← Book details Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 166 OF 175

Sashe 166

Kana Naka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Engr ya auro bakidajiya" Kallona kawai ya yi bai yi mgana ba ni kuma ban lura da yayi fushi ba. Tunda ban taba ganin Fushinsa ba sai da mukaje wajen liyafar naga ya rage Fara'a ko hirar da ya sabamin sai sama sama. Ko a wajen duk wanda yazo yi mana murnan aure in da Turanci ne shi zai amsa in yaganka bakajin Hausa sai ya kyaleka in kuma kai bahaushe ne sai yace maka"Ka yi mgana da Hausa Matata bata jin Turanci" Ba da wulakanci ba, da Mutuntatawa Saboda kada naji kamar an wareni,Liyafar mazan kowannen da matan su da ya'yan su,gaskiya yare da Wad'anda ba musulmai ba sun fi yawa Hausawan mu ba su da yawa sosai Bamu jima ba awa biyu ne an ci an sha an kuma yi Hotuna sannan mun samu kyattukan kudi da Flowers na masoya sai greeting card na fatan alheri. A gajiye muka dawo gida Engr har kayan barci shi ya sakamin bayan nayi wanka sannan ya yi min Tausa sai dai baya min hira,ni kum sai naji ban ji dadi ba daya kwanta bai rikoni ajikinsa kamar yadda ya saba ba,duk sai naji ban ji dadi ba na fara batama mutumin da ke min hidima da jikinsa da aljihunsa mutumin dake kaunata Saboda Allah. Sai na matsa kusa da shi na Rungumosa ta baya ina fadin"Kayi hakuri bazan kara ba. " Shuru yayi bai yi mgana ba sai da yaji na kara rumgumesa ina fadin"Kaji bazan kara ba" Sannan ya juyo yana kallona kafin ya sakani ajikinsa gabadaya yana Fadin"Bana so Fa'iza. bana son irin wad'anan mganganun suna fitowa daga bakin ki, ni na ganki nace ina sonki ba gayyata ta kika yi ba,kuma ba tallarki aka kawomin ba. ni na ganki nace naji na gani ina sonki a haka so a i don't care da mganar kowa kin gane" Dole na gyad'a masa kai jikina a sanyaye kafin nace"Kayi hakuri" Kai tsaye yace"Na yafe miki ma tun kafin ki nemi afuwata" Sai na kara lafewa saman kirjinsa ina ajiyar zuciya. Ranar dai ba'ayi shagali ba sai da asuba da safe ma kafin ya tafi wajen aiki sai da ya kara,lalubata ni ko fad'i nake"Baka gajiya..? Sai kawai yace min"Zan fara Zagayowa ma ina karb'an na rana" Duka na d'agakamai a baya ina Fadin"A'a wlh..". Saboda nasan Halinsa wlh zai aikata abunda ya fad'a. Zaman mu cikin kwanciyar Hankali da Fahintar juna gaskiyan Engr ne da yace me na sani akan Abdulbasit sai da na zama ya fara gudana Tsakanin mu na ke Fahimta waye na aura..? Engr mutum ne mai dad'in zama,mai addini da cika Lokacin sallah,mai gaskiya da rikon Amana shi mutum ne dan free bashi da kumbiya kumbiya duk abunda ke ransa zai fad'a maka sai dai kaji Haushi,sannan mutum ne mai girmama ra'ayin wanda yake tare da shi,komai nake so wlh shi yake min bai taba cewa nabi na shi ra:ayin ba. sai dai ma shi ya bar na shi yabi nawa ra'ayin a koda yaushe mganarsa shi ne yana girmama Ra'ayin mutane shine zaman lafiyan ka da su. Ya fahimceni nima na Fahimcesa,abunda nasan yace min baya so ina nesa da aikata shi,shima Duk abunda yasan bana so wlh tallahi ko kusa da shi bazai Kusanta ba .ban taba tunanin watarana ni Faa'iza zan zama haka ba. Ban taba tunanin yau ni Fa'iza zan samu abokin rayuwa irin Engr ba. koda yaushe na kallesa kara godema Allah nake yi,duk weekend muna Fita wayo ni da shi sannan ranar a waje muke cin abinci,kamar yadda yace duk inda ya saka kafarsa nan nake maidaa nawa kuma bai taba jin kunyar nunani a matsayin matarsa ba. Mun sha had'uwa da abokan aikinsa Cikin Fariya zai nuna ni yana fadi'n"Meet my Wife Fa'izaa.." Ban taba ganin mutum irin sa ba,shi dai kawai na kasance cikin Farinciki shine Burinsa,yana da tarin ilimi in yana Turanci kamar bature,sannan wani abun da ya kara Burgeni da shi ko waya zai yi da yan'uwansu na benue sai yace min"Zamu yi fa yaren mu kada kiji wani iri Faa'iza.." Ko kuma in yana waya da su Kafayatu da yake su ba su cikamai mgana da Hausa ko Turanci ba, sai ya nemi izinina kan zasu yi mgana da yaren su da nace meyasa yake neman izinina sai yace"Kada ya shigga hakkina naji kamar suna yi da ni" Daga ranar na kara ganin kimarsa da Darajansa sannan ya samu babban matsayi a rayuwata. Iyayensa kuwa tsakanina da su sai Godiya bayan kwana biyu sai sun kirani suna tambayata lafiya ta Papa da Maaa kamar diyar su suka Daukemi. haka suma su kayafatu nima kuma na saki jiki da su kamar yan'uwa na,nima ina kiran su tunda kudi yake sakamin kamar bai san zafin su ba. koda yaushe nima cikin waya nake yi da yan'uwana. Su Anum kuma bai wuce a sati mu yi mgana sai biyu ta wayar zainab ba. Engr har mgana yayi zai siya musu waya nace Babansu bazai bari ba Daganan bai kara mgana ba illah cewa da yayi wannan tunani ne shima mai kyau. Sannan bai taba Tursasani akan na sauya ra'ayi kan karatun Boko ba. sai ma supporting dina da yake kan ra'ayi na ba ruwansa yace ni ya ke so kuma Dole ne ya girmama Ra'ayi na. karatu nace ba na so. wlh bazai taba min Dole ba ranar da nake da sha'awa ko na furta masa ko wata makaranta ne zai kai ni nayi karatu har sai nagaji. Watan mu biyu da zuwa Edo Engr yace na shirya zamu je Lagos na zata zan rakasa wani aiki ne,ashe Hutu zamu tafi tafiya ce mai mikakkiya. Tafiyar mota muka yi kuma bai sa na Dauki kaya masu yawa ba a hotel muka kwana ranar sai da safen yake fad'amin London zamu je ya dauki Hutunsa na karshen shekara zamu sha Honeymoon yadda zai ji dadin yin kara'in sa sosai. Da nace ban fad:a kowa ba sai yace shi ya sanar da Abba baki na bude kafin nace"Kace mai me..? Kai tsaye yace"Nace masa zamu je Honneymoon mana sannan na fad'amasa kila ma sai kin samo ma su Amir kani ko kanwa zamu dawo" Nasan fa zai fad'a hakan din yasa kunya kamar Abba na gabana da yasa ma na kasa kiran shi wlh. Zuwana Lagos sai ya tasomin da kwad'ayin ganin ya'yana da na yi ma Engr mgana sai yace min na bari in muka dawo ta nan zamu sauka zamu je mu gansu. sai na bar mganan Saboda zama da shi na Fahimci yadda yake Daraja kowata mgana ko shawara da ta fito daga bakina, na kuma san tunda yace to haka din zai kasance. Kwanan mu biyu a lagos kafin jirgin mu ya tashi zuwa London Ranar an ga rawan banjo da rawan jiki a gurina haka na rike Engr da jirgi zai karta tashinsa sai da jikina ya juya,kamar zan yi fitsari karshenta dai har da zawo sai da Engr ya rakani Tiolet din Jirgin nayi,Allah yasa ma muna Vip ne,Kunya duk ta kamani sai daga baya bayan na dawo hayyacina na kalli Engr ina fadin"Kayi hakuri ban taba hawa jirgi ba ne" Sai hawaye sharr sai ya kamani ya Rungumeni yana fadin"To meye aciki..? Ai jirgi yanzu kika fara hawa Hajiya ta" Ai ko dai domin kwana goma muka yi a london mun yawata sannan ta bakin Engr ya gwangwanji amarcinsa nima ai na yi amarcin nayi kiba nayi Fari kamar bani ba na samu hutu,Hutun da ban taba Tunanin zan samu ba. Daga London Dubai muka je muka yi sati Biyu shima mun yawata naga manyan Dogayen gine gine sai da na zama yar kauye daman chan yar kauyen ce munje mun yi siyayya katin bankin Engr na Hannuna yace na daukan ma ya'yansa tsaraba tunda zamu sauka a wajen su kafin mu koma Edo. Daga Dubai sai Mumbai India shi kam garin ya yi min dadi mune har Cinema kallo, tsukewa cikin Riga da wando yanzu tuni na kware akai,sai dai bana yadda na bayyana jikina Tunda nasan Halin mijina. Duk inda muke muna tare da juna hannayena na makale cikin nasa Hotuna ko ban san adadin da muka Dauka ba da ni da shi,ina kallo kaina ina kara tuna ni ce dai Fa'izan nan da bani da komai ban mallaki komai ba. nice yau ke zagaye kasashen ketare a haka a yadda nake din nan, Allah shi bakayi masa Dubara sannan ka sani abunda ka raina watarana shi zai tsole maka ido. Duka yawon mu da muka gama a Saudiya muka yada zango Lokacin an fara Umra sai muka yi ta Ibada a Masallaci muke yini sai dare muke haduwa mu tafi masauki. Wata daya muka kwashe a Saudiya kafin mu fara shirin tafiya Lokacin da naganni gani ga ka'aba sai kuka nayi ma yan'uwa na Addu'a tare da yara na da Mijina,sannan na rikor ma kasata zaman lafiya tare da Allah ya bama iyayena aljannah,tare da sauran musulmai gabadaya. Ta Lagos din muka sake sauka kamar yadda yace,kuma tare da kayan mu muka taho Tunda Engr ya saki kudi ni kaina Sauran kayan nawa duk achan ya siya mana wasu na sawan,ba wanda ban yi ma Tsaraba ba Paapa maa,su kafayatu har da Hajiya Kudurat sai su Amir da Abba da sauran yan'uwana Tunda in ban Siya ba Engr zai ce kin ko yi ma wance Tsaraba..?in nace A'a sai yace to nayi ma kowa da kowa shi ya bani Dama. Sai da muka Huta na kwana Hud'u sannan Engr yace na kira Anty Fadila Tunda gidanta zamu fara zuwa kamar yadda na bukata Daman wayata kasheta nayi,lokacin da taji ina Lagos zamu zo ni da Injiniya ta saka ihun murna tana jin dadi. Tace tana asibiti ne ammh zata dawo sai ta turomi lambar babansu Falaq Engr ya kirasa shi ya bashi address din,Tashar Taxi muka yi tunda Direba da mota chan Edo muka barsa. ya ma ce Kano zamu je daga Lagos mu gaida Hajiya Tafeesu tana ta korafin bai kai mata ni ta ganni ba. Riga da wando na saka Baki da Fari sai na Dora wata riga mai zif ta gaba kamar aftar dreess na yane kaina da mayafi fari,sai na saka takalmi mai tsini yana da
Chapter 166 · 0% Book details