Sashe 138
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gyaran muryar da Aneelerh tay mata ne yasa ta ɗago adabarbarce ta dube su sam ta manta da Benazir duk saita kama kanta tana faman rarraba idanu akan su, Basarwa Benazir tayi tamkar bata ji me Junaid yace ba sarai ta fahimci ruɗewar da Angel tayi tasan don saboda ita ne kada ta gane wani abu.
Tun da Aneelerh tay gyaran murya junaid ya kalle ta tayi azan zai sanya rigima akan ta ɗauke shi kamar yadda ya sa6a yi ma kowa ƙiwuya amma wani iko na Allah sai ta ga bai yi ba, aranta ta ayyana watakil ya ga ne Angel dince shiyasa ya yarda da ita, miƙa hannu Batool tay da niyar ta dauke shi Ya maƙe kafaɗa alamar ba zai je ba.
Anila tace"sai kunyi hakuri da shi, baya da koshin lafiya" atare suka haɗa baki gurin furta"Allah ya bashi lafiya" ta amsa masu da ameen
"Kana buƙatar wani abu"? Cikin kulawa unaisah tay maganar tana kalon fuskar shi Ya nutsu Yana ta kallonta
"Batool zubo mashi juice a cup" unaisah ta fada tare da kallon ta da sauri batool ta ɗauko juice din da dr shureim Ya aje a cup bai sha ba ta miƙa wa Angel ta kar6a ta kanga mashi abaki A hankali ya fara sha.
"Naji shiru yaya shureim bai dawo ba" ta faɗa tare da kallon Anila
"May be bai kammala Yin wayar ba" acewar Anila
Sauke ajiyar zuciya ta ɗanyi har yanzu da sauran damuwa akan fuskarta.
Wrist watch din hannunta ta duba karfe ɗaya da rabi
"Bansan lokaci yaja har haka ba," Anila tace"nasan mami zata neme ni"
"Batasan kin fito bane"?
Ta sani amma ce mata nayi gidan ku zanje"
Da zolaya Benazir tace"Mai karya dan wuta dai," dariya Anila tay..
"Naji shirun yayi yawa, bari naje na duba Ya shureim" ta faɗa tare da miƙewa ta fuce daga dakin
Ajiyar zuciya Aneelarh ta sauke tare da kallon su Unaisah, Hankalinta Ya kwanta da ganin yadda junaid Ya saki jiki da ita.
"Aunty Anila ki bani wayarki mu dauki hoto, Na bar nawa a daki.'
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Okay" ta faɗa tare da zaro wayar tace"bari nayi maku pics din da kaina, ku gyara" hotuna ta fara ɗaukar su kala kala wani daga zaune wani daga tsaye wani kuma sukayi atare su uku junaid dai yana a maƙale da Unaisah Batool tay kwakwar ta ɗauke shi Yaƙi yarda da ita, bayan sun gama ɗaukar hotunan Anila ta ɗibi snacks a dan plate ta ba unaisah" ki bashi yaci, da safe baici abincin kirki ba" kar6ar plate din tay ta fara bashi abaki Yana ci.
Lokacin da Benazir ta fito waje neman Dr shureim A tsaye ta hango shi jikin Motar shi yana yin waya, da sauri ta nufe shi adai dai time din ya kammala yin wayar"ya shureim lafiya naga ka dade baka dawo ba" fuskar shi babu walwala Ya ce"Zeenatu ce ta kira ni da layin tani, tana kuka bata jin dadin jikin ta tace inzo gida tana son gani na"
"Baiwar Allah, dole taji ba daɗi ya shureim, Banji dadin yadda Uncle yake takura rayuwarta, ni nasan hada damuwar hakan"
ta fada cikin sanyin murya tana kallon shi
"Ka tafi ya shureim, Inyaso sai mu tsaida me abun hawa Ya kai mu gida" girgiza kai yai"a'a bazan iya tafiya nabarku ba, zan bata hakuri ta jira zuwa lokacin da zamu koma gida" ya fada yana kokarin danna mata kira da sauri Benazir ta ruƙe hannun shi amarairaice ta furta"a'a ya shureim kada ay haka, tunda kaga ta kira ka da akwai wani abu dake damunta, tana son ganinka, kuma kaima nasan hankalin ka bazai kwanta ba in har ba zuwa kai gurin ta ba..."
shiru ya yi jimm yana nazarin maganarta, aranta Allah Allah take Ya tafi duk don saboda ta samu taj yace zai kaisu a motar shi
ɗagowa yai da ido Ya dube ta"zan tafi amma zan dawo zuwa anjima in ɗauke ku" Amsa mashi tay da toh ka kula min da kanka" murmushi ya ɗanyi mata harga Allah baiso tafiyar shi ba, saboda yarinyar nan mai kama da shi ta tsaya mashi aranshi.
Akan idon Benazir motar dr shureim ta fuce daga gidan, nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tare da duƙar da kanta ƙasa, damuwa ce cunkushe a cikin zuciyarta, ga dai yarta Allah ya nuna mata da ranta da lafiyarta kuma tayi farin ciki mara misaltuwa sai dai bata jin zata samun sukuni da kwanciyar hankali in har taj bai yafe mata ba, har yanzu tana son mijinta kuma bata jin zata iya rayuwa da wani ɗa namiji a duniyar nan in ba shi ba, zurfin tunani ta shiga da ace tun farko da ya aureta sunyi zaman lafiya zai iya yi mata uziri amma Yanzu koda yaji cewa Asiri akai mata ta gudu tasan bazai ta6a yarda ba saboda yasan wacece ita
Cikin karyayyar murya ta furta"Halina ne Yaja min, Ni na ja ma kaina..."
batai aune ba taji safkar hawaye kan kuncin ta, da sauri ta sanya tafin hannu ta share ƙwallar, kafin ta juya ta nufi hanyar koma wa sitting room din tana ta ƴan waige waige cike da sa ran zata ga 6ullowar taj sai dai har ta shiga babu shi babu alamar shi...
__________Ummin America
Futowa tay daga bedroom din ta jikinta sanye da bubu gown ta material, tay rolling akanta, flat shoes ne a kafarta, matsawa tay gaban handrail ta dafa tana kallon downstairs, A falo ta hango su gaba ɗayan su banda mutun uku, kowan nan su yana azaune kan rug sun haɗa kai suna rubutu a cikin notebooks din su, Sajeed ne kadai ya zauna kan sofa da alama shi ke koya masu rubutun.
Zura hannayenta tay acikin aljihun rigarta, ta nufi stairs cikin nutsuwa take taka matakalar ta sauko down ta nufe su babu wanda Ya lura da ita a cikin su har sai da tay masu gyaran murya tukunna suka dago da kai suka kalle ta har suna haɗa baki gurin furta"Aunty Ummi zo ki ga Rubutun mu, Ki za6i nawa yafi kyau" kusan atare suke mike tare da kewayeta kowa Ya miƙa mata notebook din shi.
ƙin kar6a tay gudun kada ta haɗa rigima kallo ɗaya da tai ma rubutun su sai da taji gaban ta ya faɗi ganin wani jagwalgwalo, a fakaice ta kalli sajeed karaf suka haɗa ido da juna da sauri Ya kumshe dariya yai mata alamar ta duba mana.
"Aunty ummi nawa zaki fara dubawa, nafi su abun kirki"
Jemimah ce ke rokon ta, kar6ar book din tay tare da duba rubutunta itace ke yin rubutu shigen na thailand ka rasa ta yadda take jagwalgwala shi
"Aunty ummi in kin gama duba nata saura nawa" acewar Azeeza, Deeja tace"wlh na riga ki nawa zata duba" kamar zasu sanya mata rigima.
Jinjina kai ta yi"Jemimah Kinyi ƙoƙari ki dage kin ji, idan kika maida hankali har kyauta zanyi maki" uban tsalle ta daka na murna hada yi ma Azeeza gwalo ta kar6i notebook dinta tana ta murna
"Muga naki azeeza' mika mata tay aranta ta ayyana tab lallai wlh da a school suka rubuta Iya shegen nan, jakkin duka zasu ci' amma a fili sai ta ɗan murmusa tace"kema kinyi kokari, Ki ƙara himma" dadine Ya lullu6e azeeza ta kar6i book dinta ta juya ta nufi jemimah.
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
Ɗaya bayan ɗaya saida ummi ta duba notebooks din Har ƙwara Naufal Ya iya rubuta ba laifi tayi mamaki har saida ta tambaye shi ya akai yafi su iyawa, Da hannu ya nuna mata Sajeed"kullum A ɗaki kafin mu kwanta bacci, Shi yake koya min rubutu da karatu..." jinjina kai tay"Sajeed sannu da kokari, amma yakamata suma sauran ka dage da koya masu kamar yadda kake koya ma naufal" amsa mata yai da toh.
Deeja sai haɗe rai take don ba'a yabi nata ba, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"rubutun ma bazan ƙara yi ba" ta faɗa tana kokarin keta littafin da sauri Haris Ya ruƙe hannunta"wayace maki rubutun baiyi kyau ba, ay naki yafi na kowa" kwa6e fuska tay tare da kallon Aunty Ummi tana faman zum6ura baki tace"amma ayni baki yabi nawa ba ko" yar dariya ummi tay"oh wai saboda ni zaki keta littafin, toh kiyi hakuri mantawa nayi amma naki yafi na kowa" washe baki tay har taji dadi..
"Ni rubutun ma yai kyau ko kar yayi ba damuwa ta bace, indai ba za'a hanani cin abinci ba" ta faɗa tana hura hanci, gaba ɗaya suka sanya dariya, girgiza kai Ummi tay"Allah ya shiryeki foodie, ke dai indai zaki samu abinci baki da sauran damuwa" ɗaga mata gira tay.
Sarah da ta gama haɗe rai wurga notebook dinta tay kan sofa ta juya zata tafi
"Hey! Where are you going?' muryar ummi ce ta katse mata hanzarin ta, yamutsa fuska tay"nagaji da rubutunne zanje na kwanta" murmushi ummi tay"nasan me kike ma fushi don ban yabi rubutunki ba ko" girgiza kai tay"a'a kawai nagaji ne" daga yanayinta ummi ta fahimci zatai rawar kawai dama tana lura da ita, ta iya raina abu in baiyi mata ba.
"Okey, kije ki kwanta ki huta, da anjima, da kaina zan koya maku rubutun"
"Okay, thanks" ta faɗa tare da juyawa ta nufi dakin su tana tafiya kamar zata balle tsabar tsawon ta har yanzu bata da ƙiba.
"Kuma idan kun gaji ku aje karatun, kwakwalwa tana buƙatar hutu, amma fa dole ku dage ilmi yana da matuƙar amfani, you have to endure and persist before you succeed." ta6e baki parvin tay"Allah aunty ummi da kin daina wahalar da kanki gurin yi mana bayani, bamu gane komai.." sakin baki tay sototo tana kallon parvin abun ban haushi abun dariya
Rubina tace"nima Allah bani ganewa, Nifa nafison in kwanta inyi bacci ko inci abinci" kallon ta ummi tay
Hibba tace"dama girki kika koya mana, da yafi, kin ga sai mu dinga girka abun da ran mu yake so"
Tun da Aneelerh tay gyaran murya junaid ya kalle ta tayi azan zai sanya rigima akan ta ɗauke shi kamar yadda ya sa6a yi ma kowa ƙiwuya amma wani iko na Allah sai ta ga bai yi ba, aranta ta ayyana watakil ya ga ne Angel dince shiyasa ya yarda da ita, miƙa hannu Batool tay da niyar ta dauke shi Ya maƙe kafaɗa alamar ba zai je ba.
Anila tace"sai kunyi hakuri da shi, baya da koshin lafiya" atare suka haɗa baki gurin furta"Allah ya bashi lafiya" ta amsa masu da ameen
"Kana buƙatar wani abu"? Cikin kulawa unaisah tay maganar tana kalon fuskar shi Ya nutsu Yana ta kallonta
"Batool zubo mashi juice a cup" unaisah ta fada tare da kallon ta da sauri batool ta ɗauko juice din da dr shureim Ya aje a cup bai sha ba ta miƙa wa Angel ta kar6a ta kanga mashi abaki A hankali ya fara sha.
"Naji shiru yaya shureim bai dawo ba" ta faɗa tare da kallon Anila
"May be bai kammala Yin wayar ba" acewar Anila
Sauke ajiyar zuciya ta ɗanyi har yanzu da sauran damuwa akan fuskarta.
Wrist watch din hannunta ta duba karfe ɗaya da rabi
"Bansan lokaci yaja har haka ba," Anila tace"nasan mami zata neme ni"
"Batasan kin fito bane"?
Ta sani amma ce mata nayi gidan ku zanje"
Da zolaya Benazir tace"Mai karya dan wuta dai," dariya Anila tay..
"Naji shirun yayi yawa, bari naje na duba Ya shureim" ta faɗa tare da miƙewa ta fuce daga dakin
Ajiyar zuciya Aneelarh ta sauke tare da kallon su Unaisah, Hankalinta Ya kwanta da ganin yadda junaid Ya saki jiki da ita.
"Aunty Anila ki bani wayarki mu dauki hoto, Na bar nawa a daki.'
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Okay" ta faɗa tare da zaro wayar tace"bari nayi maku pics din da kaina, ku gyara" hotuna ta fara ɗaukar su kala kala wani daga zaune wani daga tsaye wani kuma sukayi atare su uku junaid dai yana a maƙale da Unaisah Batool tay kwakwar ta ɗauke shi Yaƙi yarda da ita, bayan sun gama ɗaukar hotunan Anila ta ɗibi snacks a dan plate ta ba unaisah" ki bashi yaci, da safe baici abincin kirki ba" kar6ar plate din tay ta fara bashi abaki Yana ci.
Lokacin da Benazir ta fito waje neman Dr shureim A tsaye ta hango shi jikin Motar shi yana yin waya, da sauri ta nufe shi adai dai time din ya kammala yin wayar"ya shureim lafiya naga ka dade baka dawo ba" fuskar shi babu walwala Ya ce"Zeenatu ce ta kira ni da layin tani, tana kuka bata jin dadin jikin ta tace inzo gida tana son gani na"
"Baiwar Allah, dole taji ba daɗi ya shureim, Banji dadin yadda Uncle yake takura rayuwarta, ni nasan hada damuwar hakan"
ta fada cikin sanyin murya tana kallon shi
"Ka tafi ya shureim, Inyaso sai mu tsaida me abun hawa Ya kai mu gida" girgiza kai yai"a'a bazan iya tafiya nabarku ba, zan bata hakuri ta jira zuwa lokacin da zamu koma gida" ya fada yana kokarin danna mata kira da sauri Benazir ta ruƙe hannun shi amarairaice ta furta"a'a ya shureim kada ay haka, tunda kaga ta kira ka da akwai wani abu dake damunta, tana son ganinka, kuma kaima nasan hankalin ka bazai kwanta ba in har ba zuwa kai gurin ta ba..."
shiru ya yi jimm yana nazarin maganarta, aranta Allah Allah take Ya tafi duk don saboda ta samu taj yace zai kaisu a motar shi
ɗagowa yai da ido Ya dube ta"zan tafi amma zan dawo zuwa anjima in ɗauke ku" Amsa mashi tay da toh ka kula min da kanka" murmushi ya ɗanyi mata harga Allah baiso tafiyar shi ba, saboda yarinyar nan mai kama da shi ta tsaya mashi aranshi.
Akan idon Benazir motar dr shureim ta fuce daga gidan, nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tare da duƙar da kanta ƙasa, damuwa ce cunkushe a cikin zuciyarta, ga dai yarta Allah ya nuna mata da ranta da lafiyarta kuma tayi farin ciki mara misaltuwa sai dai bata jin zata samun sukuni da kwanciyar hankali in har taj bai yafe mata ba, har yanzu tana son mijinta kuma bata jin zata iya rayuwa da wani ɗa namiji a duniyar nan in ba shi ba, zurfin tunani ta shiga da ace tun farko da ya aureta sunyi zaman lafiya zai iya yi mata uziri amma Yanzu koda yaji cewa Asiri akai mata ta gudu tasan bazai ta6a yarda ba saboda yasan wacece ita
Cikin karyayyar murya ta furta"Halina ne Yaja min, Ni na ja ma kaina..."
batai aune ba taji safkar hawaye kan kuncin ta, da sauri ta sanya tafin hannu ta share ƙwallar, kafin ta juya ta nufi hanyar koma wa sitting room din tana ta ƴan waige waige cike da sa ran zata ga 6ullowar taj sai dai har ta shiga babu shi babu alamar shi...
__________Ummin America
Futowa tay daga bedroom din ta jikinta sanye da bubu gown ta material, tay rolling akanta, flat shoes ne a kafarta, matsawa tay gaban handrail ta dafa tana kallon downstairs, A falo ta hango su gaba ɗayan su banda mutun uku, kowan nan su yana azaune kan rug sun haɗa kai suna rubutu a cikin notebooks din su, Sajeed ne kadai ya zauna kan sofa da alama shi ke koya masu rubutun.
Zura hannayenta tay acikin aljihun rigarta, ta nufi stairs cikin nutsuwa take taka matakalar ta sauko down ta nufe su babu wanda Ya lura da ita a cikin su har sai da tay masu gyaran murya tukunna suka dago da kai suka kalle ta har suna haɗa baki gurin furta"Aunty Ummi zo ki ga Rubutun mu, Ki za6i nawa yafi kyau" kusan atare suke mike tare da kewayeta kowa Ya miƙa mata notebook din shi.
ƙin kar6a tay gudun kada ta haɗa rigima kallo ɗaya da tai ma rubutun su sai da taji gaban ta ya faɗi ganin wani jagwalgwalo, a fakaice ta kalli sajeed karaf suka haɗa ido da juna da sauri Ya kumshe dariya yai mata alamar ta duba mana.
"Aunty ummi nawa zaki fara dubawa, nafi su abun kirki"
Jemimah ce ke rokon ta, kar6ar book din tay tare da duba rubutunta itace ke yin rubutu shigen na thailand ka rasa ta yadda take jagwalgwala shi
"Aunty ummi in kin gama duba nata saura nawa" acewar Azeeza, Deeja tace"wlh na riga ki nawa zata duba" kamar zasu sanya mata rigima.
Jinjina kai ta yi"Jemimah Kinyi ƙoƙari ki dage kin ji, idan kika maida hankali har kyauta zanyi maki" uban tsalle ta daka na murna hada yi ma Azeeza gwalo ta kar6i notebook dinta tana ta murna
"Muga naki azeeza' mika mata tay aranta ta ayyana tab lallai wlh da a school suka rubuta Iya shegen nan, jakkin duka zasu ci' amma a fili sai ta ɗan murmusa tace"kema kinyi kokari, Ki ƙara himma" dadine Ya lullu6e azeeza ta kar6i book dinta ta juya ta nufi jemimah.
Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
Ɗaya bayan ɗaya saida ummi ta duba notebooks din Har ƙwara Naufal Ya iya rubuta ba laifi tayi mamaki har saida ta tambaye shi ya akai yafi su iyawa, Da hannu ya nuna mata Sajeed"kullum A ɗaki kafin mu kwanta bacci, Shi yake koya min rubutu da karatu..." jinjina kai tay"Sajeed sannu da kokari, amma yakamata suma sauran ka dage da koya masu kamar yadda kake koya ma naufal" amsa mata yai da toh.
Deeja sai haɗe rai take don ba'a yabi nata ba, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"rubutun ma bazan ƙara yi ba" ta faɗa tana kokarin keta littafin da sauri Haris Ya ruƙe hannunta"wayace maki rubutun baiyi kyau ba, ay naki yafi na kowa" kwa6e fuska tay tare da kallon Aunty Ummi tana faman zum6ura baki tace"amma ayni baki yabi nawa ba ko" yar dariya ummi tay"oh wai saboda ni zaki keta littafin, toh kiyi hakuri mantawa nayi amma naki yafi na kowa" washe baki tay har taji dadi..
"Ni rubutun ma yai kyau ko kar yayi ba damuwa ta bace, indai ba za'a hanani cin abinci ba" ta faɗa tana hura hanci, gaba ɗaya suka sanya dariya, girgiza kai Ummi tay"Allah ya shiryeki foodie, ke dai indai zaki samu abinci baki da sauran damuwa" ɗaga mata gira tay.
Sarah da ta gama haɗe rai wurga notebook dinta tay kan sofa ta juya zata tafi
"Hey! Where are you going?' muryar ummi ce ta katse mata hanzarin ta, yamutsa fuska tay"nagaji da rubutunne zanje na kwanta" murmushi ummi tay"nasan me kike ma fushi don ban yabi rubutunki ba ko" girgiza kai tay"a'a kawai nagaji ne" daga yanayinta ummi ta fahimci zatai rawar kawai dama tana lura da ita, ta iya raina abu in baiyi mata ba.
"Okey, kije ki kwanta ki huta, da anjima, da kaina zan koya maku rubutun"
"Okay, thanks" ta faɗa tare da juyawa ta nufi dakin su tana tafiya kamar zata balle tsabar tsawon ta har yanzu bata da ƙiba.
"Kuma idan kun gaji ku aje karatun, kwakwalwa tana buƙatar hutu, amma fa dole ku dage ilmi yana da matuƙar amfani, you have to endure and persist before you succeed." ta6e baki parvin tay"Allah aunty ummi da kin daina wahalar da kanki gurin yi mana bayani, bamu gane komai.." sakin baki tay sototo tana kallon parvin abun ban haushi abun dariya
Rubina tace"nima Allah bani ganewa, Nifa nafison in kwanta inyi bacci ko inci abinci" kallon ta ummi tay
Hibba tace"dama girki kika koya mana, da yafi, kin ga sai mu dinga girka abun da ran mu yake so"