← Book details Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 151 OF 175

Sashe 151

Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yana fad'ama Mama ta washe baki tana fadin"Masha Allah. Allah ya sa albarka" Zainab ma tun tana wajen aiki ya kirata ya fad'amata itama tana ta Murna yaran na Gidan Anty Fadila yaje ya Daukosu a daran Sukaje shan I.cream da kayan kwalama saboda Murnan dawowar Fa'iza hatta Amir ranar an ga walwalansa ya shige cikin kannensa yana ta wasa da su. Akwai wani Farinciki da annushuwa a fuskokin yaran. Ishaq har kati na waya ya saka an buga masa gayya yake so ya yi sosai,ita kanta Zainab tace zasu yi walima in Fa'iza ta iso Lagos. Abba shi da kanshi ya kira Mallam mijin goggo ya fad'amasa ranar maida auran, shi kuma ya fad'ama Goggo ina kwance tunda na dawo ina fama da kaina da zuciyata wayata ko ban kunnata ba har a lokacin tana kashe ne ga,shi tunda aka san na dawo ana ta kawo ayyuka ai bani ma da wani guzari su jummala ke yi kunin aya da zobo daman Goggo ke yi yanzu. A bakin Yaya Mariya nake jin ranar asabar za'a maida aurena da Ishaq ranar sai a asibiti na kwana,Haki na farayi sama sama numfashi na sama sai kuka,kuma na kasa fitowa nayi mgana Abba kuma yayi bakam domin shima ya yi katin daurin aure, ya gayyaci abokan aikinsa. Labari ya kai ma Ishaq bani da lafiya shima Yaya isa ya fad'amai kwana na Biyu a asibiti aka sallamoni da gargadin na rika cin abinci sannan na daina yawan Tunani to ai tunani a wajena ya zama Dole. Sai dai sun ta kirana wayata a kashe shi da Zainab,Badariya ma tana son mgana dani ammh na Toshe duk wata hanya,sun yi sun yi su ji Tsarina na Biki naki mgana sai shirin walimarmu kawai nake yi dubu ashirin ashirin muka bada sai Hijaban da muka dinka iri Daya. sai ni a gida zamu yi abincin Sadaka,Sai kuma na baki Tunda Abba da Ammi da Inno suna tafe ga su Hafsah suna nan basu koma ba. Nana Fatima ma mun yi mgana ta wayar Goggo tace ranar jumma'a zata zo da safe tun da walimar sai la'asar ne, bana yarda ayi min mganan Daurin aure yanzu sai na saka kuka duk wannan Dauriyar da nake yi Engr na makale a raina bai fita ba kowani Bugawar Numfashina tare da shi acikinta ammh Farincikina ya'yana ne ya yi min katanga da shi har Abada. Tun ranar alhamis Abba da Ammi da Inno sai Raliya da walid suka Dira a Korafi daman na fad'ama Hajiya zencen walimar ammh ban gayamata na Daurin auren ba sai Raliya ne ta gayamata sannan na kira sa'adatu da Habiba na gayamusu sun kuma min alkwarin suma zasu zo min in sha Allahu. Su Ammi a gidan da Abba ya gina suka sauka,tunda Daman Baba Ati na cikin gida ita da ya'yan makota ta kama ta rike,ranar jumm'a da Safe sai ga Badariya abun bai wani bani mamaki ba nasan abunda ya kawota ko murnan ganinta ban yi ba, itama ta ga hakan don da tace min tayi ta kiran wayata a kashe yake kawai nayi mata sai kuma ta kalleni tana fadin"Amaryan tamu ba kunshi ba gyaran kai ba na jiki..?me kike nufi..? Ko amsa ta ma ban yi ba a raina sai da na Zageta in da ace yau Engr zan aura da sai nayi masa abun yafi haka ma sanin shi zai aureni ne ba domin ya yi min alfarma ba sai domin yana sona. Baki duk sun hallara har da Yaya Asiya su Anty Binta dai ance suna katsina wai Mama sun zo ita da Ishaq da Yaran nima a bakin Yaya Asiya nake ji tunda tace tare suke da Halisa ta sauka katsina Hajiyar Dala ko cewa tayi nasan zan koma uban meyasa na matsa sai da aka kashe auran..? Bata zo ba kuma wani nata bai zo ba ,ni dai gidan su Yaya isa na koma da shirin walimata na tsani naji ana ambaton sunana da na Ishaq,sai dai na ji sanyi da akace da yaran yazo garin ko banza zan ga ya'yana naji dadi. Ko kafin karfe hudu an gama komai na walimar ni a gida ma na barsu mun isa makarantan tun biyu na rana,an shirya taro tunda dukkanmu iyayanmu zasu zo,su zasu shaida karban Shahadar. Sai bayan la'asar aka fara a babban masallacin makarantar za'ayi abun,dukkanmu mun sanya Hijabai Sea greeen har kasa da Safa da bakaken likabai ni kadai ce bazawara mai ya'yan sauran matan duk yan mata ne sai maza uku. Ahalina kaf sun zo,abun mamaki har da Anty Binta, Mama,Anty mahma,Halisa,Da Ishaq,sai Amir da nagani banga Sauran ba tunda mu muna chan gaba ne,Nima din waige nake yi,Nana Fatima tazo duka ita da ya'yanta sai Sa'adatu da Habiba Allah sarki tare da su Anty Nasara suka iso masallacin,Hajiyar Raliya ma tazo ita da yayar Raliya Salima,Yaya mariya da ya'yanta su Hafsah har da su jummala laure da makotan Goggo. Naji dadi matuka har sai da nayi hawaye Amir ina cikin nikab ammh sai da ya gane ni yazo wajena na Rumgumesa ina tambayansa sauran yan'uwansa yace"Suna gida Umma Tare da Anty" Cikin mamaki nace"Katsina suka zo" Kai tsaye yace"Lagos dai ai Daada yace tare zamu koma dake ko Umma..? Sai na kasa mgana illah kai da na Dagamai,an fara gabatar da walimar jawaban manyan baki da kuma mai makaranta sai na malamai sai kuma jawaban iyayen yara har Mallam mijin Goggi yayi jawabi Abba ya yi amatsayin Babban bako. Sannan Ya muhallin d'in mu an basa dama yayi jawabi na samu lambar yabo na Hazikar mace ta farko da shekaruna na Hankali na Haddace Qur'ani ya yi kira da sauran mata su koyi dani kada su duba shekaru su tashi su nemi ilimi,Sannan ya yi mganar Lalurata ammh yace hakan nan na Dage har na riga masu lafiyan Haddace Qur'ani,mu sani Allah baya maka hallita batare da yana da manufar hakan ba ina kallon su Abba suna ta mirmishi Allah Sarki tamadina da Baba nayi musu addu'an Aljannah da na tuna da su. An fara kiranmu d'aya bayan Daya Domin karban rantsuwa naga Fitan Abba ina ta Allah Allah ya Dawo kafin a kirani sai dai addu'ata bata amsu ba nice ta Biyu,tunda in zaka karbi shahadar sai da Hannayen iyayenka da yan'uwanka gabadaya. Sanda sunana ya karade lasifikan hankalina na baya ina leken Abba domin bazan amsa ba sai hannunsa na kan Hannuna. Kira sunana ake yi"Fa'iza Sidi karofi" Ammh ban ta shi ba sai da Yaya Mariya da su Nana Fatima suka zo suka tadani ina kamkame da Hannun Amir,Sai waige nake yi Yaya mariya tace"Wai wa kike nema ne..? Kai tsaye nace"Ina Abba..? Sai alokacin suma suka san baya masallaci Nana Fatima ta matsa gefe tace bari ta kirasa kuma ta kira bai Dauka ba ganin ana ta kirana yasa na tafi,ina zuwa akace ina Dangin Fa'iza Gabadaya sai su Goggo suka taso abun mamaki har da Ishaq su mama daman tare da su Goggo suka taso zuwa inda nake tsaye. Ni dai hankalina na wajen kofar shigowa,ina jin ana jawabai wlh ban Fahimci komai ba, gabana ke fad'uwa fat Fat! Mallam ya juya bai ga Abba ba cikin wani yanayi yace"Ina Alhaji ko fitan sa din nan bai dawo ba..? Ina shirin nayi mgana sai ga Abba ya shigo masallacin ina ganinsa sai naji sanyi araina ban tsaya ma kallon bayansa ba na juya ina kallon Ishaq dake ta bayana,taka hijabi na yake kamar zan fad'i sai na juyo sai ya kauda kai yana Dariya yayi fari ammh bai yi kiba ba,sai kasumba daya tara kamar wani kumurci. Ni ko harara na ballamai ta cikin nikab dina na sauya waje zuwa kusa da Goggo Amir kuma ya Biyo ni. Sai ji nayi Yaya Mariya na fadin"Abba ashe bako ya yi" Dago kaina kenan naji Nana Fatima na fadin"Ammi kamar Engr..? Dum! Gabana ya amsa ina Dago kaina sai a na Engr yana sanye da Fararen kaya shadda ce tana maiko da yarari,Daga sama har kasa shigansa ta manyan mutane fuskarsa ma'abociyar Haiba da mirmishi tana nan har alokacin Abba na gaba yana bayansa da Takunsa na Cikakkun maza yan kwalisa. Ni dai naji Abba na gabatar da shi abun mamaki Ishaq har yana bashi Hannu harda rankwafan girmamawa Abba dai bai ce komai ba kansa ya kulle shi kuma Ishaq yasan sunan Engr a bakin Abba ammh bai taba ganinsa ba. yana jin Abba yace ga Megidansa Engr dole yakai gaisuwa tunda da taimakon Engr Aka wankesa daga Zargi. Abba kuwa mamakin Engr ne ya kamasa duk da yasan Halin nagartansa bai taba fad'amasa yasan Fa'iza zatayi walima ba,sai kiransa kawai suna masallacin nan yace gashi sun shigo Karofi ya bashi address din wajen walimar. Sai da ya fita suka had'u ya gasgasta wannan kauna da Engr ke yi ma Fa'iza,kai tsaye ma yace masa"Nan da kwana hudu tafiyata America ban manta gobe ne Daurin Fa'iza ba. sannan na rike date din walimar su ina daga cikin masoyan Fa'iza dole zan bar duk abunda ke gabana Saboda nazo na tayata murna" Daganan yasan Fa'iza ta rasa masoyi,masoyin kwarai da nagarta irin Engr Abdulbasit. Ni ko jikina sai naji ya saki ammh kuma Farinciki ya lullubeni ina kallonsa yana wurga idon nema na,karaf ko ya ganni ta idona inaga ya gane sai naga ya yi min wani kayattacen mirmishin da ya shiga har cikin tsokar jikina sai na kara Damke hannun Amir ina makyarkyata. Kafin a ba ni Shahadar sai da nayi karatu cikin suratul Yusuf farko da Tsakiya da karshe aka yi min kabbara,sannan akace yan'uwana su matso su tayani karban shahadan. Duka muka had'a hannayen mu,Engr na gefe bai saka hannunsa ba sai da Abba yaja hannunsa ya hada da nashi suka mika a tare nima na rike na Amir na mika nawa sauran ma suka miko nasu hannayen muka karba Tare sai kabbara ni ko sai ruwan hawaye. Ya muhallin d'in mu ya karbi abun mgana yace"yau na karbi shahadan haddan Qur'ani mai girma gobe kuma a wannan masallaci zan karbi nauyin igiya uku na aure, yana tayani murna Allah ya sanya alheri" Sai aka kara Daukan kabbara,Mallam ya bada sanarwan Ammi jikinta duk yayi sanyi ganin Engr,Mallam shi ya nuna Ishaq yana fadin"Ga
Chapter 151 · 0% Book details