Sashe 27
Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
yaki Rufuwa da Goggo tace min kwana zatayi sai gobe zata koma ni kawai tazo dubawa. Su Amir nata tsalle da suka Dawo suka ganta,suna son zuwa karofi ammh Ya Ishaq baya bari daga makaranta sai gida sai ko gidan Mama in ma sun je to yini ba kwana ba. Bamu samu kebewa ba sai Dare bayan yaran sun kwanta Goggo ta na gayamin taji duk abubuwan da suka faru basu yi mata Dadi ba Sai dai tayi ma Yaya mariya fada meyasa ta biye ma Binta ai ko banza ni yar'uwanta ce bai kamata ta taho ta kyaleni ba,Goggo tace kinsan mariya da bakar Zuciya,Sannan ta riga ta rantse ne yasa bata ce ta Dawo ba,ni nake fadama Goggo zuwan ya Ishaq da amaryansa na gayamata mun zauna Lafiya da ita har suka koma Goggo ta cigaba da min nasiha duk akan nayi hakuri ne watarana sai Labari. Sai Wajen d'aya saura na Dare muka kwanta da Safe kuma da Goggo Tayi shirin tafiya nace ta leka gidan Mama su gaisa tace min bazataje ba Dakyar na Lallasheta tace zata biya tayi mata Murna dagachan zata wuce a bakinta nake jin Hajiyar Dala ta kirata a waya tana mata fadan bata kyauta ba da bata zo ba Goggo tace nayi mata Tas daga Lokacin bata kara kiranta ba. Sha d'aya na Safe na raka Goggo Har bakin Hanya mun rabu tana ta kara jadaddamin nayi hakuri da rayuwa watarana komai zai wuce sannan na Dage da gayama Allah shine Sarkin Duka Duniya gabadaya. Mun rabu kamar na bita haka nakeji ammh ba Dama,har da kwallata sai da nayi,Bansan ya Goggo suka kare da Mama ba sai da washegari Badariya tazo take bani Labari Mama har da kuka ta kira Anty Binta da Ya Ishaq akan Goggo Tazo tayi mata cin mutumci Saboda ni.. Gabana ya fadi na zare ido ina kallon Badariya kafin nace"Sabo da ni kuma..? Badariya tace"Tabbas..Kinsan Halin Mama har Hajiyar Dala sai da ta kira ta fada mata..Ni dai nasan kila Goggo Fada tayi mata shikenan sai cibi ya zama kari Anty Binta nata fada haka ma shi kan shi Ya Ishaq din a waya sai Fada yake barin ma jin Mama nata kuka" Sai jikina ya fara rawa nasan komai kaina zai dawo aiko hakan ce ta faru Badariya ta tafi ba Dadewa daman Daga makaranta ta biyo sai ga Anty Binta da Mama har cikin gida wanda bazan iya tuna zuwan mama gidan nan na karshe ba. Zagi da gori da cin mutumci ba wanda basu yin ba ina da goyon Ahmad a baya na Mama ta saka Hannu ta tsinkeni da mari,na Dafe kuncina Hawaye suka Gocemin,Ahmad na barci ne ammh sai da ya tashi Hayaniyar Mama yasa ya tsorata ya fashe da kuka shi yana na Sarari ni ina na zucci. Mama ta kama kunnuwana ta murde tana fadin"Ni zaki hada ma gulma da munafunci har Goggon karofi ta taka har gidana taci min mutumci don Ubanki..?ai nayi miki komai Tunda na rike ki kuma sannan daga karshe Mijina ya aura miki D'ana kika shiga Cikin zuru'ata duk da bana so..Shegiya mai bakar aniya,Wlh fa'iza na tsaneki na tsani na bude ido na ganki a matsayin surukata" Anty Binta ta karbe da Fadin"kuma ban da Ishaq din uban waye zai aureta ya zauna da ita ahaka..? Mama tace'Ki barta zan yi mganinta Tunda bata san mutumci ba" Haka suka gama zage zagen su,suna yi suna Dungurina suna murdemun kunni sannan suka saka kafa sukayi tafiyar su haka na zauna na Rumgume D'ana ina kuka shima yana kuka har sai yaushe ne zan daina Fuskartar wannan Tozarcin..? Ba mai Lallashina na gama kukana na Share hawayena,Ashe ban tsira ba Sati biyu da Tafiyar su Ishaq,sai gashi ya Diro ranar asabar da yammah,Abunda yayi min yasa na Fahimci daman saboda yaci min Mutumci ya Dawo. Har Bangaransa ya kirani na Duka gabansa shima ya ci min mutumci,har yana fadin ba Domin mugun kalaman bakin Baba akansa ba wlh da sai ya Sakeni sai naje Goggon ta auramin Isa ko Yusuf cikin manyan ya"yanta sannan ya kara jamin kunne akan yaya mariya da gaske yake yi kada ta kara zuwarmai gida in kuma wlh tallahi ya kara ganinta sai ya wulakantata. Na Dago kaina cikin Hawaye muryata ta shake cikin wani yanayi nace"Kayi hakuri..Ba..zan iya fada mata ta daina zuwa ba ne" Sai kawai na Fashe da kuka Tsawa ya Dakamin yana fadin"To ni zan gayamata in muka hadu Tunda gidan nan nawa ne ina da iko da shi kada na kara ganinta acikin su..In kina Tunanin yar'uwan ki ce in kun had'u wani waje sai ku gaisa ammh ba"a gidana ba kin ji maa na gayamiki" Sai na kasa mgana kaina na kasa na Share majina kafin nace"Kayi hakuri don Allah.." Mikewa yayi a fusace yana fadin"Ke dai kika sani kin dai ji abunda na gaya miki..daman abunda ya kawoni kenan Har ga Allah bana son zama agidan nan chan yafiye min kwanciyar Hankali ki kula Fa'iza kada a kara kirana afadamin an hada baki dake an tozarta uwata in hakan ta kara Faruwa zan manta kalaman Baba da komai kema na wulakanta Rayuwarki wlh" Daman Tozarta ne yazo yi kuma yayi washegari tun Safe ya Dauki hanya,ko sallama bai min ba sai zuciyata ta kara Kek'ashewa na kara Fahimtar cewa ni din ba kowa bace a zuciya Ishaq da duka ahalinsa akwai yuyuwar na nemi abunda zan tsaya da kakafuna ko Saboda gaba da kuma ya'yana domin na Lura hankalinsa yayi gaba daidai da su Yaran ya daina Damuwa da su Sosai. Tun tafiyar nan da yayi sai da yafi wata bai zo ya ganmu ba,Kudin Hannuna duka ya kare bamai lekomu dagamu sai Allah,kayan abincin mu sai ya kare mun fara shiga yanayi sannan ake aiko mana da Cefane wani Lokacin Direban gidan Anty Binta ko Badariya,a wannan gabar sai da yayi wata biyu da kwanaki sannan yazo ya ganmu shima din sallama suka zo yi Zasu tafi Umra shi da Zeey da iyayanta gabadaya har da ita Zeey din suka zo sallama kwana D'aya suka yi suka koma gidan Mama kuma suka Sauka sai da Safe suka zo min sallama,nayi masa korafin Haruna ya fara mganar rashin biyansa akan Lokaci sai ya fara masifan bazai iya ba gaskiya shi bashi da kudi kuma haka ya tafi bai bani ko sisi ba,Daganan na kuduri niyar bazan kara mai mganar ba Zan neman ma kaina mafita,Bani da wata mafita alokacin sai na maida lamurana wajen Ubangiji na rokensa yaga Halin da nike ciki da ni da ya'yana ya Gaggauta sama min mafitan da zan kula da kaina da ya'yana. *Janafty**KANA NAKA..!* *Wattpad:JamilaUmar315* *Mallakar:Janafty* *Arewabook:Jamilaumarjanafty* MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866 INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866 *Wacece ZAINAB...?* Cikakken sunanta shine Zainab Lawal bako asalin duka iyayanta uwa da uba Fulani ne gaba da baya,Mahaifiyarta Hajiya Halima bata yi karatun boko ba Saboda yar asalin rugar Njob'oli ne fulani Jahar yola,Shi ma Dr.Lawal din, Mahaifinsa ya'yan maza suke da Mahaifiyar Hajiya Halima auran zumunci ne iyayansu suka kulla a tsskanin ya'yan nasu. Shi Dr.Lawal a cikin garin Yola ya girma kuma nan aka haifesa saboda Mahaifinsa ya baro cikin Ruga saboda neman ilimi kuma ya samu Dalilin da yasa bai koma cikin ruga ba kenan sai dai Lokaci bayan Lokaci yana zuwa Dubasu,Sannan shima matarsa Daga Rugar aka aura masa shiyasa shima Alhaji Lawal aka ki bari ya bar gida. Alhaji Lawal bako yayi karatun Boko har matakin Phd dinsa ya fara aiki da Hukumar Tattara haraji ta kasa reshen Jahar Yola,kuma achan ya fara zama bayan an aura masa Halima,Da farko yaso ya Bijirema auran ne,ganin kamarsa mai ilimi dan gayu a had'asa da yar Rugar da batasan komai ba Sai dai ya sauya shawara lokacin dayaje yaga Halima sai yaji zai iya auranta Saboda Tana da kyau Farace doguwar Bafullatana,ga gashi har gadon baya Hancinta har baka kyau kamar ita tayi kanta sai yaji alfahari ya karun masa Saboda Shi yana son abu mai kyau wanda zai zame masa abun Alfahari watarana. Bayan auran su a yola suka fara zama,Ya na son Halima sosai,Saboda kyanta da sanyin Halinta,sannan Bafullata ne irin sa,Abu daya ne yayi mata cikas rashin ilimin Boko na addinin ma ba sosai take da shi ba Saboda ko acikin Rugar ba kmar yanzu da gwamnati ke basu tallafe tallafe domin inganta ilimi a rugga ba, Yaso ya barta tayi karatu ammh Saboda Tsananin kishinsa yasa bai barta ba,kuma taso tayi karatun tunda ta dawo cikin gari da zama,ammh ya hanata saboda Yana da Tsananin kishi,bazai jure ganin ta a makaranta tana gwagwamarya cikin maza ba,Sai ya hanata ya nuna mata ilimi mace shine zaman gidan mijinta ta kula da ya'yanta dalilin haka yasa