← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 101 OF 238

Sashe 101

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ruƙo hannun shi chief yayi da niyar su fita daga toilet din don Ya duba lafiyar shi, da sauri Danish Ya fuzge hannun shi, dakyar sautin voice dinsa ke fita

"I don't want to see anyone! Just leave me alone! ka tafi kawai..."

"No bazan iya ƙyale ka ba, Idan kai baka damu dakanka ba, Ni na damu dakai, Please, Danish, let's go treat your nosebleed."

Girgiza kai Danish yayi"bana so, lafiyata qalou, zan kula da kaina, kawai ka tafi ni bana son ganin ka.. "

"Ni kuma ina son ganinka, ba inda zan tafi, in kaga nabar dakin nan to ka samun sauƙin abun da ke damun ka ne" babu wasa a fuskarsa yayi maganar tare da harɗe hannayensa kan kirjin shi, kallon kallon suka fara jefawa junan su, chief ya rasa yanda zaiyi da shi, yaron yafiye taurin kai ga kafiya, da ƙiwuya kamar yaron goye ...

Ƙwara ya lalla6a shi su wanye lafiya, idan ba haka ba zai iya illata kan shi..

Cikin sigar lallashi Yace"pls Danish, ka bani damar da zan baka kulawa, ba cutar dakai zanyi ba, bana jin dadin ganinka a halin da kake a ciki, na damu dakai Danish, ina jinka tamkar ɗan uwana, A shirye nake dana taimaka maka wurin ganin mun shawo kan abunda ke damun ka."

tun da chief ya fara magana cikin sanyin murya, Danish ya nutsu yana sauraron shi kamar yana fahimtar shi.

"Nayi maka alƙawarin ba zaka ta6a dana sanin yarda dani ba...." bai ƙare maganar ba, raunanniyar muryar danish ta katse mashi hanzarin shi"bazan ta6a yarda dakai ba, ƴan uwana kadai na yarda da su, amma ku ba abun yarda bane! duk halin ku ɗaya, kuna da son zuciya, ba ku da tausayi, Tun ina jariri na taso rayuwata a gidan kurkukun ƙaddara, bansan komai dangane da duniyarku ba, saboda an tauyemin hakkin rayuwata, ina da ciwon zuciyar abun da iyayena suka aikata min, bansan wani jin dadi na duniya ba, unaisah itace farin cikina......." wasu zafafan hawaye ne suka wanke fuskarshi, zuciyar chief ta karaya, baisan sa'adda hawaye suka cika idanun shi ba, sambatun Danish sun ta6a zuciyar shi, shi kanshi baisan Yana furta kalaman ba, rashin Angel ya fara zautar da shi, dama kuma abun ya jima yana ci mashi tuwo a kwarya.

Da sauri chief Ya ƙara huggin dinshi tighly a kirjin shi, kamar zasu koma mutun ɗaya, a hankali yake shafa bayanshi da tafukan hannayen shi cikin kwantar da murya ya soma yi mashi raɗa a kunanshi

"Danish ba duka muka taru muka zama ɗaya ba, ina rokon alfarma a wurinka, ka jarabani nayi maka alkawarin zan sanya farin ciki acikin rayuwarka, inaso na samu kusanci dakai, saboda na share maka hawayenka in kuma baka kulawa, bayan haka zanyi kokarin sasanta tsakaninka da ƴar uwarka unaisah duk da bansan meya faru atsakaninku ba"

Cikin sanyin murya ya furta"tayi fushi dani, ta daina sona, nasan ban kyauta mata ba, amma bayin kaina bane, ina so na bata hakuri koda ba zata cigaba da kula ni ba, ni burina ta yafe min kada ta ruke ni a zuciyarta, hukuncin yayi min tsauri bazan iya jure ba...ka taimaka min dan Allah..." a karo na farko da Danish Ya ambaci sunan Allah, ba tare da shi kanshi Ya lura da furucinsa ba, lumshe ido chief yayi, wani irin sanyine ya ratsa zuciyar sa, har lokacin suna a rungume da juna, yaji dadin damar daya samu dama burinshi yaja shi a jikin don su samu abunda suke so, yanzu ya samu mafita, ya riga daya gane lagwonsa wato Unaisah, yayi imanin badan sun samu sa6ani atsakaninsu ba, da bazai ta6a samun damar da har Danish zai kula shi ba, murmushin gefen fuska ya saki aranshi ya furta yanzu wasan zai fara🔥

"Zan taimaka maka in sha Allah, zanyi iyakar bakin kokarina gurin ganin kun sasanta tsakaninku, amma fa sai ka yi hakuri ka cire damuwa aranka, yanzu muje ayi maka treatment na bleeding dinka"

"Bani buƙata, zan iya gyara kaina" ya fada tare da raba jikin su daga na juna, ya sanya hannu ya matse hancin shi, nan take jinin ya daina ɗiga.

"Inason zanyi wanka" fita chief yayi daga ɗakin, ya tsaya a bedroom dinsa Yana jiran shi, tufka da warwara ya fara dangane da yadda zai ja shi a jikin shi , yaso yaji meya faru atsakaninsu sai dai ya fahimci baya son sanar dashi, kamar yadda itama unaisan taki sanar da shi, bai damu da hakan ba, saboda shima baison yaji abun da zai hana shi runtsawa kwara atafi ahaka yana dai kyautata masu zato.

Kafin fitowar Danish Ya kira landline na kitchen Ya isar da sakon Yana bukatar breakfast a kawo mashi a dakin Danish

Within 10 mins chef Ya shigo hannun shi ruƙe da tray na kayan abinci har saida gabanshi ya faɗi ganin jinin dake agaban jallabiyar chief bai dai tanka ba, tun da ya gaishe shi Ya sauke masu akan table kafin Ya fice daga dakin.

Harya fara gajiya da tsayuwa, jin motsin buɗe kofa Yasa shi saurin kai idon gare shi, Ya fito fess dashi kamar wani abu bai ta6a faruwa ba, towel ne ɗaure a waist dinshi, tun da ya fito chief yake kallon shi, bai ji dadi zanan tatttoo din da akai mashi ba, daga bayan shi har gaban kirjin shi da damtsen hannun shi zanan waɗannan halittunne masu zako zakon akaifu, launin ja da baƙi bawai don baiyi mashi kyau ba, hasalima kyau zanan yayi mashi sai dai abun da yake jimawa ranar daya musulunta dole yaji ba dadi saboda haramunne zanan tattoo kuma daga gani permanent ne nashi irin wanda bai gogewa, sauƙin shi ɗaya Idan ya musulunta bashi da zunubin komai.

har saida ya nufi closet kafin chief ya kau da ido daga kallon shi, ƙarnin jinin ne Ya fara takura mashi fucewa yayi daga dakin Ya nufi dakin shi, ya canza kayan jikin shi ya sanya wata jallabiyar kafin ya dawo dakin danish.

A zaune ya same shi akan mirror chair ya sanya short da singlet a jikin shi, ya zabga uban tagumi da hannun shi biyu, har yanzu ba yaji shi daidai.

"Danish bismilla, taso muyi breakfast, nasan baka ci komai ba" cikin kulawa yai mashi maganar

In a cool voice Ya furta"bana iya cin komai, Unaisah nakeson gani..." ya yi maganar tare da mikewa Ya nufi kofar fita daga dakin, da sauri chief yasha gabanshi...

"Unaisah bata nan, ko kaje dakin su ba zaka ganta ba"

Hankalin shi atashe ya furta"ta gudu saboda tana fushi dani ko"? Ya fada idanunsa cike tab da kwalla"

Girgiza kai chief yayi"ba abunda kake tunani bane, muje mu zauna I'll explain everything to you.."

Related Books:

Abban Sojoji (Takun Karshe) hausa novels complete - Novels Elite
Daudar Gora complete book 1 Document.
Daudar Gora Book 2 Complete Document
Jiddatul Khair book 1&2 complete

ya ruko hannun shi suka zauna daga gefen gado suna fuskantar junansu..

Calmly chief ya zayyana mashi komai dangane da zuwanta asibiti, bai boye mashi komai ba ...." bawan Allah har cikin ranshi yaji dadi da unaisah ta haɗu da mamanta, sai dai yana jin tsoron ta juya mashi baya tun da ta samu iyayen ta..."

"Angel dina taga mamanta"? Jinjina mashi kai chief yayi,

"Kaima in sha Allah iyayenka zasu bayyana kuma zasu baka farin cikin daka rasa arayuwarka ..." yanayin fuskarshi ne Ya canza zuwa tsantsar 6acin rai.

"Bana son su, bani bukatarsu, bana son ganin su, na tsane su, ni bani da iyaye, unaisah ce gatana" murmushi chief yayi.

"Baka tunanin kaima iyayenka suna kaunarka? Think about it. zai iya yiwuwa wani ne a danginka ya sadaukar dakai ba iyayenka ba, kai da kanka kace tun kana jinjiri aka sadaukar dakai, watakil iyayenka basu san an sace masu kai ba, don ni gaskiya bana tunanin a duniyar nan za'a samu iyayen da zasu haifi kyakkyawan yaro kamar kai su suyi watsi da shi...." shiru Danish yayi baice mashi komai ba, kamar yana nazarin maganar shi, sai dai babu alamun zai fahimce shi.

Cikin dabara chief yacigaba da kwantar mashi da hankali, har ya samu suka ci abinci atare, bayan yayi mashi alkawarin zai kai shi wurin Unaisah amma ya bashi shawarar ya ɗan bata tazara watakil ta sauko daga kan dokin zuciyar da tahau...yace mashi bazai iya ba, baya jin dadi in bata atare da shi, yafi son yaganta akusa dashi ko da bazata kula shi ba.. Akarshe yace mashi da anjima zai kai shi wurinta suga juna in har hankalin shi zai kwanta....

Lokacin da su Batool suka farka har yar rige rigen zuwa dakin unaisah su kayi don suga kota dawo amma suna shiga suka iske babu kowa, Hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba, wasu har sun fara kuka, saida Ummi ta sauko down ta same su zazzaune kan sofas kowannansu Ya zabga uban tagumi kamar masu zaman makoki.

Suna ganin ummi suka nufe ta"aunty ummi har yanzu yar uwarmu bata dawo ba, dan Allah ina taje ne bata fada mana ba"?

Kwantar masu da hankali tayi kafin ta sanar da su inda taje, har suna hada baki wurin fadin aunty ummi dan Allah zamuje asibitin wurinta, harma muga yar uwar chief din muyi mata ya jiki"

"Kuyi hakuri, ba za'a bari kuje ba, ku bari ta dawo kawai, in sha bazata jima ba" rigima suka sanya mata musamman jemaimah da azeeza dakyar ta samu ta shawo kansu har suka hakura.

_______________________________✍️

*OIH*

A hankali ta buɗe idanunta, ta ƙurawa ceilling ido na wani lokaci, kafin ta shafa jikinta da hannunta, jin babu mutun yasa ta yunƙura zata miƙe da sauri hajiya layla ta taimaka mata ta zauna, muryarta na rawa ta furta"wayyo Allah na, mami ina babyna? wa ya dauke min ita? Jiya fa na ganta da ido na, har na rungumeta a kirjina! Ko dai mafarki nayi ne..."? gaba ɗaya tabi ta ruɗe ta ɗaga hankalin ta, dafa kadarta hajiya layla tayi fuskarta da murmushi tace"kwantar da hankalin ki, babyn ki tana nan cikin koshin lafiya kuma tana a tare dake" girgiza kai tayi tana faman zare ido tace"to ay banganta ba! Babu ita ko'ina, wani ya dauke min Angel dina..." ta fada tana laluba bedmattress.
Chapter 101 · 0% Book details