Sashe 134
Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
sai nima naga duk ta rame kamar ba Badariya ba. Kayan na fara nuna mata tagani ta saka albarka kafin tace"Anty Fa'iza kina da kyakyawan zuciya matar da sanadinta kika rasa mijin ki kika yi ma wannan Hidimar haka..? Kai Tsaye nace"Ko daya. Zainab ba ita tayi sanadiyar mutuwar aurena ba,Ita me ta sani.?abunda ta gani ko taji gayamata akayi badar..Ni nayi mata don Allah ne domin Sanadin kaunar datagwadamin ni da ya'yana abaya nima fa tana min alherin nan Bazan manta da ita ba" Badariya ta yi jim kafin tace"Eh gaskiya tana da kirki sai dai ba matar Aure ba ce. Bata fa ta aikin komai sai fita aiki Jamal yace wannan yar renon ke Jagwalgwala abinci ko Kuma ya ishaq ya siya,bata aikin fari ballatana na baki yaran ma Anum ce da Amir masu kula da su da kuma yayarki dake chan" Kai tsaye nace"Daman ai bata aiki ko suna Abuja ma'aikata garesu" Badariya ta tabe baki kafin tace"Ai yanzu daga shi har Maman sa gane amfaninki Anty Fa'iza Mama yanzu ita ke girki ban da Lalacewa ina mama ina wani girki" Ido na zaro kafin nace"Subhanallah garin yaya..?to su dauki yar aiki mana" Badariya ta gyara zama tana Fadin"Basu samu ba daga nan ba'a samu wacce zataje chan ta zauna ba,Sai Dole yar chan kuma wa suka sani..?Anty Zainab kuma bata saba ba tace bata ma zata iya ba,Mama kuma tana Tausayin Yaya ishaq da yara nan Dole yanzu ita ke yi shiyasa na kosa na koma naje na amsheta tunda abunda suka shuka ne suke girbansa Daidai gwargwado" Ta fada idanuwanta sun tara Hawaye kai tsaye na nuna jimami na har acikin zuciyata kafin nace"Gaskiya kan gwara ki koma,kuma ammh Anum ta iya Dafa Saukakkun abinci ita da Amir. Badariya tace"Yaya Ishaq yace bazasu rika girki ba, sun yi kankanta ita kuma Gimbiyar tace bazatayi ba" Kai na jinjina ban sake mgana ba,araina nace Rariyan da ya siya kenan ita ke zubar ruwan. Badariya sai ta nemi min kuka na kalleta cikin wani yanayi kafin nayi mgana ta rigani da fadin"Anty Fa'iza wlh hakkin ki ne yake bibiyata" Sai na tsorata da Sauri na zaro ido kafin nace"Hakki kuma..?ni me kika min..? Har ga Allah na tsorata na tuna muna waya da ita sosai har Raliya suna kirana ita da Laila su gaisheni bayan an kwana Biyu zuciya ta zargesu ko sun ce nace wani abu ne akan Badariya Ammh sai naji ta rike Hannayena tana Fadin'"Abubuwan da su mama suka rika yi miki ne ita da Anty Binta da Yaya ishaq wlh hakkin ki ne ke Bibiyana Anty Fa'iza, ba mashinshini Wlh bani da Saurayi rabon da ma wani yace yana sona na manta wannan ba hakki ba ne Anty Fa'iza..? Ta fad'a sai kuka sai Tausayinta ya kamani har ga Allah ina sakata cikin addu'ata Na rumgumota ina Lallashinta har abada bazan manta da karamcin Badariya a gareni ba ta kaunace ni lokacin rayuwa ta juyamin baya har kuma gobe tana kaunata ita Fa'iza ta kaunata tun Fa'iza na Fa'izarta,Sai da naga ta daina kuka sannan na Dagota na share mata hawaye Lokaci d'aya ina Fadin"Ki daina Fadin haka Badar. Ni fa ban ta rike su a raina ba har shi Yaya ishaq din na yafe masa Darajan ya'yan mu aure lokaci ne in Lokacin ki yayi zaki yi. Mu masoyan ki muna yi miki addu'a in sha Allahu Nagarin na nan tafe" Kai ta girgizamin cikin Raunin murya kafin tace"Ban ki mganarki ba Anty Fa'iza ammh ki sani sharri dan aike ne inda ka aikasa zai dawo maka komai Daran Dadewa. Mama ta aikata miki ba Daidai ba. yafewarki bazai hana Allah ya nuna mata Ishara a kaina ba shi Yaya Ishaq ya fara gani Anty Binta ma tunda itama Halisan yar Mijinta ta hanata zama Lafiya kwanaki har gida taje ita da ya'yanta, suka mata duka har ciki dan Sati uku ya fita ajikinta sai da tayi yaji tayi kwanaki a gida kafin manya suka ciki aka Sulhunta" Ido na zaro cikin Firgici domin ni ban ji Labari ba,Ganin haka yasa Badariya ta cigaba da fadin"Wlh kwanakin baya akayi,Anty Binta na bala'in zata kai kara kotu Anty Mahma ta bata amsa da cewa ba zencen kai kotu duk abunda kayi shi zaka girba walau khairan walau sharri kamar yadda ta hana Fa'iza zaman lafiya itama kwatankwacin haka za'a hana yarta ai sai tayi shuru tasan gaskiya" Tagumi nayi har araina ban ji dadi ba nace"Allah ya kyauta" Badariya tace"Amin ga miji dan iska manenim mata chan naji Suwaiban Hajiyar Dala na gulmar, suna ta zagin Halisa araina nace Allah ya kara" Ajiyar rai na sauke nace"Allah ya kawo mata mafita" Ta amsa da amin kafin tace"Har da ita amasu yawo dani ban yi aure ba ido cikin ido na fada'mata da aure irin nata gwara babban mace agida muka yi kaca kaca da ita naso Anty Binta tamin mganar. har ita ban so na kyale ba sai kuma batamin ba" Nasan Badariya da Fad'a sai na Shiga bata hakuri ina fadin"Sai hakuri badar..Ki rika banza da irin su. aure Lokaci ne kuma in sha Allahu Lokacin ya kusa" Tana mirmishin yake tace"Allah yasa"hira muka cigaba da yi a bakinta ma nake jin wasu labaran,mun gangara Hirar Raliya tace min tana da ciki taje ma kwanaki ta mata kwana Biyu tana fadin alherin Raliya gareta da basu had'a komai ba ina bata Hakuri,nasan irin zafin datake ji acikin ranta,muna tare da ita har Bayan La'asar sannan tayi shirin Tafiya,tace min gobe da asuba zasu dau hanya har ta siya ticket din motar,su Anty binta suna chan basu dawo ba,Na nuna mata kayan duka da na kowa da kowa tace ta gani ina da wata atamfa da Anty Nasara ta bani ban ko Dinkata ba,sai na hada mata da kayan kwalliya da Hajiya ta kawomin wanda na ijiye ma su Hafsat basu zo ba na bada kudi 5k nace tayi Hakuri zan yi mata sako tana ta Godiya. Da zata tafi Goggo ta hadamata su zogale kubewa,kuka tace ta kai ma Mama,har zaure na rakata kamar kar mu rabu bayan tafiyanta abun ya Dameni har na fadama Goggo Abunda Badariya tace itama tayi shuru kafin tace"Allah ya kyauta ammh ai fadar Allah ne ya hana kansa zalunci kuma muna bayinsa ya hanemu da shi" Daga haka bata kara mgana ba,a raina n a kuduri zan kara Dagewa da addu'an Allah ya kawo ma Badariya miji na gari na nuna sa'a. Bata kirani ba sai da aka kwana tunda kwana suka yi tafiya ta hadani da yaran suna ta murna,sannan itama Zainab din ta kirani tamin godiya daga karshe tace"Naga sako Little tace bata Hakura ba,sai Takwaranta tazo ta ganta" Dariya kawai nayi ban yi mgana Domin na saba jin korafin Zainab kan rashin zuwana. Wannan kayan da Ishaq ya gani suka zaburar da shi yana son zuwa kuma yana Tsoro,ammh yana ta kamun kafa wajen Abba ko da yaushe yana kiransa shi ko Abba in ya kirasa sai ya bige da masa Hiran aiki da Duniya in kuma Ishaq yaso sako wata mgana sai Abba ya shanshantar da mganar,shi kuma nauyi da kunya yasa ya kasa neman ma kansa mafita ammh yasan Yana Bukatar fa'iza. Mama kuma ya yi mata magiyan ta shiga Lamarin kai tsaye tace"Ishaq ba ruwana bazan kara saka baki a zalunci Fa'iza dani ba. kaje ka sameta kafin ta gama Iddanta ka kara bata Hakiri in ta Hakura zata dawo don kantaina murna in kuma bazata Dawo ba Ishaq bazan saka baki ba sai kayi Hakuri ka rumgumi zainab din tunda ita ka zaba" Tunda ta fadi haka yasan bazata kara mgana ba,Anty Binta ma haka tace yaje ya samu Fa'iza tunda baban nata baya tare da ita ya Lallasheta Anty Mahma dai bata ce komai ba amnh a ranta tana Fatam Fa'iza kada ta amince. Ga su ga Zainab din nan ko su basu ci albarkacin ta zauna da su ba,Mama ce take yi da suka zo ne suka karbeta,Ammh tana jin sauki ta koma aiki wai basu bata hutu ba,sannan tareda Shema'u take tafiya saboda Renon Little,Allah yasa yaran na gida an yi Hutu da Mama ta shiga uku. Jamal kuma an kira su yana Gombe ya tafi Camp abunsa. Da shawarwarin su ya yanke shawaran tahowa karofi ya sameni bayan ya gama shirya yadda zai yi amfani da kalaman bakinsa ya shawo kaina. ***** Bani da masaniyar zuwansa ko abunda ya shirya a ransa,Ranar asabar da nake da kwana hamsin da shidda cikin idda ne ranar na tashi da jini na Biyu,Da aranar Abba da Ammi za su Karofi sai suka fasa An kira su Abba taro a Parthercourt sai ya tafi ajiyan. har Goggo ta saka su Yaya mariya sun je sun gyara gidan an saka Turare sai kuma zuwan nasu bai yuyu ba. Da Safe bayan na tashi nayi wanka nayi mana abun karyawa jummala bata zo ba sai karfe goma,sai na gyara Falon Goggo na zauna ina karyawa ita taje kaima Mallam nashi ta dawo ta zauna kusa dani tana shan koko da kosai shi nayi mana lokaci d'aya kuma muna taba Hira sama sama acikin Hiran ne nace"Goggo bayan na gama Iddata na ina so na dawo da girke girke na tunda kuna da Fili a nan" Goggo tace"Sosai ko Tunkuya goma ce za'a dorata a gidan nan kuwa. Sai ki Dauki ma'aikata su rika tayaki ayyukan" Ina tusa kosai bakina nace"Haka nake Tunani da na bari sai Abba yazo ne sai nayi masa mganar" Goggo tace"Eh ki yi mganar da shi hakan yana da kyau sana'a nada Dadi zaman haka bazai dameki ba" Mun dan saurara da Hirar sai chan nace"Goggo yaushe za'a je katsina a kwasomin kayana..?ina so a kwasomin wasu ina so nayi amfani da su. wasu kuma sai na kyautar da su kada su lalace" Goggo tayi shuru kafin tace"Kin ga mun Sha'afa da wannan mganar to yanzu ya za'ayi?Dole sai an kira Ishaq din tunda kila key din gidan na Hannunsa" Kai tsaye nace"Nima ina da shi Goggo" Domin kamar na sani na cire na kofar gida guda daya da na Dakina. Goggo tace"To shikenan zan saka mallam ya kira Baban naku a gayamasa abunda yace shikenan" Da