← Book details Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 131 OF 175

Sashe 131

Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

bai bar Diga saman Farar takardan gabansa ba. Abba ya had'e rai ko kad'an bai yi fara'an da zai fuskanci saussauci ba sai da yaga ya jima yana rubutun sannan ya mika hannu yana Fadin"Sakin kawai na bukata in ka Rubuta bani takardan kawai" Kansa na kasa ya turama Abba Takardan ya saka hannu ya Dauka bayan sallama sai Saki d'aya da yayi ma Fa'iza,daganan sai ya dora kalamai Lausassu zuwa ga Fa'iza. Abba bai gama karantawa ba ya ninke Takardan ya maida cikin jakarsa sannan ya Dago yana kallon Ishaq Lokaci d'aya da sakin Fuska yana kare ma Office kallo kafin yace"Masha Allah Office yayi kyau sosai.." Shi dai yana zaune ya kasa mgana ji yake yi kamar an zare mai jijiyon kuzari a jikinsa,wani irin sanyi jikinsa ya yi sanyin da bai taba yi ba mamakin Abba ya kamashi yadda ya raba shi da Fa'iza sannan ya zauna yanata jansa da Hira. Ko kwakwaran mgana ya kasa sai dai ya rika bin Abba da ido da suka fad'a kamar wani Mara lakka ajikinsa. Abba kuma yaki tafiya sai ma gyara zama da yayi yana fadin"Ya yanayin aikin naka? fata dai ba wata matsala ko..? Ishaq kansa na kasa ya gyad'a masa kansa kamar wani Tsohon kadangare,Abba bai damu ba ya cigaba da fadin"Allah ya taimaka ka maida Hankali in kana da wata matsala ka kirani kai Tsaye ka fad'amin har gobe har Jibi ni Uba nake gareka kaji ko..? Nan ma kai ya gyad'a kamar kadangare. Ishaq aransa yana fad'in kaji Cuta ka rabani da matata kuma kana cemin kai Uba na ne" Abba kamar bai Fahimci yanayin da Ishaq ke ciki na son kadaici ba, ya gyara zama yana bashi Labarin Seminar da sukayi a Abuja ta kwana Hudu Ishaq takaici da bakinciki suka yunkuro masa, ammh ya kasa mgana Abba kwarjini yake masa sannan duk Rashin kunyarsa Abba yafi karfi nan a wajensa. Abba sai ya kallesa ganin sai mutsu mutsu yake yi ya kasa zama waje d'aya a saman kujera cikin kulawa yace"Fitsari ka ke ji ne..? Nan ma ya girgiza kai kawai sai Abba yace"To ina ga Basir ke damunka ka nemi mganguna naga baka iya zama waje D'aya, sai Faman muskutawa kake yi kamar mai kurga" Sai a alokacin ya Dago yana kallon Abba kamar almajirin da ya yini yana yawo bai samu abinci ba haka ya lamgwabe kai ya kasa mgana. Ga takaicin mganar Abba ga Sakin da ya yi ma Fa'iza sai daga baya yaji meyasa yayi Saurin barin Hargagin Abba ya yi Tasiri a kansa..? Yana wannan Tunanin yaji Abba ya katseshi da Fadin"Ina su Amir da Amaryata Anum..? Duk suna makaranta kenan..? Sai alokacin ya iya bude baki murya kamar wanda aka shake yace"Eh suna makaranta sai 1pm zasu tashi tunda yau Friday" Abba yace"Allah sarki da suna gida da naje na Duba su ammh bakomai akwai Next time bari na zo na wuce Daman sakon nan nazo karb'a ,sannan naga Sabon Office dinka kuma nagani Allah yasa albarka kaji ko..? Yafada Lokaci d'aya yana mikewa,Jakarsa ya Dauka ya rataya Dakyar Ishaq ya iya mikewa kamar ma Jiri yake gani bakinsa na rawa yace"Gidan Anty Fadila zaka biya Abba..? Kai Tsaye Abba yace"Daganan sai Filin Jirgi daman abunda ya kawoni Lagos kenan" Har Abba ya yi masa sallama ya fice ya kasa Daga kafa ya Bisa Saboda yadda suka yi masa sanyi da nauyin Dagawa ko da ya samu ya Turasu dakyar ya fita har taxi din data kawo Abba ta mika da shi sai ya yi Tsaye Sototo na rashin mafita yana jin Tsigar jikinsa na tashi kowani Kofofin Fatarsa iska ya samu sararin shiga yana Hurasa da jan kafa ya juya ya koma Office dinsa cikin mummunan yanayin da bai taba tsammanin zai shiga ba. Abba kuwa yana filin jirgi ya yanke shawaran kiran Mallam mijin Goggo yaji salama da ya cikama Fa'iza alkawarinta,bayan ya samu mallam a waya sun gaisa kai tsaye yace masa"Mallam ka fad'a ma Fa'iza ta fara kirga iddanta daga yau, na karbo mata Takardan Sakinta a wajen Ishaq" Sai mallam ya yi shuru kafin yace"Allah yasa haka shine mafi Alheri. zan gayamata in sha Allahu Alhaji" Da haka suka yi sallama,Daganan ko minti Talatin bai yi ba jirgi ya sake Daukansa zuwa Abuja dagachan zai samu Mota zuwa kaduna. Mallam kuwa Suna gama waya da Abba ya kira Goggo dakinsa ya fad'amata yadda suka yi da Abba. Goggo itama sai da tayi jim kafin ta Sauke Numfashi tace"Mutuwar aure bai da Dadi ko kad'an mallam" Kai tsaye yace mata"Umarnin Allah ne. ammh an ce duk sanda akayi saki sai al'arshin Allah ya girgiza" Goggo ta jinjina kai cikin wani yanayi kafin tace"Allah ya zaba mafi alheri. Allah yasa hakan shine alherinta su kuma yaran Allah ya raya mata su ya shirya su" Ya amsa da Ameen Ameen kafin ya Dora da Fadin"sai ki fad'amata da wuri Saboda ta fara Lissafin iddarta" Goggo tace"Sai tayi idda mallam..?Naga shekaru bakwai basu had'a Shimfida ba" Mallam yace"Ai da ba su taba Had'awa ba ne sai kice haka,ammh har da zuru'a tsakani fa ba tantama ya Dora mata Iddarsa" Sai Goggo ta jinjina kai kafin ta fita tana Fadi'n zata shaida min. Lokacin da Goggo ta fito Daga Dakin mallam muna Tsakar gida ni da Jummala muna had'a zobo muna yar Hira sama sama sai Goggo bata katsemu ba sai da muka gama muka jera su cikin Frezer na kira Almajirin Goggo ya tadamin min inji Tunda ba Wuta. Na koma Daki nayi wanka nayi sallar azahar ina zaune ina Salatin Annabi Goggo ta shigo itama sanye da Hijabin da alamun itama sallar ta Idar gefen katifar gadon ta zauna sai da na Shafa na Dago ina fadin"Goggo yau me zamu ci..? Kai tsaye tace"duk abunda kika Dafa" Bata bari na sake wata mganar ba tace"Yau nawa ga wata..? Na kalleta kafin nace"Sha hud'u ga watan jumada ula Goggo" Sai goggo ta dora da Fadin"Daga yau ki fara lissafin iddarki" A bazata mganar tazomin sai na Kurama Goggo ido cikin wani yanayi ganin ta mike tana shirin barin Dakin yasa nace"Goggo.." Ban karisa ba ta juyo tana Fadin"Ishaaq ya sake ki. Baban ki ya karbo miki Takardan ki" Daga haka ta fice sai naji wani irin Sanyi ya ratsani tundaga sama ta har kasan kafata sanyin da kamar ina cikin kankara na kasa Fassara irin yanayin da nake ciki. Sai naji na koma na gyara zama Dabas yanzu shikenan ba zan kara zama tare da yara na ba..? Sai kuka ya tasomin hawaye wani na korar wani,Ammh kuma zuciyata dake cikin kunci naji tana Bud'ewa wani iska mai Dadi na kadani kamar an Saukemin wani kaya mai nauyi a saman kaina. Sai na Daga hannuwana sama ina Fadin"Ya Allah ga baiwarka nan Fa'iza Mafitan alheri na rokeka kan aurena da Ishaq Tunda ka zab'amin wannan mafitan nasan itace alherina na kuma Karbeta da Hannayena Biyu, Allah ya shiryamin yarana Allah ka kare su da kariyar ka ka jikansu da jikan ka ya Allah'" Haka nayi ta maimaitawa kafin na Shafa,na Dauka zan ji na Damu sai kuma Lokaci d'aya na watsake na cigaba da Harkokina,Dambun Shinkafa nayi mana na zogale. Goggo nata mamakin walwalata ita da mallam,Anty Nasara da Yaya mariya suka zo gidan ni dai ban fad'a musu ba sai Goggo ce ta fada musu suka kalleni da mamaki ina wasa da Abul dan wajen Anty Nasara. Goggo tace"Hakika da an matsama Fa'iza ta koma auran Ishaq da an cutar da ita, kalli yadda take fara'a yau kadai da akace ba auransa a kanta" Yaya Mariya tace"Alhandulillah yau Allah ya raba Fa'iza da wannan kaddareren auran" Anty Nasara ta Dora da Fadin"Yadda bataji dadin auren ba ne auren gabadaya ya fita a kanta. Allah yasa hakan shine alheri" Nan dai suka cigaba da mganar ina zuwa wajen kuma suka yi shuru,ban nuna wani abu ammh nasan mganata suke yi. Sai dare Abba ya kirani ya kara Jaddamin shima yayi mamaki da bai ji ni cikin Damuwa ba,sai Hankalinsa ya kwanta ya kara tabbatar ma kansa da gaske nake nagaji da aure da Ishaq rabasa shine alheri,shima a bangaransa Ammi kada'i ya fad'amawa ta ko rangada guda,Abba ya kalleta cikin mamaki kafin yace"Sakin auren kike ma Gud'a Aziza..? Ammi tace"Baban Nana aure dai irin na Fa'iza a tayata Barka da arziki". Mirmishi kawai yayi bai yi mgana ba aransa yana jin farinciki ganin yadda nima Farincikina ya soma dawowa. **** LAGOS. *9:30pm* Da wuri yau Ishaq ya tashi daga Office kamar zazzabi yaji zai rufe shi bayan tafiyar Abba,ba kowa a gidan sai Jamal sai shema'u mai renon yara. Mama na katsina bata dawo ba sannan Zainab na wajen aiki. Anty Fadila ya kira yace in Direba yaje daukan yara ya kawosu gidanta sai yammah Jamal zai zo daukansu taji muryansa ba Dad'i ta tambayeshi sai yace mata bai jin dadi tayi masa sannu da haka suka yi sallama. Sa ni yayi ko sun dawo abinci da zasu ci ma aiki ne,yarinyar nan kuma bata iya komai ba sannan ma ai girkin gidan ya yi mata yawa yaushe zata iya. Shima ranar kwance ya yini salla ma agida ya dinga yi ruwa ko a cokali bai sakama cikinsa ba. Gabadaya yadda ya tafiyar da zamantakewarsa da Fa'iza ya ke hassowa ta wani Fanni bai ga Laifinta ba, ya zauna da ita cikin Kaskancin Rayuwa da zalunci da mugunta bai taba mu'amalatan Fa'iza da kyakyawan zamantakewa ba. Ammh ai ya gane kuskuransa ya nemi gafaranta yasan Tunda Fa'iza ta iya bude baki tayi mgana ko duniya zata hade bazata Dawo ba. shiyasa kawai ya Rubuta takardan sakin nan ammh ji yake yi kamar an zaremai wani lakka mai amfani a jikinsa. Zainab ya yi ta jira sai 6pm ta Dawo gidan har Jamal yaje ya Dauko su Amir, Anty Fadila tace ya barsu su kwana Tunda sun sake suna ta wasa sannan suna Haddan Qur'ani gobe asabar, sai jamal yace bari ya tafi dasu goben sai su dawo. Shema'u ke taimaka ma yaran sun dawo basu da yunwa ammh yasha takaici da ya fito falo sai yaran ke Budurin su Zainab bata dawo ba. Kuma shidda na yammahn data shigo wai ta gaji Dakinta ta shige ta
Chapter 131 · 0% Book details