Sashe 76
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kada ki kuskura ki ƙara zuwa ɗakin shi idan ba haka ba Kinsan zan iya komai akanki, har Daddyn naki bazan ƙyale sa ba saina ja masa kunne akanki in har yana son zaman lafiya dani" waro idanu waje tayi tare da ɗagowa tana kallon shi, Ya haɗe rai kai kace ba daga bakinsa maganar take fitowa ba,
Harara ya watsa mata kafin ya juya zai bar ɗakin, durowa tayi daga kan gadon jiki na 6ari tayi saurin shan gaban shi Ya tsaya yana kallonta,
Wani irin kwarjini yayi mata a ido, cikin sanyin murya tace"tunda bakaso bazan ƙara ba, amma dan Allah kada ka ta6a min Daddyna wallahi ina son shi bana son wani abu ya same shi, kuma ay shi baisan alaƙar dake a tsakanina dakai ba shiyasa yace haka..." marairaice masa fuska tayi kamar zata sanya mashi kuka
wani irin kallo taga Yana bin ta da shi, tunawa da abunda Ya faru ɗazu ne Yasa tayi saurin matsawa ta bashi hanya don Ya wuce,
Yana fita daga ɗakin ta sauke ajiyar zuciya, tsoki ta dan ja abun na shi ya fara bata takaici, Wannan wani irin kishi ne? "Jarababbe kawai" ta faɗa tare da samun wuri gefen gadonsu ta zauna tana faman haɗe rai, ta ƙudiri aniyar sai ta koma ɗakin chief yi masa aiki ko ba yau ba sai dai Ya haɗiyi zuciya ya mutu, saboda shi bazata ƙi bin umarnin Daddynta ba duk da tana jin tsoron yace zaiyi mashi wani abu don ta fahimci ba kaine da shi na,
_______________Mahboob
Shigowa gidan yayi bayansa a goye da Baby Junaid, tunda yayi sallama idanunsa suka sauka akansu Zeenatu dake a falon har kusan firgita yayi da ganinta saboda kyanta da yaja hankalinsa, Aneelerh na ganinsa ta miƙe tana faɗin "Oyoyo Baby junaid ɗina, mahboob Ina ka kai min shi tun safe sai Yanzu fisabilillah, halan koma abinci baici ba" ta faɗa tare da kar6ar Junaid ta rungume shi a jikinta, sam babu kuzari a jikinshi kamar bacci ma yakeyi ya farka
Muryarsa tamkar zai fashe da kuka Yace"Mommy, Yaya mahboob bai da tausayi sai da nace masa ni ya dawo dani gida amma yaƙi ya dawo dani, kuma wallahi Allah bazan sake binsa unguwa ba" idanunsa aruntse yake masifa, gaba ɗaya mutanan falon Suka kwashe da dariya hada Benazir da bata jima da fitowa ba, Yaron ba ƙaramin burgesu Yayi ba musamman Zeenatu, duk rashin sakewarta jiki na rawa ta miƙe ta nufi su Aneeleeh tace "Aunty ki bani shi in dauke shi"
Murmushi Benazir tayi "Allah yasa ya yarda rigima ne da shi" miƙa mata shi tayi, abun mamaki jikinshi har 6ari Yake wurin Miƙa ma Zeenatu hannu don ta ɗauke shi Ummi na dariya tace "ɗan ƙwal uba yaga farar fata, da mu mukace masa yazo yadda ransa ya 6aci ɗin nan wlh ba zuwa zaiyi ba" dariya sukai baki ɗaya,
Rungumesa Zeenatu tayi har wani ƙara ƙanƙameta yakeyi, komawa tayi kan sofa ta zauna hannunta akan sumar kan shi
daga bisani mahboob Ya gaishe da su Dr shureim fuskokinsu da fara'a suka amsa mashi, gabatar masu da shi Aneelerhtayi kamar yadda ta gabatar masu da Zahra a matsayin ya'yan uncle dinta,
Sunji dadin karramasu da akayi, ko da lokacin salla yayi Mahboob ne Ya raka Dr shureim masallaci sukayi sallah atare,
Har wuraren karfe shida na marece suna agidan, Dr shureim yaso su tafi Mami ce ta tsaida su saboda abie ya kira waya yace in sunzo su jira su dawo gidan don su gaisa, Bayan dawowar su Abie a falo suka zauna wata sabuwar firar suka soma yi cikin raha hada Uncle ɗan Iya Ya dinga basu labaran ban dariya gaba ɗaya suka cika su da farin ciki, baiwar Allah Benazir daurewa kawai takeyi duk don kada su gane halin da take a ciki, Aneelerh ce da Mami kadai suka san meke damunta, da zarar sun haɗa ido da Aneelerh take yi mata alamar tayi haƙuri, har bayan sallar magrib suna gidan
Lokacin da zasu tafi har bakin motarsu suka rako su baki ɗaya Kamar kar su rabu da juna, musamman benazir da Aneelerh, haka itama Zeenatu da Junaid yaron Ya kwanta mata aranta, har hotuna tayi masu da wayar Dr shureim, ko time ɗin da zai ci abinci ita ta bashi abaki, bayan sunyi sallama da junansu suka tafi, su mami basu daina kallon motarsu ba har suka fuce daga gate din gidan kafin suka koma ciki.
______________
Tun cikin mota Zeenatu ta lura da Yanayin Benazir ta haɗe rai sosai fuskarta tayi jawur Ko magana bata son yi, Ita kaɗai tasan raɗadin da take ji ta ƙosa su koma gida saboda taji zafin 6oye mata gaskiya da Mami tayi,
Motarsu na ƙarasa shiga gida Kamar jira take Dr shureim Yayi parking azafafe ta hankaɗe murfin motar ko yar purse dinta bata dauka ba ta nufi falo,
Hankali a tashe Dr shureim Ya fito Yabi bayanta, Itama Zeenatu ta fito hannunta ɗauke da purse ɗin Benazir ta bi bayansu,
Da karfi take ambaton sunan Mami kamar maƙoshinta zai 6allo, ko sallama batayi ba,
Jiki na 6ari Hajiya layla da Hajiya Sarah suka fito daga dakunan su,
Tunkafin ma tayi magana Hajiya layla ta fahimci meke damunta abun da take gudune Ya faru, dama tun ɗazu take zullumin dawowarsu har kiran Benazir ɗin tayi amma batay picking ba balle har ta samu damar Yin magana da Aneelerh don ta dakatar da ita akan kada ta faɗa mata gaskiyar abun da Ya faru,
"Benazir ba saida nace maki idan kin isa gidan ki kira ni ba? Meyasa bakiyi hakan ba...." a rude Mami ta furta hakan, Cikin shesshekar kuka tace "Nagode ma Allah dana manta ban kira ba, abun da kike 6oye min shi aka faɗa min! Mami meyasa zakiyi min ƙarya akan 6atan mijina da ƴata?" rai a matukar 6ace tay maganar tana kallon cikin idonta,
"Wallahi baku kyauta min ba, kinsan kuwa yadda na ƙwallafa raina akan son ganinsu? Mami why? Why kikai min haka..."
"Dan Allah Kiyi haƙuri Benazir, tayi hakan ne saboda guje ma bacin ranki.." Hajiya Sarah ce ta fara kokarin shawo kanta, Zeenatu dake kuka da gudu ta nufi ɗaki ta shige saboda bata son tashin hankali, Idanunta jawur ta kalli Hajiya Saratu "miye amfanin boyemin da tayi? Bayan dole wata rana zanji awani wuri! Da ace ta faɗamin da yanzu komai ya wuce saboda ba yadda zanyi dole inyi haƙuri ....ni banji daɗi ba Mami wlh baki kyauta min ba...."
Dr shureim Sam Ya kasa magana, tsananin tausayin benazir ne Ya cika sa, baisan Ya akai Aneelerh ta sanar da ita ba,
Kallonshi Benazir tay"Yaya Shureim why? Kaima hada kai aka haɗa baki don 6oye mun gaskiya? Ban ta6a tunanin zakuyi min haka ba..."
"Zanyi maki bayani ki nutsu ki saurare ni...." bai ƙare maganar ba da gudu Benazir ta bar falon ta shige ɗakinta, tana shiga ta maido ƙofa ta datse tabar su atsaye suna kallon kallo,
"Shureim wai wanene Ya faɗa mata? Kuma kana agidan baka dakatar da hakan ba?" cike da damuwa Mami ta faɗa,
"Wallahi Mami bansan komai dangane da wanda Ya faɗa mata ba nasan dai bai wuce Aneelerh, kawai yanzu tun da ta riga ta sani muje mu lallasheta har asamu ashawo kanta,
Babu irin bugun da basuyi ma kofar dakin Benazir ba amma taƙi buɗe masu, tana jiyo sautin muryoyinsu daga waje sunata yi mata magiya akan ta buɗe masu ƙofa,
Tana kuka tace masu dama sun daina wahala saboda bazata bude ba har sai lokacin da ranta yabar gangar jikinta" wannan maganar tay matuƙar ɗaga masu hankali, Mami tun tana lallashinta har takaiga hada mata da ashar amman tayi burus taki buɗewa,
Wuraren ƙarfe tara na dare su Alhaji ubaid suka dawo gidan, nan fa suka tarar da abunda ke faruwa kowa Yayi tsaye kofar ɗakin Benazir in ka cire Alhaji musa wanda tun shigowarsu daya gama sauraran abunda ke faruwa yace su kyaleta in ta gaji zata buɗe kofar, Yana faɗan hakan Ya ƙara gaba abunsa, Babu wanda Yaji dadin maganarsa Hatta Alhaji ubaid yaji zafin Yadda Ya nuna halin ko'in kula akan halin da Benazir ɗin ke ciki, Har wurin ƙarfe 12 na dare ana abu ɗaya don dole suka hakura kowa Ya koma ɗakinshi ransu a jagule ahakan ma babu wanda Ya Iya runtsawa a cikin su..
Dr Shureim Yana Cikin Yin zarya a ɗakinsa kwatsam Ya tuna da shaƙar da ake ma Benazir idan dare Yayi Tabbas Yana ji aranshi za'a Iya kaimata hari duba da halin da take a ciki ba lallai ta iya ta6uka wani abu ba gashi ta datse kofa, Fitowa yai da sauri har Yana tuntu6e garin sauri Ya nufi kofar ɗakin Yay knocking shiru batai magana ba, Cikin sanyin murya yace "Pls idan kina saurarena ki tashi ki kunna karatun alkur'ani kada ki kwana ahaka, Yakamata kiyi hada nafila..." shiru bata tanka masa ba, jikinsa yai mugun sanyi baisan awani hali take a ciki ba, karshe zama yayi a ƙofar ɗakin don baya jin zai iya tafiya yabarta ya ƙwammace ya kwana anan.
____________________________
Sai dare Zahra ta kunna wayarta da Mahboob Ya kawo mata daga wurin gyara, Cike da zumuɗi ta shiga gallery dinta anan taga hotunan da suka ɗauka tare da Unaisah, da sauri ta fito daga ɗakinta ta nufi bedroom ɗin Aneelerh, tana shiga ta sameta a zaune kan prayer mat hannunta ruƙe da cazbaha tana ja yayin da acan ƙasan zuciyarta take tunanin ko ya su Benazir suka isa gida taji shiru bata kirata ba, har kira tay amma ba'ay picking ba,
Jin sallamar Zahra yasa ta ɗago kai ta kalle ta,
"Zahrah me kikeyi har yanzu baki kwanta ba"?
"Taya zan Iya runtsawa bayan ban nuna maki hotunan dinner ba, sai Yanzu na samu damar kunna wayar ma" ta faɗa tare da miƙa mata, Kar6a Aneelerh tayi kafin ta soma bin hotunan da kallo,
Zahra na atsaye tana kallonta, kwatsam taga Aneelerh ta zabura ta miƙe tsaye hannunta na kerma tuni cazbahar ta jima da barin yatsan ta,
A ruɗe ta furta"Zahra wacece wannan Yarinyar da kukai hoto da ita??"
Harara ya watsa mata kafin ya juya zai bar ɗakin, durowa tayi daga kan gadon jiki na 6ari tayi saurin shan gaban shi Ya tsaya yana kallonta,
Wani irin kwarjini yayi mata a ido, cikin sanyin murya tace"tunda bakaso bazan ƙara ba, amma dan Allah kada ka ta6a min Daddyna wallahi ina son shi bana son wani abu ya same shi, kuma ay shi baisan alaƙar dake a tsakanina dakai ba shiyasa yace haka..." marairaice masa fuska tayi kamar zata sanya mashi kuka
wani irin kallo taga Yana bin ta da shi, tunawa da abunda Ya faru ɗazu ne Yasa tayi saurin matsawa ta bashi hanya don Ya wuce,
Yana fita daga ɗakin ta sauke ajiyar zuciya, tsoki ta dan ja abun na shi ya fara bata takaici, Wannan wani irin kishi ne? "Jarababbe kawai" ta faɗa tare da samun wuri gefen gadonsu ta zauna tana faman haɗe rai, ta ƙudiri aniyar sai ta koma ɗakin chief yi masa aiki ko ba yau ba sai dai Ya haɗiyi zuciya ya mutu, saboda shi bazata ƙi bin umarnin Daddynta ba duk da tana jin tsoron yace zaiyi mashi wani abu don ta fahimci ba kaine da shi na,
_______________Mahboob
Shigowa gidan yayi bayansa a goye da Baby Junaid, tunda yayi sallama idanunsa suka sauka akansu Zeenatu dake a falon har kusan firgita yayi da ganinta saboda kyanta da yaja hankalinsa, Aneelerh na ganinsa ta miƙe tana faɗin "Oyoyo Baby junaid ɗina, mahboob Ina ka kai min shi tun safe sai Yanzu fisabilillah, halan koma abinci baici ba" ta faɗa tare da kar6ar Junaid ta rungume shi a jikinta, sam babu kuzari a jikinshi kamar bacci ma yakeyi ya farka
Muryarsa tamkar zai fashe da kuka Yace"Mommy, Yaya mahboob bai da tausayi sai da nace masa ni ya dawo dani gida amma yaƙi ya dawo dani, kuma wallahi Allah bazan sake binsa unguwa ba" idanunsa aruntse yake masifa, gaba ɗaya mutanan falon Suka kwashe da dariya hada Benazir da bata jima da fitowa ba, Yaron ba ƙaramin burgesu Yayi ba musamman Zeenatu, duk rashin sakewarta jiki na rawa ta miƙe ta nufi su Aneeleeh tace "Aunty ki bani shi in dauke shi"
Murmushi Benazir tayi "Allah yasa ya yarda rigima ne da shi" miƙa mata shi tayi, abun mamaki jikinshi har 6ari Yake wurin Miƙa ma Zeenatu hannu don ta ɗauke shi Ummi na dariya tace "ɗan ƙwal uba yaga farar fata, da mu mukace masa yazo yadda ransa ya 6aci ɗin nan wlh ba zuwa zaiyi ba" dariya sukai baki ɗaya,
Rungumesa Zeenatu tayi har wani ƙara ƙanƙameta yakeyi, komawa tayi kan sofa ta zauna hannunta akan sumar kan shi
daga bisani mahboob Ya gaishe da su Dr shureim fuskokinsu da fara'a suka amsa mashi, gabatar masu da shi Aneelerhtayi kamar yadda ta gabatar masu da Zahra a matsayin ya'yan uncle dinta,
Sunji dadin karramasu da akayi, ko da lokacin salla yayi Mahboob ne Ya raka Dr shureim masallaci sukayi sallah atare,
Har wuraren karfe shida na marece suna agidan, Dr shureim yaso su tafi Mami ce ta tsaida su saboda abie ya kira waya yace in sunzo su jira su dawo gidan don su gaisa, Bayan dawowar su Abie a falo suka zauna wata sabuwar firar suka soma yi cikin raha hada Uncle ɗan Iya Ya dinga basu labaran ban dariya gaba ɗaya suka cika su da farin ciki, baiwar Allah Benazir daurewa kawai takeyi duk don kada su gane halin da take a ciki, Aneelerh ce da Mami kadai suka san meke damunta, da zarar sun haɗa ido da Aneelerh take yi mata alamar tayi haƙuri, har bayan sallar magrib suna gidan
Lokacin da zasu tafi har bakin motarsu suka rako su baki ɗaya Kamar kar su rabu da juna, musamman benazir da Aneelerh, haka itama Zeenatu da Junaid yaron Ya kwanta mata aranta, har hotuna tayi masu da wayar Dr shureim, ko time ɗin da zai ci abinci ita ta bashi abaki, bayan sunyi sallama da junansu suka tafi, su mami basu daina kallon motarsu ba har suka fuce daga gate din gidan kafin suka koma ciki.
______________
Tun cikin mota Zeenatu ta lura da Yanayin Benazir ta haɗe rai sosai fuskarta tayi jawur Ko magana bata son yi, Ita kaɗai tasan raɗadin da take ji ta ƙosa su koma gida saboda taji zafin 6oye mata gaskiya da Mami tayi,
Motarsu na ƙarasa shiga gida Kamar jira take Dr shureim Yayi parking azafafe ta hankaɗe murfin motar ko yar purse dinta bata dauka ba ta nufi falo,
Hankali a tashe Dr shureim Ya fito Yabi bayanta, Itama Zeenatu ta fito hannunta ɗauke da purse ɗin Benazir ta bi bayansu,
Da karfi take ambaton sunan Mami kamar maƙoshinta zai 6allo, ko sallama batayi ba,
Jiki na 6ari Hajiya layla da Hajiya Sarah suka fito daga dakunan su,
Tunkafin ma tayi magana Hajiya layla ta fahimci meke damunta abun da take gudune Ya faru, dama tun ɗazu take zullumin dawowarsu har kiran Benazir ɗin tayi amma batay picking ba balle har ta samu damar Yin magana da Aneelerh don ta dakatar da ita akan kada ta faɗa mata gaskiyar abun da Ya faru,
"Benazir ba saida nace maki idan kin isa gidan ki kira ni ba? Meyasa bakiyi hakan ba...." a rude Mami ta furta hakan, Cikin shesshekar kuka tace "Nagode ma Allah dana manta ban kira ba, abun da kike 6oye min shi aka faɗa min! Mami meyasa zakiyi min ƙarya akan 6atan mijina da ƴata?" rai a matukar 6ace tay maganar tana kallon cikin idonta,
"Wallahi baku kyauta min ba, kinsan kuwa yadda na ƙwallafa raina akan son ganinsu? Mami why? Why kikai min haka..."
"Dan Allah Kiyi haƙuri Benazir, tayi hakan ne saboda guje ma bacin ranki.." Hajiya Sarah ce ta fara kokarin shawo kanta, Zeenatu dake kuka da gudu ta nufi ɗaki ta shige saboda bata son tashin hankali, Idanunta jawur ta kalli Hajiya Saratu "miye amfanin boyemin da tayi? Bayan dole wata rana zanji awani wuri! Da ace ta faɗamin da yanzu komai ya wuce saboda ba yadda zanyi dole inyi haƙuri ....ni banji daɗi ba Mami wlh baki kyauta min ba...."
Dr shureim Sam Ya kasa magana, tsananin tausayin benazir ne Ya cika sa, baisan Ya akai Aneelerh ta sanar da ita ba,
Kallonshi Benazir tay"Yaya Shureim why? Kaima hada kai aka haɗa baki don 6oye mun gaskiya? Ban ta6a tunanin zakuyi min haka ba..."
"Zanyi maki bayani ki nutsu ki saurare ni...." bai ƙare maganar ba da gudu Benazir ta bar falon ta shige ɗakinta, tana shiga ta maido ƙofa ta datse tabar su atsaye suna kallon kallo,
"Shureim wai wanene Ya faɗa mata? Kuma kana agidan baka dakatar da hakan ba?" cike da damuwa Mami ta faɗa,
"Wallahi Mami bansan komai dangane da wanda Ya faɗa mata ba nasan dai bai wuce Aneelerh, kawai yanzu tun da ta riga ta sani muje mu lallasheta har asamu ashawo kanta,
Babu irin bugun da basuyi ma kofar dakin Benazir ba amma taƙi buɗe masu, tana jiyo sautin muryoyinsu daga waje sunata yi mata magiya akan ta buɗe masu ƙofa,
Tana kuka tace masu dama sun daina wahala saboda bazata bude ba har sai lokacin da ranta yabar gangar jikinta" wannan maganar tay matuƙar ɗaga masu hankali, Mami tun tana lallashinta har takaiga hada mata da ashar amman tayi burus taki buɗewa,
Wuraren ƙarfe tara na dare su Alhaji ubaid suka dawo gidan, nan fa suka tarar da abunda ke faruwa kowa Yayi tsaye kofar ɗakin Benazir in ka cire Alhaji musa wanda tun shigowarsu daya gama sauraran abunda ke faruwa yace su kyaleta in ta gaji zata buɗe kofar, Yana faɗan hakan Ya ƙara gaba abunsa, Babu wanda Yaji dadin maganarsa Hatta Alhaji ubaid yaji zafin Yadda Ya nuna halin ko'in kula akan halin da Benazir ɗin ke ciki, Har wurin ƙarfe 12 na dare ana abu ɗaya don dole suka hakura kowa Ya koma ɗakinshi ransu a jagule ahakan ma babu wanda Ya Iya runtsawa a cikin su..
Dr Shureim Yana Cikin Yin zarya a ɗakinsa kwatsam Ya tuna da shaƙar da ake ma Benazir idan dare Yayi Tabbas Yana ji aranshi za'a Iya kaimata hari duba da halin da take a ciki ba lallai ta iya ta6uka wani abu ba gashi ta datse kofa, Fitowa yai da sauri har Yana tuntu6e garin sauri Ya nufi kofar ɗakin Yay knocking shiru batai magana ba, Cikin sanyin murya yace "Pls idan kina saurarena ki tashi ki kunna karatun alkur'ani kada ki kwana ahaka, Yakamata kiyi hada nafila..." shiru bata tanka masa ba, jikinsa yai mugun sanyi baisan awani hali take a ciki ba, karshe zama yayi a ƙofar ɗakin don baya jin zai iya tafiya yabarta ya ƙwammace ya kwana anan.
____________________________
Sai dare Zahra ta kunna wayarta da Mahboob Ya kawo mata daga wurin gyara, Cike da zumuɗi ta shiga gallery dinta anan taga hotunan da suka ɗauka tare da Unaisah, da sauri ta fito daga ɗakinta ta nufi bedroom ɗin Aneelerh, tana shiga ta sameta a zaune kan prayer mat hannunta ruƙe da cazbaha tana ja yayin da acan ƙasan zuciyarta take tunanin ko ya su Benazir suka isa gida taji shiru bata kirata ba, har kira tay amma ba'ay picking ba,
Jin sallamar Zahra yasa ta ɗago kai ta kalle ta,
"Zahrah me kikeyi har yanzu baki kwanta ba"?
"Taya zan Iya runtsawa bayan ban nuna maki hotunan dinner ba, sai Yanzu na samu damar kunna wayar ma" ta faɗa tare da miƙa mata, Kar6a Aneelerh tayi kafin ta soma bin hotunan da kallo,
Zahra na atsaye tana kallonta, kwatsam taga Aneelerh ta zabura ta miƙe tsaye hannunta na kerma tuni cazbahar ta jima da barin yatsan ta,
A ruɗe ta furta"Zahra wacece wannan Yarinyar da kukai hoto da ita??"