← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 122 OF 238

Sashe 122

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hajiya sarah tace"ni nama rasa ta cewa wlh, amma ni aganina, abun da yakamata shine mu lalla6ata mu fada mata cewa daddyn yarinyar yazo ya dauke ta sun tafi mall, da anjima zai dawo da ita, saboda mu samu mu bar hospital ɗin da ita, in ba haka ba dakyar zata amince ta bi mu" gaba daya sunyi amanna da maganar hajiya sarah, atare suka nufi dakin, suna shiga suka isketa zaune gefen gado duk ta yamutse gashin kanta kamar na mahaukaci, ga fuskarta sharkaf da ruwan hawaye.

Atare suka hada baki gurin yi mata sallama, da sauri ta miƙe tana kallonsu, muryarta na rawa ta furta"mami! Ya shureim! Daddy! aunty Sarah! Ina babyna? Tana ina? Na duba ko'ina banganta ba! Dan Allah ku fadamin waya daukar min babyna? Wlh in har ba'a dawo min da itaba, zuciyata zata buga in mutu kowa ya huta"!

kusan atare suka haɗiyi yawu kowa yasha jinin jikinshi, dakyar hajiya Sarah tayi karfin halin furta"haba Benazir? Meyasa zaki daga hankalinki akan yarki? Waya isa Ya rabaki da ita? Ki kwantar da hankalinki, Yarinyar nan takice halak malak.."bubbuga kafafunta tayi saika rantse da Allah batasan me take ba, bayan da hankalinta tsabar pretending ne

"Ni kawai ku fadamin tana Ina? Meyasa banganta ba"?

"Benazir, daddynta ne ya dauke ta, sunje mall zasuyi maki siyayya da anjima zai dawo da ita gida..." cike da fargaba hajiya layla tayi maganar, shiru tayi jimm na ɗan wani lokaci kafin ta sauke nannauyar ajiyar zuciya fuskarta ayamutse tace"mami dagaske Taj yazo nan? Shi ya dauki Angel dina"? Murmushi suka sakar mata, dr shureim yace"kwarai kuwa dagaske shiyazo ya dauketa.."

"Amma bai tambayeni ba? Ko ya daina sona? Ta fada tana zare masu eyes dinta

Alhaji ubaid yace"ya tambayeki mana, ay saboda ke sukaje yin siyayyar, yana son ya faranta miki rai.." wani irin tsallan murna ta daka tana dariya.

kallon kallo su hajiya layla suka jefawa junansu hankalinsu atashe, wato akwai gwarama idan suka koma gida taji shiru taj baizo mata da yarta ba.

"Mommy zamu jiraku a mota" dr shureim ya fada tare da kallon daddynsu atare suka fuce,

Badajimawa ba, saiga su sun fito tare da benazir har ta canza kayan jikinta ta maida kayan da aka kawota asibitin da su, a backseat na motar dr shureim ta zauna, yana agaba tare da alhaji ubaid, Hajiya layla kuma a motar hajiya sarah ta zauna, a jere motocin suka fuce daga asibitin.

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK

COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:06 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe page 40 Complete
by
Novels Elite Admin
September 03, 2024
Sponsored Link
Takun Ƙarshe
Ex-Prisoners💓

Gaba ɗayan su suna zaune kan sofas na falo.

"Aunty ummi wai yaushe angel dinmu zata dawo gida ne? Jemimah ce ta faɗa tana faman haɗe fuska.

Sajeed yace"ni ma na damu da rashin dawowarta gashi tun jiya ko awaya bata kira munji muryarta ba.."

Batool tace"dan Allah aunty ummi ki kira mana ita mu gaisa, ko hankalinmu ya kwanta" tayi maganar tana kallon Ummi, gaba ɗaya hankalinta yana akan wayar hannunta da alama chatting takeyi batasan ma me suke cewa ba..

"Dama kun daina wahalar da kanku gurin yi mata magana, saboda hankalinta ba akanku yake ba.." acewar Parvin.

ɗaga murya batool tayi"Aunty Ummi..." aɗan firgice ta ɗago da ido tana kallon ta"batool! Lafiya kike kwala min kira kamar baki san ina akusa ba"? Dariya su naufal sukayi

Batool ta marairaice mata fuska"aunty ummi muna ta yi maki magana kin yi shiru baki amsa mana ba.." maida hankali tayi akansu

"Okey, Ina sauraronku lafiya"?

Kafin wani ya furta magana acikinsu ba zato ba tsammani, sallamar Unaisah Ta katse masu hanzarin su, kusan atare suka miƙe da gudun gaske suka nufeta hada masu tuntu6e garin sauri, Batool ce ta fara karasawa gareta ta faɗa jikinta suka rungume juna kamar zasu koma mutun ɗaya sai faman tikar dariyar murna sukeyi, gaba ɗaya sukayi mata rumfa kamar zasu lasheta yadda kasan sunyi shekara basu ganta ba,

Bayan ta raba jikinta daga na Batool, tabi su ɗaya bayan daya tayi hugging din yan mata, sajeed Ya buɗe hannu zai rungumota tayi saurin ja da baya tunawa da maganar aunty ummi itafa yanzu tsoran hada jikinta da namiji take yi saboda gudun kada ta samu ciki.

*_______________________________Daga Alƙalamin Boss Bature🔥✍️*

Bayan ta raba jikinta daga na Batool, tabi su ɗaya baya daya tayi hugging din yan mata, sajeed ya buɗe hannu zai rungumota tayi saurin ja da baya tunawa da maganar aunty ummi itafa yanzu tsoran hada jikinta da namiji take yi, gani take kamar ciki zai shiga, har naufal ya kai hannu zai yi hugging dinta again ta ƙara ja da baya hadi da girgiza kan ta, mamaki ne ya kama su Naufal ganin yadda ta hana su ta6a ta kamar taga wani mugun abu.

"Meyasa mu bazaki rungume mu ba, ko bakiyi kewarmu ba"? murmushi ta sakar masu"kuyi hakuri ba haka bane, nayi missing dinku gaba ɗayanku.." girgiza kai sajeed yayi ni ban yarda ba Allah, naufal yace"kinfi son su batool shiyasa kika rungumesu ko"? Javed ma yace"ni banji dadi ba, wariya kike nunawa atsakanin mu.." gwalo parvin tayi masu, Sarah tace"nan fa ba prison bane, mun riga da mun gane jinsin mu, ku maza mu mata don haka kuyi hakuri no more hugs atsakanin mu ehe" dariya suka sanya.

Batool tace"bayan haka aunty ummi ta fada mana babu kyau mace ta rungume namijin da ba muharramin ta ba, koda ruke hannunsa ne" wani irin farin ciki ne Ya lullu6e Unaisah dake sauraronsu taji dadin yadda suka fara gane abunda ake koya masu.

Gaba daya kalamansu akan kunnan chief dake abakin kofar shigowa falon maganar Batool ta faranta ranshi dama yajima yana son a fahimtar dasu game da mannewa juna da sukeyi amma yanzu alhamdulililah sun fara hankali

Mubeen yace"amma ay a prison mu na yi kuma baku ta6a hana mu ba"

Harara Parvin ta watsa mashi"ay lokacin muna a jahiliya period ne, yanzu kan mage ya waye..."

maganarta ta basu dariya, fashewa ummi tayi da dariya ashe tana tsaye abayansu.

Unaisah na ganinta tayi sauri nufarta suka rungume juna

"Oyoyo my babe Unaisah, welcome back home munyi kewarki abar kaunarmu"

"Nima nayi kewarku aunty ummi fatan na same ku lafiya..." ta fada tare da dago da kanta

"Lafiyalou Unaisah, ya jikin patient din? Ko har an sallame ta"!

"Yau za'a sallame shiyasa na taho gida, taji sauƙi sosai, tama ce in gaishe mata da ku" murmushi ummi tayi"Allah sarki muna amsawa, wlh naji dadin samun lafiyarta..."

Kallon su Naufal tayi sun haɗe fuska babu annuri duk don saboda taƙi hugging dinsu, jemimah ta tuntsire da dariya tana fadin wai ma haushi suke ji don kinki rungumarsu jibar su ma kattai da su.."bata ƙare maganar ba, Sajeed Ya tallabi keyarta nan take ta fara ta6e baki zatayi kuka,

Naufal Ya ɗaga hannu zai buge bakin da sauri ummi ta ruƙo hannun shi tana dariya tace"ya isa haka pls, wasa takeyi maku"

"Pls Angel, To mu gaisa da hannu" Sajeed Ya fada tare da mika mata hannu shi, shiru tayi jimm har ta miƙa hannu zata ruko nashi ba zato ba tsammani chief ya shigo falon yayi hanzarin daura hannunshi akan na Sajeeed, gaba daya suka shiga nutsuwarsu sam basu san da zaman shi ba.

cikin girmamawa suka fara gaishe da shi, ummi ma ta gaida shi ya amsa mata, Sajeed baki ya ki rufuwa saboda sunyi musabaha da chief, yaƙi sakar mashi hannu.

"Pls chief can you hug me"? Ɗaga mashi gira chief yayi tare da yin huggin dinshi, wani irin dadi ya lullu6e shi.

"Nima pls" acewar Naufa, miƙa mashi hannu yai da sauri naufal ya rungume chief harwani bude hanci yakeyi yana shakar kamshin turaren shi

Kunya ta hana Haris yin magana, lura da hakan yasa chief mika mashi hannu da sauri ya matsa kusa da shi suka rungume juna, bayan ya saki haris Ya rungume javeed da mubeen wayyo dadi, tsabar murna kamar anyi masu albishir da gidan Aljanna, Ummi sai satar kallonshi takeyi saboda kyan da yayi mata, kai ko amafarki bata ta6a tsammanin zata haɗu da chief face to face ba sai gashi cikin ikon Allah ƙaddara ta haɗa ta zama da shi agida ɗaya, ta yaba da hankalinshi, nutsuwarshi, wayewarshi, saukin kanshi da ilminsa komai Allah Ya bashi uwa uba ga tarin Dukiya.

Gaba ɗaya yan matan sun ɗaure fuska, ganin su naufal sun fara yi masu gwalo saboda chief ya rungumesu..." bubbuga ƙafa Jemimah tayi muryarta da shagwa6a tace"wayyo Allah, mu ma dan Allah yaya chief ka rungumemu..." dariya sajeed yayi tare da cewa"no bazai rungumeku ba, jinsin ku daban namu daban, kowa ya rungumi jinsinsa koba haka ba guys"? Ya fada cike da shakiyanci yana kallon su Javed,
Chapter 122 · 0% Book details