← Book details Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 175

Sashe 9

Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ta Shuka ne take gani ta zaunar da Mama da Hajiyar Dala ta gaya musu komai ta kuma yi kokarin cire musu wannan Tunanin ammh batayi nasara ba Dole ta zuba musu ido ganin abun na neman ya lalace Sai Goggon Karofi ta raba Gardama ta Dauketa kawai ni da Farko ban san matsala ko matsin Rayuwa ba, sai da sanadin ciwon Hajiya ya wujijjiga Rayuwata. sannan na kara Fahimtar bamu da gata sannan maraici ya gama Lullube rayuwarmu tun a baya na Fad'a muku ita kanta Tamadina ba su da wani gata balle mu yi Tunanin samun gatan ta barayinta gatanmu kenan Dangin Babanmu su kuma k'alilan din su ke son mu da Kaunarmu. Bazan taba mantawa da wata rana na Dawo daga allon Safe ina shiga Dakin Hajiya na ganta kwance ba yadda take ni na Ruga na je na kira Goggon Karofi tazo ta gani,aka kwashi Hajiya sai asibiti ashe Faduwa tayi ta samu shanyewar barin jiki,ta koma sai dai a kwantar a tayas,ganin haka yasa Goggon Karofi suka yi shawara da Baban katsina ta maida Hajiya da ni gidanta tana kula Damu gabadayamu,Ko wata uku Hajiya batayi tana jnya ba,jikinta ya kara Rikicewa ga nauyi yayi ma Goggo yawa Mijinta ma'aikacin gwamnati ne ammh kuma akwai Dawainiya shi kuma Baban katsina Lokacin ya na matsayin Daractan Ilimi ne na Katsina gabadaya ya samu Rufin asiri sosai. Shiyasa Saboda ya rage mata nauyi yace zai daukeni alokacin cikin Fargaba ta kallesa kafin tace"Abban Ishaq kana ganin ba matsala..? Ajiyar rai ya sauke tabbas akwai matsala yasan Halin Saudatu ammh kuma ai gidansa ne kuma shi ke auranta Dole Fa'iza ta zauna karkashin kulawarsa shiyasa cikin karfin Hali yace"Kada ki damu ba wata matsala ta had'a kayanta da zarar na tashi da ita zan wuce" Nayi kuka kamar zan mutu da naji Goggo tace na shirya nabi Baban Katsina gidansa Yaya mariya ne da Goggo suka rika Lallashina ni nasan gidan bamai kaunata,Daga maman har Anty Binta da Ya Ishaq wanda in dai suka yi Hutun Makaranta yakan Biyo Baban katsina ya gaida Hajiya wlh baya kallona bazan taba mantawa da Ranar da ya fara ganina agidan Hajiyar karofi ba kallon Sama da kasa yayi min kafin ya kauda kai ya yamutsa Fuska ya kalli Hajiya yana Fadin"Hajiya wacece wannan mummunar bakar yarinyar..? Hajiya cikin yar Dariya tace"Baka gane ta ba ko..? Fa'iza ce yar wajen Marigayi Babanka Sidi" Ina kallo ya kara kallona ya yamutsa Fuska kamar yaga kashi kafin yace"Hajiya bata da kyau Sannan ban taba ganin baki irin bakinta ba kamar ta shafa shuni" Yafad'a cikin Sigar Tozarci ita ko Hajiya Dariya tayi kafin tace"Kuma kai nayi ma kamu ba" Agaba na ya Tofar da yawu kafin yace"Allah ya tsareni Hajiya ai ni Matata bata zo duniya ba tukunnah" Alokacin Hajiya bata Dauka wani abu ba ammh ni da na taso cikin wannan yanayin nasan tozarci ne nayi kuka Sosai. Ina kuka ina komai Baban katsina ya sakani a mota yana bani baki sai Katsina Hajiyar karofi kuma bata mgana Sosai jikinta yayi zafi,sai dai bin mutane da ido kawai sai hawaye bata mgana. Tana kallona zan tafi na rike hannunta ta gyadamin kai ina kuka tana Hawaye itama a mota ma kukan na Dinga sharba sai da Baban katsina ya jawoni jikinsa yana Lallahina Fadi yake yi"Kwantar da Hankalinki Fa'iza zan kula dake kwantacin yadda sidi zai kula da dake in yana raye" Lokacin ba jinsa nayi ba ammh nasan Lallashina yake yi. Sai dare muka isa katsina anguwar Kofar soro Makeken gidan da Baban katsina ya gina Tun ranar da na saka kafata acikin gidan nan ban kara farinciki ba har fita ta zuwa gidan Ishaq babu abunda ya Sauya. Nasan dai Baba na gaba ina Binsa a baya da jakar kayana ina kalle kalle har Babban Falon gidan in da mama ke zaune ita da Yaya Ishaq sai Anty Binta da tayi aure ammh acikin garin katsina Sai Jamal wanda ke bi ma Yaya ishaq sai Karamar su Badariya. Dukkansu Baban suka zuba ma Ido da farko Mama ta fara mai lale bata ganni ba sai da ya juya yana kallona kafin yace"Saudatu ga Fa'iza ta Dawo Hannuna da zama har na aurar da ita ki kaita Dakin yaran nan ta yi wanka ta Huta" Ai ranar naga tashin Hankali agabanmu Mama ta dinga Bala'i tana fadin bazan zauna mata agida ba Dangin munana maciya amana Dangin kurame me zatayi dani ban da akara mata wahala Fada dai sosai tana Fad'a Baban katsina na Fad'a har yakai ga Baba ya kusa saka ma Mama Hannu sai da su Ya Ishaq suka Shiga Tsakani ita kuma tayi shewa tace da ya sa ke ya mareta wlh bazan zauna mata agida ba. Ranar a falo na kwana rakub'e ina rawan sanyi da tsoro,Duk naji mganganun Mama Saboda da karfi take mganarta Tunda Baba ya shige Ciki itama ta shige a Fusace ban kara ganin kowa ba Badariya ce tazo wajena Anty Binta tajata suka tafi gidanta saboda Kada ta rabe ni Jamal kuma daman ba wani babba ba ne alokacin tashi yayi ya shige Dakinsa ko ajikinsa Ya Ishaq ne ya taso yazo gabana yana min kallon Tsana da kaskanci kafin yace"Dama kece Kurman nan..? Ko Bebiya ma zan ce..? Ban ji sa ba shiyasa na kura masa ido kauda kai yayi ya wuce yana fadin"Abubuwan sun yi miki yawa..ga baki ga Muni ga maraici ga Ki kurma" Daga haka shima ya Tsallake ashe wasa farin girki wani kukan Rahma ne Duk yadda Baban katsina yaso ya inganta Rayuwata ya kasa Domin Mama tafi karfinsa bashi da yarda zai yi da ita,Tunda nazo gidan ta sallami Duka yan aikinta a shekaruna sha Uku a duniya na bautu da aikin Wahala nau'i Dabam Dabam,in na tashi Tun asuba bana komawa sai wani Daran abinci kuma sai an rage nake samun naci Tun ban iya girki ba har na iya aiki kuwa ba wanda ban iya ba In Baba yayi mgana sai tace zata koreni. Nayi wahala da Mama da ya'yanta sannan nayi wahala da Anty Binta da Ya'yanta Ya Ishaq ko ta gabansa na Gifta sai ya Hantare ni da Mummuna,baka,Tun bana Fahimtarsa har na fara gane hantara ce da Tsana shi da Anty Binta sun ce basa son kallon Fuskata baki na da muni na yayi yawa. Baba yaso ya maidani makaranta Mama tace zai yi asaran kudin sa ne Tunda baji nake yi ba Sai yace zai maidani islamiya Dakyar ta amince ina zuwa ta Lasar zuwa shidda na yammah ammh sai nagama duka aikina sannan zan fita,anan na samu na Sauke alqur'ani daman kum na d'an yi nisa a karofi,sannan nayi karatun Sauran Littafan Addini da wannan zan iya cewa na Tsira a zamana a gidan Baban katsina. *Janafty**KANA NAKA..!* *Wattpad:JamilaUmar315* *Mallakar:Janafty* *Arewabook:Jamilaumarjanafty* *Book 1* _*Barka da Zagayowar Ranar Haihuwa HAFSAT MUSTAPHA HAFNAN(SAHIBATU),Madallake da ke,Allah ya karo shekaru masu albarka Happy birthday*_ *Assalamualaikum! Phydoors* *collection (home of all you need)tazo muku da kayan gyaran girki masu inganci da Gina jiki da faranta Ran Mai gida harda Ma yaranmu domin inganta girkin uwargida Kai harma da amarya tazo muku da egusi,* *crayfish ,manja ogbono dadai sauransu Zaku iya tuntubar ta wannan nomber 08062181151 ko Kuma shafinmu na yanar gizo https://instagram.com/phydoors_collection?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==Muna aikawa ko Wani gari da iKon Allah,ko gwada kayanmu da iKon Allah sai Kun dawo* Sai kuma girken girken zamani da na gargajiya da na koya a iya zamana agidan mama shima ba wai ita ta koyamin ba,Ni na koya da kaina Saboda ina da karambani Mama bata taba Damuwa dani ba tsakani na da ita sai Harara da hantara,tana ganina a matsayin wata aba mara gata da galishu wuya ce da wahala yasa tun ban iya komai ba har na koya. Na yarda ina da nakasun rashin ji ammh bani da nakasun wani abun Hallita ajikina ina da rai na da lafiyata to zan yin komai,Na iya wasu girken girken a tashar arewa24 na shirin su Akushi da Rufi wani Lokacin Tibin ita kad'ai afalo tayi ta babatu in nagama aikina sai na Lallabo nazo na zauna Duk da bana jin yadda suke koyar da girken girken ina bin yanayin yadda suke Hada komai ina ganewa. Sannan da kuma Anty Mamah babbar Diyar mijin Anty Binta ce mahaifiyarta ta rasu ne dalilin da yasa ma ya auri Anty Binta kenan. Tana aure acikin asibitin Kashi wato Othorpedic na katsina mijinta Likita ne tana da Yan biyu wato Twins,Mama na yawan Tura ni gidanta Saboda reno Yaran nata duka mazane Hassan da Husaini masu Rigima ne Anty Mahma ba kamar Anty Binta take ba,bata da mugunta sai dai akwai saka aiki,Kuma tana da kyauta sannan bata kyamatata ko tayi min fada, in naje gidanta kamar jaka har gwara ma gidan mama ina Hutawa sai dai ita bambamcin su bana girki da kaina ita da kanta take shiga kitchen tayi abunta ammh nakan shiga na taimaka mata da yanke yanke da miko miko to da haka nake zura ido ina Fahimtar wasu abubuwan nasan bani da gatan da zan yi karatu ko ina dashi ina jin tsoro zuwa makaranta saboda kada akusheni ko ayi ma Nakasuna Dariya shiyasa na kan kasa ido da raunannun kunnuwana ina duba wasu abubuwan da jin wasu abubuwan iya abunda zan iya ji na kuma d'auka. Sannan agidan Anty Binta ma na koya su Snaks saboda Diyar Anty Binta ta farko mai suna Halisa zamu iya zama tsaran juna tunda Anty binta tayi aure tana da kananun shekaru alokacin to ita ke sana'ar yin Snaks in naje gidan nakan kasa idanuwana ina lura da abubuwan da take yi a hakan na nake daukan wasu abubuwan. Da yake ita Halisa tana da bambamci da su ba kasafai take nuna kyama gareni ba sai dai bata shigemin sau tari nakan taya ta aikin Snaks din ta in an kawo mata dayake sana'arta ne tayi suna tunda tana amfani da Social media alokacin. Tun ina da shekaru goma sha Hudu a duniya jikina ya gogu da aiki babu aikin da zai gagareni komai yawansa agidan Mama tun karfe Hudu nake tashi Daga barci naje kitchen na kintsa Sannan na Dora abun kari sai naje na tada Badariya bayan na saka mata Heater
Chapter 9 · 0% Book details