← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 238

Sashe 52

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Haka zamu zuba mashi ido muna kallon shi? Baka ga yadda Ya matse ta bane? Ko magana takasayi"!

Cikin muryar lallashi Taj Ya dubi Danish dake ta faman zare idanunsa tsabar masifa har ƙanƙance su yakeyi

"Dan Allah kayi hakuri ka sake ta, indai saboda ni ne bazan ƙara taba maka ita ba" Mamaki da al'ajabine Ya kama su Ummi dake kallon Ikon Allah

"Meyasa zaka bashi hakuri? Kaida ƴarka? Tsoron shi kake ji ne"? A harzuke Big guy yai maganar

Taj yace'ba tsoron shi nake ba, fitina ke bana so, idan mukace zamu bi ta karfi da yaji donmu kar6e ta wlh ba zamu iya ba sai dai muja yai mata wata illar kwara mu lalla6a shi' guntun tsoki Big guy yaja, gaba daya haushin danish Ya cika shi, duk da yana tausayin prisoners sai dai ayanzu lamarin danish Ya fara sanya shi kokwanto akansa, gani yake kamar yaron yana da wata muguwar manufa.

Haduwa su Naufal sukayi suna ta yi mashi magiya don Ya sake ta, Amma Ya ƙi sakinta

Suna acikin wannan Halin, a lokacin da basu yi tsammani ba, Sallamar Salsabeel Ta katse su, gaba ɗaya suka dago suna Kallon shi

Ganin shi yasa danish sakin Unaisah tai taga taga zata faɗi da sauri batool ta ruƙota, sai faman haki takeyi tana sauke ajiyar zuciya kamar wadda tasha gudu....

Sunyi tunanin shi kadaine Yazo, kusan atare muryoyinsu khadeeja Ya daki kunnuwansu, tunkafin su karasa shigowa suka fara kokarin tunano su wanene? Saboda sun haddace muryarsu ko tari sukayi za su iya sheda su.

Ɗaya bayan ɗaya suka fara Shigowa bakunansu dauke da sallama, Lokaci ɗaya suka Ci burki suna Kallon su Unaisah dake kallon su, kusan atare zuciyoyinsu ke harbawa da matsanancin karfi, Tsabar rudani da al'ajabi Ya hana su gasgata abunda idanuwansu suke nuna masu, har abada ba zasu ta6a mantawa da muryoyin yan uwansu ba, balle kuma kamannin su da basu ta6a gogewa a idanunsu ba, Kokwanto sukeyi anya kuwa yan uwan sune da suka baro prison ba rai? Ko dai mafarki sukeyi ne? Ko kuwa idanunsu ne suke nuna masu badai dai ba? Tayaya ma haka zata yiwu?

Murza idanunsu suka farayi don su kara tabbatarwa da kansu abun da suke gani dagaske ne ko akasin hakan!

Kamar yadda suke al'jabin ganin su haka suma su Rubina suke kallon su da matuƙar ruɗani akan fuskokin su, babu mai magana acikinsu falon yayi tsit kamar mutuwa ta gifta, har na tsawon mintuna kafin salsabeel Ya fara magana

"Abun da kuke tunani dagaske ne, Ku daina kokwanto, wadannan da ku ke gani ƴan uwanku ne, da kuka baro agidan kurkukun ƙaddara, ni kuma sunana salsabeel ɗan tsohuwa tamira, nasan ba lallai ku shaida kamanni na ba, amma ita Unaisah ta gane ni...." fuskar shi dauke da murmushi ya yi maganar, har lokacin babu wanda ya motsa daga cikin su kamar gumaka, tsantsar tsabar rudani da mamaki ne Ya daure su har suka kasa magana, Hatta khadeeja da take da tabin hankali tayi kasaƙe tana bin su da kallo kamar tana so ta tuna su wanene su ...... .

"Tayaya ma haka zata yiwu? Ni fa nagaza gasgata abun da idanuna suke nuna min, Kaina Ya ƙulle dan Allah ku fahimtar dani, ni dai a iya sanina kafin mu baro gidan kurkukun ƙaddarar amace muka barsu yanzu kuma sai mu gan su da ransu da lafiyar su? dama wanda Ya mutu Yana dawowa ne"? Sajeed ne Ya faɗa fuskarshi da alamun ruɗani

Salsabeel Ya fahimci halin da kowan nan su Ya shiga, In har ba faɗa masu ainihin abunda ya faru yayi ba, toh zaiyi wuya su yarda da bunda suke gani, cikin sanyin murya ya fara ba su labarin abun da ya faru bayan barin su gidan kurkukun ƙaddara......

Waiwaye adon tafiya

Tayaya akai Salsabeel tare da su khadeeja suka ku6uta daga gidan kurkukun ƙaddara!? Bayan a iya sanin mu su deeja sun mutu sakamakon zuciyarsu da ta buga❓❓❓

Bari mu koma baya don jin meya faru?

Suna shiga Cikin Toilet ɗin, Danish Ya datse ƙofar da sihirin shi, ya Janye tukunyar fulawar daga kan ƙofar, nan ta ke ta bayyana duk irin wahalar da suka sha ta ƙi buɗewa shi Bugu ɗaya yayi mata gaba ɗaya ta 6alle murfin ƙarfen ya dare biyu, Sun yi mamaki da al’ajabi yace da su”Ba zai bi su ba, zai tafi da Akwatin kayan su tare da back pack ɗin su, za su tarar dashi a bakin ƙofar da zasu 6ula idan sun ƙarasa” hankalin su bai kwanta da maganar shi ba, gani su ke yi kamar wani mummunan abun zai faru da su idan baya atare da su, ganin sun toge sunƙi tafiya yasa shi Kwantar masu da hankali, daƙyar ya samu su ka Zuƙunna ƙasa tare da kutsa kai ɗaya bayan ɗaya su ke shiga cikin ƙofar da rarrafe, Bayin Allah ga yunwa ga ƙishin ruwa, ga raɗaɗin da zuciyarsu ke yi masu, Ita kanta hanyar da suka biyo Wata uwar ƙura ga yanar girgizo da ƙwari sai hawan masu jiki su ke yi, Amma saboda rashin kwanciyar hankali yasa basu damu da su ba. Babu mai magana acikinsu saboda ƙunar da ran su ke yi masu, Angel ce tai ƙoƙarin tunasar dasu akan suci gaba da ambaton addu’o’in data koya masu ko sun samu sassaucin a wurin Allah, sun ɗau ki shawararta ahaka suka Dinga tafiya da rarrafe babu ƙaƙƙautawa, idan suka gaji su kan ɗan zauna su huta kafin su dasa da wata tafiyar, A ƙalla sun shafe tsawon awanni Takwas suna rarrafawa ba tare da sun kawo ƙarshen Ƙofar ba, a takure su ke Bayin Allah sun ga rayuwa gwiwowin ƙaffuwan su duk sun gurje sun sage, maƙoshinsu ya bushe ƙamas, tun suna ambaton ƙishir ruwa suke ji har sun gaji sun yi shiru.........”😭

A tsugunne yake gaban gawar tsohuwa tamira, yayin da hawaye ke sintiri kan fuskarsa, idanunsa sun kaɗa jawur da su, zuciyarshi ta gama karaya, tamkar baya a cikin hayyacin shi, gaba ɗaya rayuwar duniyar ta sire mashi, duk sai yaji ya tsani kanshi, bai da wani buri daya wuce shima Ya mutu, sai dai baya son ya mutu batare daya gyara rayuwarsa ba, yana da burin wata rana yayi rayuwar yanci, kamar ko wani ɗan adam, yana son yayi sallah ya gana da ubangijinsa, Tun kafin Ya mallakin hankalinsa Rayuwarsa take a cikin gidan kurkukun ƙaddara cikin kunci da takaici, idanunsa sun jima suna gane masa bakin zaluncin da ake aikawata agidan kurkukun ƙaddara, babban takaicinsa mutuwar mahaifinsa tamira batare da ta cimma burinta ba na ganin ta kawo karshen zaluncin shuwagaban nin gidan kurkukun ƙaddara, bai ta6a tsammanin zata riga shi mutuwa ba, yaso ace yacika mata burinta sai dai kash ƙaddara ta riga fata......

Babban burinshi Su Unaisah su tsira da ransu ko dan su kai labarin gidan kurkukun ƙaddara saboda al'umma su san da zaman shi, ko an samu wadanda zasu yi shahada su kawo karahen zaluncin da ake aikatawa.....

Hawayen dake sauka kan kuncinsa a hankali suke ɗiɗɗiga saman gawar tsohuwa tamira....

Gaba ɗaya ya manta da lokacin shi da ke tafiya, sam ya shafa'a ya manta da zancen binne gawarsu da yace zaiyi saboda hankalinsa ya gushe.

Kwatsam yayi zurfi acikin tunaninsa, ba zato ba tsammani kamar daga sama Yajiyo sautin dirar wani abu mai matuƙar razanarwa, harta ginin dakin sai da ya girgiza, lokaci ɗaya ya zabura ya miƙe zuciyarshi na harbawa da karfi da karfi, tunkafin ma yaga menene ranshi ya bashi cewar Giants ne na gidan kurkukun ƙaddara, mutanan da babu ɗigon imani aransu, zuciyarsu tamkar dutse take, kurame ne kuma makafi ne basa ji basa gani umarnin Elders din su kadai suke bi.

Wani irin wahalallan Yawu salsabeel Ya hadiya mai ɗacin gaske, tuni zufa ta soma wanko mashi, gaba daya yabi ya zauce saboda bai da karfin da zai Iya ja da su, sunfi karfin shi nesa ba kusa ba.

Tsabar kidimar da yayi ce ta shi yin zarya a dakin tsohuwa a kokarinsa naya nemo hanyar da zai kubutar da gawawwakinsu gudun kada su wulakantasu ..

Kafin yayi wani yunkuri Ya soma jiyo takun tafiyarsu, A matuƙar firgice Yake kallon fadadan kafafuwansu.

Kusan su uku ne, Wasu irin gabza gabzan samudawa masu kirar Zakuna, kamar fatalwu haka suka fado dakin, from head to toe sun rufe jikinsu da bakaken kaya baka Iya ganin komai nasu.

_Yawu salsabeel Ya haɗiya, ta ko'ina zufa ce ke tsastsafo mashi ta cikin hudojin gashin fatarsa, muryarsa da tsantsar tashin hankali Ya furta"zanyi maku bayani...." bai ƙarasa maganar ba, Muryar wani basamude daga cikin su mai amon gaske Ya furta"Salsabeel ka yi kuskuren ƙetare iyakarka, ka riga da kasan hukuncin wanda Yaci amanar Elders! Sakamakon ka mutuwa ce, zakayi mummunar mutuwa salsabeel zamu kashe ka sannan mu watsa ma karnukan mu naman ka su cinye shi, bayan haka waɗannan ƙasƙantattun gawarwakin da ke a kwance zamu kwanta da su, idan muka gama biyan buƙatarmu da su, zamu cire sassan jikinsu muyi farfesu da su, Kasusuwan jikin su kuma zamu rataye su ne......_ 😳😳😳

*Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️*

*Littafin kurkukun ƙaddara 500 ne, dukanshi Book One two and 3 Idan kin shirya biya ga Details da zaki tura*

3196407426

First bank

Bature Hafsat Muhammad,

*bayan kin tura zaki bada transaction reciept ko screenshot na debit alert a matsayin shaida ta wannan layin 08169856268*

YOU MAY LIKE THESE POSTS
Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
SUBSCRIBE US[14/10, 6:05 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 20 Complete
by
Novels Elite Admin
June 20, 2024
Sponsored Link

Novels Elite English
_*~✊💋BOSSLADIESWRITERS💋*~_

سجن القد💋🔥💞

~Takun Ƙarshe🔥~

Dedicated to Aunty Kubra💋💞

قصة حب رومانسية غير عادية بين السجناء مع تطورات معقدة💋💘😘

An extraordinary romantic love story between prisoners with complex twists ❤💋💘

Daga alƙalamin Boss Bature💋✊

_AUNTY XEE Thank you for being there for me. Your support has been a lifeline.💋💞_

__________________________E20✍️
Chapter 52 · 0% Book details