Sashe 41
Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
wake,har da kudi in ji Goggo na karba araina ina roko ma Goggo Gida a gidan Aljannah Saboda yadda ta rike zumunci bata yada shi ba. Kwana Biyu Hafsatu tamin ta koma saboda makaranta sannan tana kunshi yanzu sosai take samun masu zuwa nayi mata murna saboda sana'a itace mace a wannan zamanin da muke ciki. *Littafin KANA NAKA book2and3,paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.* *Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223* *Janafty**KANA NAKA..!* *Wattpad:JamilaUmar315* *Mallakar:Janafty* *Arewabook:Jamilaumarjanafty* MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866 Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700 MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866 IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE Haka nan na cigaba da gungura rayuwata cikin dad'i da akasasin na cire damuwar komai a raina na riga nasan Yaya Ishaq ya zabi zainab daman a kaina sannan yanzu da abubuwa su kara kamari sai na Fahimci bayan ni ma ya zabi Sabon Iyalansa da Zainab ta fara tara mai fiye da ya'yansa sai na saka araina ni kadai suke da bayan ni ba su da kowa Nasan zafin maraici nasan zafin rayuwa a gidan da ba gidan ku ba,bana fatan daya daga cikin ya'yana su fuskanci abunda na Fuskanta shiyasa duk kai da kawo na da Hakurina saboda su ne. Ko da yaushe in na yi sallah ina D'aga hannuna sama nayi ma Allah kirari da sunanayensa matsarkaka sannan na yi masa magiya da naci domin ya sama min mafita kan rayuwar da nake ciki nasan bani na Tsara ma kaina ba Allah ya tsaramin kuma yaso ya ganni a haka to bazan yi masa butulci ba, sai dai zan rokesa ya sama min mafita. cikin irin kyakyawan mafitar da yake sama ma Salihai daga cikin bayinsa. Sannan a koda yaushe addu'ata akan ya'yana shine Allah ya shiryamin su Allah ya jibanci lamarin su Allah ya sa su kaunaci junansu kada Allah ya Dora musu hassada da son kai Allah yasa su daukaka su haskaka acikin al'umma. Na cire Ishaq da abunda ya shafeshi acikin raina,Domin ina da tabbacin an kawo gabar daga ni har shi mun Fahimci wani irin zama muke gudanarwa ko da yake ni ai na Dad'e da sanin irin yanayin zamantakewa ta dashi shine a wajensa yake kallon duk abubuwan da yake yi min ahakan ma kamar yana min alfarma ne. Tunda suka koma ban kara jinsa ba,Nima ban damu ba tunda ko ina da wayar baya nema na sai na maida kaina wajen kula da ya'yana,Ba na ganin kowa sai jamal shima sai in ya shigo anguwar tamu ne,Badariya kuma Mama ke hanata zuwa tunda basu koma makaranta ba sai na Dad'e ban ganta ba. Ko cefanen mu ya kare sai dai nayi ta Dubaru na, saboda yara in ni nayi hakurin yunwa su baza su iya ba,akwai Ranar da sai mu yini bamu ci ba Daga karshe Garin kunun Ahmad nake dama musu su sha su kwanta,saboda bani da inda zan fita in nema koma naje tona ma kaina asiri zan yi sannan daga karshe ace karya nake yi,ana ganina a katon gida sannan an san mijina babban ma'aikaci ne ba kowa ba ne zai san yanayin da yawan mata suke Fuskanta acikin katon gida ba,da yawan mu ai kurace lullube da fatar akuya. Ko sa'adatu da muke zumunci da ita sosai ban taba bud'e baki na fad'a mata matsalata ba sai dai yau da gobe bata bar komai ta fara Fahimtar gidan ne kawai da mijin ammh babu wani Sauran jin dadin da nake ciki da ni da ya'ya na har ta kai yara su ka daina zuwa da Abinci makaranta Saboda komai ya kare sai dai ruwa,Tsakin da Goggo ta aiko min dashi da garin Danwake duk ya kare a kitchen di'na ko kwaran Shinkafa bani da shi ban kuma san inda zan je na mema ba. Mun yi sati cikin wannan yanayin Duka Dubaruna sun kare nima na kasa,Ranar wata laraba ko makaranta basu je ba,Basu ci abinci jiya da Daddare ba haka da Safe Anum da Musty suna kwance suna fama da ciwon ciki kuma nasan na yunwa ne Ahmad kuwa ya lafe ajikina sauran garin kunu ne na dama mai kadan ya sha shima ba domin ya ishesa ba,Amir kuma saboda ya na babba yasa bai nuna gazawarsa ba,Ammh shi kan shi yana jin yunwa ni kaina Dauriyan kawai nake yi ammh na fara Sarewa. Muna zube afalo kamar kayan wanki kukan zucci nake yi na kasa na Sarari na Daga hannuwana sama nace"Ya Allah ga baiwar ka nan Fa'iza ka fini sanin Halin da nake ciki..Allah kayi gaggawan kawo min mafita d'aya daga cikin mafitar ka ya Allah" Ban gama sauke Hannuwa na ba naji Sallama ina d'ago kaina naga Sa'adatu ashe Haruna ne yace ta shigo ta duba yau su Amir basu je makaranta ba Allah Sarki bawan Allah wajen wata biyar Yaya Ishaq bai biyasa kudinsa ba ammh bai taba gazawa daga kai su makaranta ba har mgana nayi mai ko zai bari ne yace min bakomai yiwa kai ne. Ko ban fad'a mata ba ganin mu cikin wannan yanayin ya bata tsoro ta kalleni cikin Tausayawa tana fadin"Maman Amir Allah yasa dai lafiya na gan ku duk a kwance sannan Mallam yace yau su Amir basu je makaranta ba shiyasa yace na shigo na duba ko kuna lafiya? Ina kokarin mikewa Ahmad ya lafeni na jingina da kujera ina fadin"Lafiya lau Sa'adatu yau din dai basu samu zuwa ba ne" Shuru tayi kafin ta kalli su Anum lokaci d'aya tana fadin"Anum ko ba lafiya ne yau ban ji Surutun ki ba..? Kawai sai yarinyar nan ta saka kuka cikin kukan take fadin"Yunwa muke ji tun jiya bamu ci abinci ba" Musty ma sai ya fara kuka wai shima Yunwa Ahmad na jin su shima ya saka Rigima na saki baki kawai ina kallonsu na kasa mgana ta Dago tana kallo na kafin tace"Haba Maman Amir sai ki bar yara da yunwa in suka samu wata matsalar Dalilin haka fa..? Sai na kasa mgana Hawaye suka cika kwarmin idona cikin wani yanayi nace"To ya zan yi Sa'adatu..? Bani da wata mafita sai wacce ubangiji ya kawo min kawai" Cikin mamaki tace"In shi babansu baya gari ba ga gidan iyayansa ba,bai kamata suna garin nan kuna zama cikin wannan halin ba ai yunwa bala'i ce musamman ma ga yaran nan" Mirmishin takaici nayi mata ban kara mgana ba da Sauri ta mike ta fita ba jimawa sai ga shi ta Dawo da kuni da yawa abotiki da Soyayyan Dankalin Hausa ta Diremin tana fadin"In ke kin Daure ai su baza su iya daurewa ba saboda yara ne..Zaman taren kenan da ko Amir kika aikomin da nasan abunda zan yi" Ni dai ban ce komai ba sai godiya nake yi mata nan da nan na tashi na shiga Kitchen na Dauko Kofuna na zo na Zuzzuba musu na saka ma kowa Dankalin,ita tafiya tayi ta barmu bayan ta kawo mana,Sai gashi mun ta da shi duka Lalle gaskiyan almajiri da yace yunwa bata da Hankali na yarda sai da muka koshi na samu karfin jiki,Amir shi ya taimaka min ya gyara Dakin su ya kwashe kayan da suka zubar a kasa ni kuma na gyara Sauran d'akunan nayi ma Anum da Musty da Ahmad wanka Amir ma na cudamai baya sai bayan sun shirya naje nayi wanke wanke tun jiya ban samu yi ba nima kaina ba ni da karfin jiki. Zuwa chan sai ga Sa'adatu da Shinkafa yar Hausa takai tiya Hud'u da Garin tuwo da Tsaki,Da kayan miya har da su maggi da mangyada,Na rasa da bakin da zan yi mata godiya na share kwallar data zubomin Lokaci daya ina fadin" Nagode..Nagode yadda kika ji kaina da ni da ya'yana ke ma Allah ya jikan ki" Ta amsa min da Ameen Ameen ta jima muna hira sama sama da ita kafin ta tafi wannan kayan abinci su suka taimakemu suka fitar damu daga cikim Halin da muka so fadawa na rashin abinci Maman da ya bar ma sallahun komai namu bata Damu ba ko zamu mutu mun dad'e bamu mutu ba. Abun da ke bani mamaki in ni bata kaunata ya'yan da har da D'anta aka bada gudummuwar fitowarsu duniya bazata tuna da su ba..?ammh bata Damu ina da yakinin ko rasa su sukayi sai nafi kowa asara ita d'anta yana da matar so sannan da yaron so bazata damu domin yunwa ta illatamu ba. Ni kuma tundaga Lokacin nayi alkwarin ko zamu mutu bazan kara tambayanta wani abu daya Danganceni ni da ya'yana ba in suka Sauke Nauyin dake kansu ruwan su in basu sauke ba bazan matsa musu ba, duk wanda yayi nagari don kansa sannan Hakki ne ranar gobe kiyama sai Allah ya tambayesu domin ai ya'ya abun kiyo ne ga wanda aka bamawa,kuma za'a tambayi kowa yadda ya kiwata nashi. Haka na dinga ririta kayan abincin nan Saboda in suka kare mu ne a ruwa