bada son raina ba" ya faɗa tare da daura tafin hannunsa saitin inda Ya mare ta, dabara ce ta fado mashi da sauri ya saita fuskar shi saitin tata, sihiri gaskiyar mai shi, ruwan hawayensa dake ɗiɗɗiga kan fuskarta sune suka goge tabon marin da ya yi mata cikin kankanin lokaci fatar ta dawo fara sol kamar ta jinjira, numfashi Yaja tare da sauke ajiyar zuciya a hankali launin idanunsa suka dawo yadda suke.
kallonta da yake yi ahaka yafi masa kwanciyar hankali akan Ya farfaɗo da ita saboda fargaban masifarta.
Daga gefenta Ya raba jikin shi, Ya kwanta tare da lumshe idanun shi, bai ta6a fuskantar tashin hankali irin na yau ba, tayaya zai iya shawo kan Unaisah ta fahimci abunda yake nufi"?
Kwatsam yana a cikin mawuyacin halin nan ba zato ba tsammani ya tsinkayi Muryar Khala a cikin kunnanshi..
"Uhum Garkuwa Namu"
A rude Ya mike zaune yana bin dakin da kallo, cikin sauri Ya share hawayen fuskarsa, jikinshi har 6ari yake garin zumudin ya sauko daga kan gadon, Hasken ɗakin shi ne Ya dauke ɗuff Duhu Ya mamaye ko'ina, bai nufi ko'ina ba sai gaban mirror Ya yaye madubin idanunshi su ka yi mashi tozali da tsohuwa Khala zaune kan armchair, Cikin shigarta ta gado fuskarta a yamutse ba annuri.
Zama yayi kan Mirror chair din with respect ya gaishe da ita, da fara'a ta amsa mashi
Kafin Ya nutsu Yana jiran jin me zata ce ma shi
"Ina fata kun fara shirye shiryen kawo farmaki"? shiru ya yi baice mata uffan ba.
Yanayin dake a kan fuskarshi ta nazarta nan take ta fahimci baida matsaya
Yar dariya tayi"jikana, faɗamin ba, me ake Ciki ne"? dakyar Ya labarta mata abinda ke faruwa bai boye mata komai ba
Girgiza kai tay"yaro man kaza, Har yanzu Jinin Elders ne a jikin ka, amma Alhamdulillah naji dadi da Allah Ya bani ikon ganawa dakai a karo na biyu, saboda na fahimci ka na bukatar in wayar maka dakai, in kuma yi maka karatun ta nutsu ta yadda zaka fahimci su wanene Elders da kuma dalilin dayasa suka raine ka..." aruɗe Yake kallon fuskarta...
"Kasan wacece ni, ka kuma san matsayina agidan kurkukun kaddara, nafi ka sanin komai Danish, duk wani abu da suke aikatawa a tafin hannuna yake" ta faɗa tana nuna mashi tafin hannun ta.
"Abu na farko da baka sani ba, Elders Mayaudara ne, Maha'inta, maciya amana, bansan ko ka san da labarin nan ba, amma inaso ka sani tun kana jinjirinka cikin tsummanka suka sace ka daga wurin iyayenka, suka rabaka da su batare da saninka ba, sannan suka sadaukar da kai zuwa gidan kurkukun ƙaddara, Ni nasan su wanene Iyayen ka, wallahi basu san kana araye ba, an yaudare su ne da sunan ka mutu...." dafe kanshi yayi da hannu ɗaya zuciyarshi cike fal da ruɗanin maganarta, bazai ce tayi karya ba sai dai kokwanton da zuciyarshi keyi bazai bari ya aminta da ita ta cikin sauƙi.
"Bani da isasshen lokacin da zan yi maka bayani, amma atakaice ka zauna kayi nazari Danish, kai ganau ne ba jiyau ba, kasan komai, har yau zubda jinin mutane suke yi kamar kwari, Laifin me suka yi masu? Ahaka zaka rufa masu asiri uhyum? Ita kanta yarinyar da kake gudun rabuwa da ita ba zasu kyale ta ba, wallahi in har baka bada goyon baya an kawo karshen su ba, da kai da ita sai kun salwanta, saboda suna nan suna shirin yadda zasu kashe ku.."
waro idanun shi waje yayi jin abinda tace.
Murmushin gefen fuska ta saki tare da jinjina mashi kai"hmm wai kana tunanin Suna kaunarka? To wallahi ko ɗaya basu ta6a kaunarka ba, sun raineka ne don biyan bukatar kansu, idan kai me hankali ne ga misali nan, Yanzu da suke ganin sunci moriyarka amfaninka ya kare kana neman tona masu asiri ba ga shi har sun ɗauke mukamin da suka baka na garkuwarsu ba, sun ba Jeremiah, kai kuma nema suke su salwantar da rayuwarka saboda kai kadaine kasan sirrinsu dakai kadai za'a iya farmakarsu...."
wani irin gumin tashin hankaline Ya wanke fuskarshi, Maganar tsohuwa khala tayi matuƙar yin tasiri a zuciyar shi.
Kusan sau uku Tana ambaton sunan shi bai amsa mata ba, saboda zuciyarshi ta lula duniyar tunani
Har saida tayi mashi gyaran murya kafin ya dawo hayyacin sa
"Ina Gabriel? Ya rayu ko ya mutu"? ya ɗanyi mamakin jin ta tambayi gabriel ko a ina ta san shi"?
"Yana adakinsa, bacci yakeyi"
"Masha Allah, Naji dadin jin hakan, sai dai, Yar Uwarsa daya bari agidan kurkuku tana acikin mawuyacin hali..."
"Who's she? ya tambaya don sam ya manta da cewa Gabriel Yana da sister.
"His twin sister Gabriella...." a takaice ta labarta mashi rashin imanin da tsohuwa inno tasa giant yayi mata, tsabar 6acin rai jikinshi har tsuma yakeyi
"ta rokeni akan Tana son ganin ɗan uwanta, nayi mata alkawarin ko zan rasa raina ne in dai muna da tsawaicin kwana zan haɗa ta da ɗan uwanta" cikin rauni na murya tayi maganr tare da mikewa daga kan kujerar da take, ta haske mashi Gadon da Gabriella take akwance kamar babu rai a jikinta, sai jan numfashi take dakyar dakyar
"Nayi zaton ta samu lafiya, amma wani abu ya faru jiya wanda Ya ɗaga hankalina, tana daga zuƙunna tayi aman Jini, ta dafe ciki tana faɗin Yan hanjinta suna konewa, Inaji araina Inno ce tayi mata asiri, nadai yi kokarin yi mata yan dabaruna ahaka Jikin da sauƙi amma tana bukatar taimakon gaggawa daga gare ku idan ba haka ba da wuya ta rayu.."
Jikin shi yayi sanyi saboda tsantsanin tausayin yarinyar daya kama shi, yanzu ya tuna ranar farko da aka kawo su har tsohuwa Zafreen tasa aka raba su.
"Danish Ahaka zaka rufa masu asiri? Shikenan babu wani wanda zai kawoma bayin Allah dauki! Haka zamu barsu su cigaba da azabtar da rayuka? Ba zamu ɗauki mataki ba"? Sam ya kasa magana saboda raunin da zuciyar shi tayi
*Da wata irin kakkausar murya ta firta"YA RAGE NAKA GARKUWA, DOLE ƊAYA CIKIN BIYUN NAN YA FARU! KO DAI KA BADA GOYAN BAYA AKAWO MASU FARMAKI, KO KUMA SU SU KAWO MAKU FARMAKI SU GA BAYAN KU..."*
Sau Uku ta maimaita Hakan, kafin ta cigaba da ƙarfafa mashi gwiwa daga bisani bayan ta ƙara jaddada mashi kwanan watan da zasu yi black night, ta bashi wasu muhimman bayanan da zasu amfane su, daga nan ta 6ace ma ganin shi, kifa kanshi yayi gaban mirror ɗin Zuciyar shi cike fal da damuwa, anan wani wahalallan bacci mai nauyi ya yi awon gaba da shi.
Lokacin da Batool ta farka daga bacci taga babu Unaisah adakin, bata damu ba, bayan tayi sallar asuba, taji shiru bata dawo ba, hakan yasa ta miƙe ta fito daga dakin tafara neman ta, sai da tabi ɗakunan Yan uwansu duka ta duba taga babu Unaisah, Hankalinta ba karamin tashi yayi ba,.
Da sauri ta nufi ɗakin Aunty Ummunsu, tayi knocking almost 3 times, kafin ta samu Ummi ta buɗe kofar, tana miƙa hadi da yin hamma ko kayan baccin jikinta bata kaiga cire wa.
"Babe, Har kin tashi"? Daga mata tayi"Aunty Ummi sister tazo nan? Na farka banganta ba"
Girgiza kai Ummi tayi"Bata zo ba, kin duba ko'ina"?
"Eh," ta fada da damuwa
ɗaga mashi gira tai"Hell fucking yeah, ko nayi ƙarya ne"? Kasa magana yayi,
"abu ɗaya ne zakayi wanda zai wanke ka daga gareni, shine Ka cire tsoro, Ka basu haɗin kai akai farmaki gidan kurkukun kaddara, ta hakanne kaɗai zan yarda dakai in kuma har ka bijire min kaki bin Umarnina, wlh na rantse da wanda raina yake a hannunsa muddin baka bada goyon baya ba, na kwammace in mutu da ciwon sonka, akan in aure ka"! Da sauti mai karfi tayi maganar tare dakai hannu ta daki handrail..
duk abunda ke faru tsakanin su babu wanda ya sani
"In kuwa har ka bari Chief yayi nasarar ruguza kurkukun ƙaddara batare da taimakonka ba, zan mallaka mashi kaina..." bata kare maganar ba sakamakon zazzafan marin daya kwasa mata wanda shi kanshi bada sanin shi ba, a karo na farko data fara jin tafin hannunsa akan fuskarta da sunan mari, wa'iyazubillah wani azababben radadi taji ya ratsa sassan jikin ta kamar an watsa mata wuta jirine Ya kwashe ta, ta tafi zata kife ƙasa cikin zafin nama Ya taro ta da hannunshi ya dawo da ita kan kirjin shi, yayi hanzarin daukarta kan kafadarshi Ya nufi bedroom dinshi da ita gudun kada wani ya riskesu a halin da suke a ciki.
Yana shiga ɗakin Ya kwantar da kan gadon shi, kamar matatta, da alama suma tayi saboda azabar da taji.
Hankalin shi idan yai dubu toh ya tashi, Jikinshi sai kerma yake kamar wanda sanyi Ya kama, zafin Kishi Yaja mishi bala'e..
Duk da sanyin A.c din dakin hakan bai hana gumi tsastsafo mashi kan fuskarshi ba, zukunnawa yayi daga bakin gadon yana kallon gefen fuskarta, shi kanshi Ya tsorata da ganin yadda fatar gurin tayi ja sosai, shatun fingers in shi ya fito ruɗu ruɗu.
Yatsun hannayen shi Ya zuba ma Idanun shi Yana kallon su cike da danasanin marin da yayi mata, ya san yadda marin Evil giant yake da zafi, zata Iya kai Sati da radadin dafin marin a jikin ta.
cike da takaici ya dinga bugun kanshi da hannayen shi kamar zai zauce saboda zafin abun da ya yi mata
Tuni hawayen da suka taru cikin idanunshi suka fara Yar tseral kan kuncin shi, abu biyu ya haɗe mashi ga zafin munanan kalaman data jefe shi da su ga takaicin marin da yayi mata.
Cikin karyayyar murya ya furta"ba laifina bane, ke ce kika bata min rai, gashi kinja na mareki bada son raina ba" ya faɗa tare da daura tafin hannunsa saitin inda Ya mare ta, dabara ce ta fado mashi da sauri ya saita fuskar shi saitin tata, sihiri gaskiyar mai shi, ruwan hawayensa dake ɗiɗɗiga kan fuskarta sune suka goge tabon marin da ya yi mata cikin kankanin lokaci fatar ta dawo fara sol kamar ta jinjira, numfashi Yaja tare da sauke ajiyar zuciya a hankali launin idanunsa suka dawo yadda suke.
kallonta da yake yi ahaka yafi masa kwanciyar hankali akan Ya farfaɗo da ita saboda fargaban masifarta.
Daga gefenta Ya raba jikin shi, Ya kwanta tare da lumshe idanun shi, bai ta6a fuskantar tashin hankali irin na yau ba, tayaya zai iya shawo kan Unaisah ta fahimci abunda yake nufi"?
Kwatsam yana a cikin mawuyacin halin nan ba zato ba tsammani ya tsinkayi Muryar Khala a cikin kunnanshi..
"Uhum Garkuwa Namu"
A rude Ya mike zaune yana bin dakin da kallo, cikin sauri Ya share hawayen fuskarsa, jikinshi har 6ari yake garin zumudin ya sauko daga kan gadon, Hasken ɗakin shi ne Ya dauke ɗuff Duhu Ya mamaye ko'ina, bai nufi ko'ina ba sai gaban mirror Ya yaye madubin idanunshi su ka yi mashi tozali da tsohuwa Khala zaune kan armchair, Cikin shigarta ta gado fuskarta a yamutse ba annuri.
Zama yayi kan Mirror chair din with respect ya gaishe da ita, da fara'a ta amsa mashi
Kafin Ya nutsu Yana jiran jin me zata ce ma shi
"Ina fata kun fara shirye shiryen kawo farmaki"? shiru ya yi baice mata uffan ba.
Yanayin dake a kan fuskarshi ta nazarta nan take ta fahimci baida matsaya
Yar dariya tayi"jikana, faɗamin ba, me ake Ciki ne"? dakyar Ya labarta mata abinda ke faruwa bai boye mata komai ba
Girgiza kai tay"yaro man kaza, Har yanzu Jinin Elders ne a jikin ka, amma Alhamdulillah naji dadi da Allah Ya bani ikon ganawa dakai a karo na biyu, saboda na fahimci ka na bukatar in wayar maka dakai, in kuma yi maka karatun ta nutsu ta yadda zaka fahimci su wanene Elders da kuma dalilin dayasa suka raine ka..." aruɗe Yake kallon fuskarta...
"Kasan wacece ni, ka kuma san matsayina agidan kurkukun kaddara, nafi ka sanin komai Danish, duk wani abu da suke aikatawa a tafin hannuna yake" ta faɗa tana nuna mashi tafin hannun ta.
"Abu na farko da baka sani ba, Elders Mayaudara ne, Maha'inta, maciya amana, bansan ko ka san da labarin nan ba, amma inaso ka sani tun kana jinjirinka cikin tsummanka suka sace ka daga wurin iyayenka, suka rabaka da su batare da saninka ba, sannan suka sadaukar da kai zuwa gidan kurkukun ƙaddara, Ni nasan su wanene Iyayen ka, wallahi basu san kana araye ba, an yaudare su ne da sunan ka mutu...." dafe kanshi yayi da hannu ɗaya zuciyarshi cike fal da ruɗanin maganarta, bazai ce tayi karya ba sai dai kokwanton da zuciyarshi keyi bazai bari ya aminta da ita ta cikin sauƙi.
"Bani da isasshen lokacin da zan yi maka bayani, amma atakaice ka zauna kayi nazari Danish, kai ganau ne ba jiyau ba, kasan komai, har yau zubda jinin mutane suke yi kamar kwari, Laifin me suka yi masu? Ahaka zaka rufa masu asiri uhyum? Ita kanta yarinyar da kake gudun rabuwa da ita ba zasu kyale ta ba, wallahi in har baka bada goyon baya an kawo karshen su ba, da kai da ita sai kun salwanta, saboda suna nan suna shirin yadda zasu kashe ku.."
waro idanun shi waje yayi jin abinda tace.
Murmushin gefen fuska ta saki tare da jinjina mashi kai"hmm wai kana tunanin Suna kaunarka? To wallahi ko ɗaya basu ta6a kaunarka ba, sun raineka ne don biyan bukatar kansu, idan kai me hankali ne ga misali nan, Yanzu da suke ganin sunci moriyarka amfaninka ya kare kana neman tona masu asiri ba ga shi har sun ɗauke mukamin da suka baka na garkuwarsu ba, sun ba Jeremiah, kai kuma nema suke su salwantar da rayuwarka saboda kai kadaine kasan sirrinsu dakai kadai za'a iya farmakarsu...."
wani irin gumin tashin hankaline Ya wanke fuskarshi, Maganar tsohuwa khala tayi matuƙar yin tasiri a zuciyar shi.
Kusan sau uku Tana ambaton sunan shi bai amsa mata ba, saboda zuciyarshi ta lula duniyar tunani
Har saida tayi mashi gyaran murya kafin ya dawo hayyacin sa
"Ina Gabriel? Ya rayu ko ya mutu"? ya ɗanyi mamakin jin ta tambayi gabriel ko a ina ta san shi"?
"Yana adakinsa, bacci yakeyi"
"Masha Allah, Naji dadin jin hakan, sai dai, Yar Uwarsa daya bari agidan kurkuku tana acikin mawuyacin hali..."
"Who's she? ya tambaya don sam ya manta da cewa Gabriel Yana da sister.
"His twin sister Gabriella...." a takaice ta labarta mashi rashin imanin da tsohuwa inno tasa giant yayi mata, tsabar 6acin rai jikinshi har tsuma yakeyi
"ta rokeni akan Tana son ganin ɗan uwanta, nayi mata alkawarin ko zan rasa raina ne in dai muna da tsawaicin kwana zan haɗa ta da ɗan uwanta" cikin rauni na murya tayi maganr tare da mikewa daga kan kujerar da take, ta haske mashi Gadon da Gabriella take akwance kamar babu rai a jikinta, sai jan numfashi take dakyar dakyar
"Nayi zaton ta samu lafiya, amma wani abu ya faru jiya wanda Ya ɗaga hankalina, tana daga zuƙunna tayi aman Jini, ta dafe ciki tana faɗin Yan hanjinta suna konewa, Inaji araina Inno ce tayi mata asiri, nadai yi kokarin yi mata yan dabaruna ahaka Jikin da sauƙi amma tana bukatar taimakon gaggawa daga gare ku idan ba haka ba da wuya ta rayu.."
Jikin shi yayi sanyi saboda tsantsanin tausayin yarinyar daya kama shi, yanzu ya tuna ranar farko da aka kawo su har tsohuwa Zafreen tasa aka raba su.
"Danish Ahaka zaka rufa masu asiri? Shikenan babu wani wanda zai kawoma bayin Allah dauki! Haka zamu barsu su cigaba da azabtar da rayuka? Ba zamu ɗauki mataki ba"? Sam ya kasa magana saboda raunin da zuciyar shi tayi
*Da wata irin kakkausar murya ta firta"YA RAGE NAKA GARKUWA, DOLE ƊAYA CIKIN BIYUN NAN YA FARU! KO DAI KA BADA GOYAN BAYA AKAWO MASU FARMAKI, KO KUMA SU SU KAWO MAKU FARMAKI SU GA BAYAN KU..."*
Sau Uku ta maimaita Hakan, kafin ta cigaba da ƙarfafa mashi gwiwa daga bisani bayan ta ƙara jaddada mashi kwanan watan da zasu yi black night, ta bashi wasu muhimman bayanan da zasu amfane su, daga nan ta 6ace ma ganin shi, kifa kanshi yayi gaban mirror ɗin Zuciyar shi cike fal da damuwa, anan wani wahalallan bacci mai nauyi ya yi awon gaba da shi.
Lokacin da Batool ta farka daga bacci taga babu Unaisah adakin, bata damu ba, bayan tayi sallar asuba, taji shiru bata dawo ba, hakan yasa ta miƙe ta fito daga dakin tafara neman ta, sai da tabi ɗakunan Yan uwansu duka ta duba taga babu Unaisah, Hankalinta ba karamin tashi yayi ba,.
Da sauri ta nufi ɗakin Aunty Ummunsu, tayi knocking almost 3 times, kafin ta samu Ummi ta buɗe kofar, tana miƙa hadi da yin hamma ko kayan baccin jikinta bata kaiga cire wa.
"Babe, Har kin tashi"? Daga mata tayi"Aunty Ummi sister tazo nan? Na farka banganta ba"
Girgiza kai Ummi tayi"Bata zo ba, kin duba ko'ina"?
"Eh," ta fada da damuwa