← Book details Sauyin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 118 OF 128

Sashe 118

Sauyin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Kasancewar gidan ba kowa sun fita zuwa gona daga nan su zagaye gari da maimartaba daga Nihal sai sultan ke gida Nihal na hada masu kaya cikin trolley a cewar su idan sun gama abinda suke zasu biyo su, kasancewar gobe suke sa ran komawa gida sultan na zaune saman bed yana dana system yana shan coffee Nihal dake kokarin wuce shi rike da shirt din shi zata saka cikin trolley, fisgo ta sultan yayi ta fada saman kirjin shi far da ido Nihal ta mashi tana cewa, "rigima ko ka bari na gama hada kaya nan kaji love idan na biye maka sai mu kai gobe bamu hada komai ba tun jiya kake min haka dana fara hada kaya sai ka hanani" binta da idanuwa sultan yake, ya amshe rigar hannun ta yace, "hayaty ki zauna ki huta zan cigaba da hada kayan bana so kina zarya kina wahala min da baby" yar dariya mai sauti Nihal ta saki tana zagaye hannu ta a wuyan shi tace, "love hada kaya ba wani aiki bane yanzu zan gama sai mu fita mu zaga gari ko mu bi su Ammi" Nihal ta ida zancan tana kashe mashi ido ta rarafa zata sauka daga saman bed jawota sultan yayi yana mata cakulkuli dariya Nihal take tana cewa, "na lura baka so na hada kaya" kwace kanta Nihal tayi tana daukar pillow tana tilawa sultan yana biyo ta yana dariya suna zagaye dakin tana mashi gwalo da gudu Nihal ta fice daga daki tana gudu tana sakowa daga stairs sultan na binta har suka iso main parlour a nan sultan ya samu nasara daukar ta cak yana juya ta tana dariya, knocking din kofar da akeyi ne yasa su natsuwa suna kallan juna cikin muryar mai dadi Nihal tace, "sauke ni na bud'e kofa ina tunani su mom sun dawo" makale kafada sultan yayi yana nufar kofar Nihal na cewa, "love ka sauke ni mana ka sani ko bakin kunya ne tana maganar," tana zaro ido kara matse ta sultan yayi yana cewa, "to minene matata ce na dauka" ya ida zancan yana kashewa Nihal ido ya murda kofar yana murdawa Nihal ta rintse ido turus sultan yayi yana bin Sara da kallo ita ma sakin baki tayi da hanci tana kallan shi tana kallan Nihal kamar ba yan kasa ba tana jinjina gata da Nihal ta samu da tatali, waro ido Nihal tayi ganin Sara ya sata durowa daga rukwan da sultan ya mata tana murmushi tana maida gashin ta baya cike da kunya tana kallan sultan tace, "Sara shigo mana kin tsaya bakin kofa" Nihal ta ida zancan tana murmushi pack sultan ya sakar mata a kumatu yace, "bari naje na dawo" toh Nihal tace, har a lokacin Sara na rab'e da kyar ta iya gaishe da sultan da ze wuce ta sannan ta ida shigowa tana bin parlour da kallo hannu ta Nihal ta kama ta ce, "shigo mana sai wani bin bango kike sai ka ce bakuwa" murmushi Sara ta saki ta shigo ta zauna saman kujera Nihal na dauke pillow din kujera da suka watsar sannan ta bud'e fridge ta ciro mata dirks masu sanyi da kayan marmari sannan Nihal ta zauna tana cewa, "ya muka ji da hakuri Sara?
"an gode Allah"
"Allah ya ji kanta" murmusawa Sara tayi tace, "Amin," Nihal tace, "ki ci mana ko ruwa naga kin kasa sha, ya umma"
"Umma na nan Lafiya lau tana ma gaishe ki" zamowa Sara tayi daga saman kujera ta kama hannun Nihal dake zaune tana cewa, "bani da bakin da zan rukeki gafara abinda iyaye na suka maki Nihal na rokeki ki yafewa iyaye na ko zasu zamu sasaucin azabar da suke sha" hawaye ne suka gangarowa Nihal ta kauda kai tare da zame hannu ta dake cikin na Sara cikin sanyi murya tace, "idan dai ke ce Sara na yafemaki amma maganar su Baffa mu daina ta please karki yanke mana farin cikin da muke ciki yanzu" Nihal ta ida zancan hawaye na gangaro mata shuru Sara tayi hawaye na wanke mata fuska bakin ta na rawa tace, "Nihal..! daga mata hannu Nihal tayi tace, "bana san irin wannan maganar idan har kin san ita zaki min kofa bude take kina iya tafiya idan kuma ba ita bace ki zauna mu cigaba da hira mu cikin jin dadi" Nihal ta idan zancan tana murmushi yake shuru Sara tayi tana bin Nihal dana mujiya, ba yarda Sara ta iya haka ta ja baki tayi shuru ko jan ta a jiki da Nihal ta keyi tayi kokari ba kadan ba nan Sara ta saki ciki tana cin kayan marmarin da Nihal ta kawo mata tana ci Nihal na jan ta da fira sama-sama har ta gama ci kiran sallah la'asar ne ya tashe su tare suka gabatar da sallah bayan sun idar Nihal ta ja Sara bedroom trolley din ta Nihal ta bud'e tana murmushi ta cire kayan sultan dake ciki, ta fara zaro nata tana gwadawa a jikin Sara tana murmushi ganin yarda kayan suka mata kyau yasa Nihal jawo Sara gaba dressing mirror tana murmushi Sara ma murmushi ta saki mai had'e da hawaye tana jinjina alkairi irin na Nihal cikin muryar ta mai dadi tace, "shiga toilet ki gwada" haka Sara ta shige toilet ta gwada kayan ta fito tana bin bango washe baki Nihal tayi tana cewa, "masha Allah kayan sun maki kyau" jawo hannu Sara tayi tana juya ta tana murmushi tace, "kayan sunyi maki kyau sosai" murmushi Sara ta saki tace, "na gode Nihal bani da bakin da zan gode maki" Sara ta ida zancan tana sakin kuka bata fuska Nihal tayi ta ce, "bana san irin haka Sara" ta ida zancan tana rungume ta haka Nihal ta ta kwashe kayan sultan dake cikin trolley din ta gabaki daya kayan ta taba ma Sara har da trolley din, kala biyar kawai ta bari suma saboda ta samu na canza wa anjima sai kuma kayan da zata sa gobe su tafi godiya Sara ta rinka zubawa Nihal tana hana ta har su Ammi suka dawo gida Sara nan sai kusan yamma likis Nihal tasa driver ya sauke Sara gida.

Tunda driver ya aje Sara ta fara ganin yan unguwar tsaye a kofar gidan su sunyi cirko-cirko da alama gulma ake, gaban tane ya yanke ya fadi, da gudu ta karasa ciki abinda ta ganine ya sata shock Baffa ne mace a tsakar gida Dara na gefe tana rokwan liman ya taimaka ayiwa tanimu sutura kowa ya kasa daukar gawarshi saboda yarda yake wari naman jikin shi na zagwayowa, wasu irin hawaye ne suka wanke ma Sara fuska daga daki ana juyo ihu gwoggo na hauka gefe guda kuma yan unguwa na zagin su har suna cewa dama irin wannan mutuwar ta dace da tanimu kowa na fadin albarka cin bakin.

```Taku har kullun salma mas'ud nadabo```[3/6, 2:18 PM] Sister: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🕊 *SAUYIN RAYUW* 🕊
💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞
*Story*
*And*
*Writing*✍🏾
*By*
*Salma mas'ud nadabo*👑

🌲 *REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM*🐄
(```We are the best among the rest```)

*page: 135_136*

Innalillahi wa'inna ilaihi raju'un Sara ke anbata ta rushe da kuka tana kallan Dara dake faman rokwan liman ya amshi gawar Baffa gefe gudu yan unguwa na fadin albarkancin bakin su marasa dadi, Dara kuwa kuka take sosai har cikin zuciyar ta take jin ta yafewa Tanimu duniya da lahira domin Allah yayi kuncin tun a nan gidan duniya, duk yarda Dara taso liman ya amshi gawar Baffa ayi mashi sutura fir yaki haka liman ya fita Sara ta bi shi a baya bakin kofa ta duke tana gunjin kuka Dara dake gefe tace, "ni yanzu ya zamuyi da gawar yaya" Sara da dake gunjin kuka tace, "koma me ya faru Baffa shi ya ja mana, tun a nan gidan duniya gawar shi ta fara wulakanta"
"Kul karna kuma jin irin wannan furucin a bakin ki addu'a akewa mamaci ba fadin maganganu mara sa dadin jin ba, ko duniya zata fadi magana mara dadi ke mahaifin ki ne addu'ar ki yake bukata, Allah ya ji kan yaya ya gafar ta mashi" Sara dake kuka tace, "Amin" ganin ba sarki sai Allah yasa Sara fita da gudu zuwa masaukin su Nihal, kafar ta ko takalma babu har ciwo taji a kafar ta amma bata damu ba burin ta ta isa masaukin su Nihal tana gudu yan gari na nuna ta da baki.
Chapter 118 · 0% Book details