Sashe 86
Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
a amsa kuwwa ne? Hararan ta nayi ina fadin"in baki saka ba tare da kunnuwan ki zan ji wayar" Dariya ta kyalkyacemin da shi Anum Ai shakiyace ta maidani kamar kakarta. kab'ar wayar nayi ita kuma sai ta fice tana dariya ashe ta jima da Dauka ni kuma ina amsa jin ba'ayi mgana ba yasa na yi sallama lokaci d'aya ina fadin"Maman Fadil kina jina.? Kawai sai naji muryansa cikin sanyi da zati yana fadin"Ba maman Fadil ba ce,Baban Fadil da Anum ne" Sai nayi kasake ina jinsa da waya a Hannuna nama kasa mgana jin nayi shuru yasa yace"Kin yi shuru Fa'iza..? Dakyar na tattaro yawun bakina sannan na iya samun mganata ta fita gaishesa nayi ya amsa yana fadin"Ya gida ya yara na..?ina fatan komai lafiya..? A gajarce nace komai lafiya,kawai sai yayi kasa da murya yana fadin"Nayi kewarku Fa'iza na kosa na dawo wlh" Kam na kame da waya a hannuna ina kifkifta ido kamar nan ne nake da Raunin ganin ba kunnuwana ba. Har yana kara lankwashe murya wajen fadin"Ko baki yi kewaata ba ne Faa'izaaa!"? Yadda yaja sunan nawa ne sai da Tsikar jikina ta tashi yar abunda na Dade ban ma san yanayin shi ba,Ganin yana neman kwace min yar natsuwata yasa na basar da tambayansa ina fadin"Ya su Zainab da yara..? Kasa kasa yace"Suna lafiya..Gata ma ta shigo ku gaisa" Na dauka fad'e kawai yake yi sai da naji mganarta tana fadin"Honey waye hala..? Kai tsaye naji yace mata"Karbi mana..Fa'iza ce' Sai ta karba da murnanta muka gaisa ta tambayi su Anum nace suna gaisheta cikin yanayin mganarta tace"Na zata tare da su Honey zai taho sallah sai na ganshi shi kad'ai Maman Amir"ina yar dariya nace"Shine bai bukaci yazo da su ba ne,ammh ki bari da Babban sallah. Nima ai ina binki bashi zuwan su Farhan ko..? Da sauri tace"Zasu zo ina so sai na yaye Fadil ne na tattaro miki su gabadaya Fadil ai d'an gidan Umma ne,ko wannan zuwan yana ganin Honey ya fara gauranci yana kiran sunanyensu Anum Umma ko Rad'am a bakinsa" Dariya nayi ina fadin"Ina ruwan Farhan" Cikin mganarta ta cigaba da fadin"Daddy ne ya hana da wannan hutun ma kin gansa,ammh zan kara tuntubansa in ya bari zaki gansu" Kai tsaye nace"Allah yasa ya bari din" Bamu jima muna mgana ba muka yi sallama ina ji tana cewa"Honey ga shi"sai nayi saurin latsan dan jan abun nan alamun kashewa bazan iya da sababbin kalaman da Yaya Ishaq ya koya a kaina ba,Bani da wajen sauke su ballatana su samu muhalli sai ga shi ya kara kira sai na kwalama Amir ya kira yana zuwa na mika masa wayar ina fadin"Baban ku ne,jeka ku taru da yan'uwanka zai yi mgana da ku" Da Murna ya karb'a suka fita falo ina jinsu suka Dauki wayar suna ta Bidirinsu gajiya yayi ya kashe wayar ko kudin ne kila suka kare, tunda ya Fahimci ni din ne bana bukata jin mganarsa sai ya shafa ma kansa lafiya. Bai dawo ba sai da ya kwashe kwana Goma tsakanin miji da mata daman sai Allah,har ga Allah bana son auran Zainab ya kare saboda haka,ance ba'a son kishiya ammh ni Fa'iza ina kaunar Zainab da zuciya d'aya ta karbeni ta mutumtani fiye da yadda wanda ya ijiyeni ya mutuntani,bawai don tana ma ya'yana Hidima ba a'a ance Halin mutum ka fad'esa bata da wulakanci bata da girman kai,tunda nake da ita bazan ce ta taba min wani abu da ya sosa min raina ba. tana kaunata tana kaunar ya'yana nima shiyasa nake kaunarta da ya'yanta bana fatan kuma auransa ya samu matsalan ina addu'an ya kauda dukkan Fitina ya Dauwamar da su har abadan saboda sun fi dacewa da juna. Zainab ta aiko ma da yara Tsaraban kayan sallar da tayi musu yan kanti harta Amir yan kanti ta siya masa ni kuma sai ta aiko min da Takalmi da Jaka da mayafi,Mama kuma Atamfa da leshi har da kud'i Badariya ma da nata Jamal ma boyel da takalmi shima uban gayya sabbin kaya ya Dawo da su fin kala Biya Mama an samu Duniya sai washe baki take tana jin dadi fadi take yi"Kaga to in da abun arziki yake zaune da digadigansa Ishaq ammh ka zauna kana wani shirme,in da ka zauna wazai biyo ka da wannan kayan arzikin..? Shuru yayi bai mata mgana ba,yasan shi da Zainab akwai kauna da Fahimtar juna matsalan ilmin addininta Ragagge ne batasan miji yafi ubanta iko da ita ba, gani take yi da ita da miji duka suna karkashin ikon Mahaifinta ne shi kuma Daman haka yake so,kada ikon ya'yansa ya tashi Daga Hannunsa har Abada yana son komai ya'yansa zasu yi cewarsa ne da ikonsa,Ko wannan zuwan ya sake zuwa ya basa hakuri sai da ya gama gayamaasa mgana har yana fadin bai kai ba,bai kuma isa ba, kaunar da yake masa ne yasa ya aura masa Zainab ammh shi ai ba sa'an auranta ba ne Daganan yasan Allah ne ya kai shi inda za'a koya masa Rayuwar duniya indai bai santa ba. Mama nata mgana ko jinta bai yi ya fada kogin Tunani sai da Jamal ya tabashi sannan ya dawo Hayyacinsa Mama tace"Ka daina wannan zurfin Tunanin fa" Anty Hure da bata koma ba har Lokacin tace"Kuma hawan jini yafi kama yara yanzu ba". Shi dai shuru yayi bai yi mgana ba Sai da Mama ta tambayesa ya mganar aikinsa sannan yayi ajiyar zuciya yace"Mganar aiki ana ta nema Mama ni ma ban zauna ba in da naji ana neman masu karatu irin nawa ina Tura Cv dina ko za'a dace.." Mama tace"Yanzu shikenan ka rasa wanchan aikin naka.?. Kai tsaye yace"Sai dai fatan samun wani Mama ammh wanchan sai babban Rabo kad'ai ne zai iya dawo min da aikina, shima bayan Hukuma ta wankeni daga wannan zargin" Mama ta jinjina kai kafin tace"bakomai muna gayama Allah ko waye ya yi maka sanadin barin ka aikin ka da ikon Allah shima bazai taba samun kwanciyar hankali ba" Aransa ko sai yace"Ba wani bane Hakkin Fa'iza ne. Allah ne yaso ni ma da Rahma ba sai na mutu ranar lahira na tashi da bari d'aya na jikina na Rinjaya na ba.Subhanallah Allah ya Tsaremu" Sai jikinsa ya dau d'imi ya tuna wa'azin da yaji lokacin dayaje Abuja na wani malami ya na fadin azabobin da Allah ya Tanadar ma mai kuntata ma matarsa da wanda ya kara aure bai kwantanta adalci a tsakanin matansa ba ,sai yaga kamar malamin yasan shi,kamar da shi yake yi wa'azin jin wannan wa'azin ya sa tsoron Allah ya kara kamasa. wannan azumin ya Dawo da kudirin niyar bama Fa'iza hakuri su Fuskanci Sabuwar rayuwa ammh ya kasa kwarjini Fa'iza take yi mai,sannan bata sakar mai fuska, kuma bata yadda su kebe inda ba Mutane kamar bata son ma taji dame yazo ya Lura da ita tana da'ri da'ri da shi. Ni ko ta bangare na bansan yana yi ba, duk da ai ya fad'amin in ya dawo zamu yi mgana ammh sai na rika kauce ma haduwa dagani sai shi ko bana wani abu,in Hafsah na makaranta da yara bana yarda nayi zaman daki ina Tsakar gida ina tsiro aikace aikace sanda Sakon Zainab ya iso da kaina na kirata nayi mata godiyan Dawainiyar tayi yawa sai ta yi dariya kafin tace min"'Haka Honey yace. Ammh sai da yayi korafin ban siya ma Uwargida nata Leshin ba" To na dai ce a bini bashi zan biya in sha Allahu"har muka gama waya ina mamakinsa wai uwargida..?lalle abunda ya baka dariya wata rana shi zai saka kuka gashi ina gani akan Ishaq kabir karofi. Duk neman Hanyar da zai samu kaina yayi bai samu ba,na kauce ma wannan haduwar tamu,kwatsam sai ya Tsiri shigewa dakina ya kwanta saman gadona Hake hake Allah na tuba ko a zamanin baya, baya shigowa Dakina iyakarsa in kira ne ko mgana daga bakin kofa ballatana yanzu da komai ya sauya. Ni ban ma san yana shiga ya kwanta ba,Saboda in yara sun tafi makaranta ni kuma ina waje ina aiki Dakina sai dai in nazo daukan wani abu nakan shigosa,ranar ma Zobo aka zo siya na Dubu d'aya naje neman ledojin da nakan tara acikin dirowa ta, har ga Allah ban gansa ba ina ta duba ledan sai ji nayi kafa daga bayana tana zungurin Bayana na tsorata na juyo a firigice sai kawai naga Namiji kwance a kan gadona ban ko ga fuskarsa ba saboda ya rufe kansa a tsakanin Filo gefe nayi gabana na fadi jikina ba inda baya rawa ammh bakina bai yi ihu ba sai naji nace"Subhanallah waye anan..? Ashe yana ji sai ya Dago kansa yana Dariya ido na zaro ina kallonsa kafin nace"kai ne..? Mikewa zaune yayi yana fadin"To da waye zai shigo miki daki ya kwanta in ba mijin ki ba..? Sai na jinjina kai mamaki ya cikani,Ban ce masa koomai ba na koma na cigaba da neman ledata,Saboda yanzu kuma sha'aninsa nasa yafi karfin Tunanina kawai ban ankaraba sai ji nayi ya chachumeni ta baya ya rumgumeni ya hadani da kirjinsa,tudun kuguna na dukam bayansa Hannayensa Cak ya dadumo kirjina kamar ya samu wani abun har da sauke ajiyar zuciya nan da nan jinin jikina ya daina aiki ya Tsaya cak! sai na rasa ina zani tun ballatana da Bakinsa ke saitin wuyana ya na fesar min da Numfashi ko a lokacin da rabon ya'ya ke giftawa tsakanina dashi bai san wadan'an abubuwan ba. shi dai bar sa ya biya bukatarsa in ya Damesa. Ba domin ya damu da ni ya nawa Bukatan ba.?shiyasa tun a wanchan Lokacin bazan iya dora komai akan bukatawata ba, na dai san ni bakuwa ce a harkan bansan komai ba. Yanzu da yake yi min wad'anan salon sai nake neman rasa hankalina, a yanzu ma Hannayensa suka fara kasa zuwa wajen cikina yaraf na saki hannayena jikina na rawa ban dawo Hayyacina ba sai da ya daga riga ta,ya dafa haannunsa saman marana Fatar Hannunsa ta had'u da nawa lokaci daya muka gwama Numfashi Hmmmm!!!!!" Bai kyaleni ba,sai ma bakinsa da ya kai saman kunnena ya lasa sai da naji ji kamar na shid'e na sake dawowa,Lokaci d'aya da ya yi amfani da wata irin karuwar