Sashe 19
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk yadda Taj yaso ya fahimtar dashi amma Yaƙi ya gane, ba don yaso ba, Ya amince mashi akan suyi Bincike akansu, don su samu hujjojin da zasu fallasa su, har hukuma ta ɗauki mataki a kansu, Tun daga wannan Lokacin Suka soma tunanin ta ina zasu fara neman su, A ƙarshe Uzair ne ya ba shi shawarar su koma inda suka fara ganinsu acikin dajin nan, Cikin sa'a ranar da suka je again suka sake ganin miyagun mutanan nan sun kamo wani mutumin, kamar yadda suka kamo malamin nan, da alama Leƙen asiri shima Yayi masu, Akan idonsu suka koneshi, ranar Taj hankalin shi ya tashi matuƙa har yace ma Uzair shidai zai Cire hannun shi, kusan faɗa sukayi da uzair akan hakan, daƙyar suka sasanta kansu, kuma suka Cigaba da bibiyan Alhazawan nan, Sai dai duk wannan tsawon lokacin da suka ɗauka suna Bibiyarsu Allah bai basu damar sanin kosu wanene su ba, daidai da fuskokin su ba su sani ba, Abu ɗaya kawai suka sani inda suke yankewa mutum hukunci wato Cikin dajin nan a bakin ƙorama, Abunda su taj basu sani ba, duk wani motsinsu akan idanuwansu suke yin shi, Sunsan komai game da bibiyar su da su ke yi zuba masu ido kawai su kayi, yayin da su basu san da hakan ba, Lalube kawai su ke yi acikin duhu............
Ganin babu Riba a bindiddingin su da sukeyi ne yasa Taj ya cire hannun shi, uzair kuma yasa naci Akan binciken shi, duk yadda taj ya gargaÉ—eshi amma Ya sanya kafiya, ashe ajaline ke kiran shi.
*************************
A daren Ranar Alhamis ne Wannan mummunan ƙaddarar ta riskesu wadda tayi silar rasa rayukan su,
Wuraren ƙarfe 9 na dare, Taj na zaune tsakiyar gadon shi, ya tasa laptop ɗinshi agaba yana ta ƴan danne danne acikin, har ma ya yi shirin kwanciya singlet ce ajikin shi tare da short, wani aiki ne ya tsayar da shi, Allah Allah ya ke yi ya gama aikin ya je ya kwanta, sai hamma yake yi, ba zato ba tsammani yajiyo bugun ƙopar falo,
Agogo ya kalle, Cike da mamaki Ya sauko daga saman Gadon ya fito ɗakin ya nufi cikin falon, a baƙin ƙopar ɗakin ya tsaya tare da tambayar wanene? Daga waje yajiyo muryar aneeleerh,ka bude mun kopa nice" muryarta Cikin shessheƙar yaji sautinta, jiki na rawa ya buɗe mata ƙopar har saida gaban shi ya faɗi ganin Yadda fuskar ta tayi jawur saboda kukan da ta sha, kayan Bacci ne ajikinta riga da wando sai mayafin data yafa akanta, gefen goshinta kwantaccen gashin kanta,
AruÉ—e yace"Aneelerh? Lafiya? me meya faru ne? Ya akai naganki acikin daren nan'?
Daƙyar take iya kallonshi, da runannun idanuwanta wadanda suka yi jawur da su,
"Uzair ya fita bansan inda yaje ba Cikin daren nan, na farka bangan shi ba, hankalina bai kwanta ba, na je wurin baba mai gadi don in tambaye shi ko sun yi magana da uzair kafin fitar shi, yace mun eh sunyi magana da shi kafin ya fita amma bai faɗa ma shi inda zaije ba,......" tunda ta soma magana hankalin taj ya ɗungunzuma, jikin shi ya soma kakarwa, fargabar shi kada ace uzair ya tafi Wurin mutanan nan, dama yace mashi bazai fasa bindiddiginsu ba, idan kuwa hakane to kuwa tabbas yaje yi masu leƙen asiri ne,
Jin yayi shiru bai ce mata komai ba yasa tace"ko kasan inda ya tafi ne"? girgiza mata kai yayi alamar a'a, saboda bai son ya tayar mata da hankalinta,
"Kin kira layin shi"? ya yi tambayar yana kallonta,
"Na kira shi har bansan adadi ba, Amma bai ɗaga ba, kuma kiran yana shiga"jinjina kai yayi" Bari na jaraba kiranshi, ki shigo Ciki ki zauna" yakai ƙarshen maganar yana nuna mata sofa,
Cikin sanyin murya tace"bazan Iya zama ba," tausayinta duk ya kamashi, bedroom dinshi ya koma a hanzarce Ya kai hannu ya É—auki wayar shi dake a jiye gefen laptop É—in shi, Ya shiga call logs, ya danna ma uzair kira, tana fara ringing, uzair yayi picking call É—in,
Rufe shi da faÉ—a yayi ta inda ya ke shiga bata nan yake fita ba,
"Duk inda kake ka dawo gida yanzu yanzu, kasa baiwar Allah sai kuka take yi, Saboda rashin hankali, Ka kama hanya ƙarfe tara na dare ka tafi ka barta batare da ka sanar da ita inda kaje ba, Anya kuwa kasan me ka ke yi? wai shin ina kaje ne ma.......? duk wannan suratan da taj ke yi uzair baice mashi uffan ba, A ƙarshe ma saiya yan ke kiran gaba ɗaya, jikin taj ba ƙaramin sanyi ba, tunani ya shiga yi wai shin dawa ma yake waya? idan uzair ne meyasa bai yi ma shi magana ba? kuma ya ɗaga kiran Anya kuwa ba'a samu matsala ba, sake kiran Layin ya yi a switched off ya samu wayar, Nan fa jikin shi ya mutu, hankalinshi Ya tashi
Saman bedside drawer Ya É—aura wayar, ya fito daga É—akin ya koma falon, Cike da zullumin amsar da zai ba aneelerh,
Lokacin da ya shigo falon ya ƙaraso inda take tsaye, sai ya shiga Yin ƴan kame kame,
"Bai ɗaga kiran ba ko" ta yi tambayar a ƙagare,
Muryarshi na inda inda yace"Am..um..kingane..eh..muyi waya dashi, ki kwantar da hankalin ki, Yana kan hanyar dawowa gida, yanzu ki koma ki kwanta, kada ki takura kan ki,"
Wani irin kallo yaga tana yi ma shi kallon ban yadda dakai ba, da sauri yace"kiyi hakuri ki koma gida, nan badajimawa ba zai dawo"
Jiki asanyaye Ta juya ta fuce daga falon, Ko bayan tafiyarta saida ya kuma kiranta awaya, Ya ƙara kwantar mata da hankalinta,
Kasa zama ya yi, zarya ya shiga yi tsakanin É—akin shi zuwa palour, ya rasa meke yi ma shi daÉ—i duniyar nan, duk bayan Æ´an mintuna sai ya jaraba kiran Layin Uzair don yaji in ya bude wayar amma a kashe yake samun ta,
Bawan Allah ya rasa ta zama, duk ya shiga damuwar rashin amininsa, juyawa ya yi da sauri Ya haye upstairs ɗakin angel, ya tura ƙopar ɗakin a hankali, ko'ina duhu, ya lalauba jikin bangon ya kunna switch, tare dakai idanuwanshi kanta, Sai bacci take yi, ta ƙudundune Cikin bargo, murmushi ya ɗan saki kafin ya ɗauke i danuwan shi daga kanta, ya mayar dasu kan wall ɗin dakinta, Zanunnukan da tayi ne tare da kalaman da ta rubuta ma shi, a kullum ya kallesu sai yaji farin Ciki acikin zuciyar shi, duk mun baƙin Cikin da yake ciki,
A hankali Yake tafiya cikin É—akin nata, ta 6angaren hagu ya zagaya saitin inda take kwance saman gadon, Kneel down Yayi tare dakai hannu Ya yaye blanket É—in data rufa da shi, rigar bacci ce ajikinta,
Kyakkyawar fuskarta Ya ƙurawa ido yana kallonta, Hakanan ya dinga jin bugun zuciyar shi na ƙaruwa, wani irin matsanancin faduwar gaba, a cikin zuciyarshi ya shiga ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" ya ambaci hakan ba iyaka,
"Daddy" muryar ta ce ta katse shi, kallonta yayi ganin ta buÉ—e manyan idanuwanta a kan fuskar shi,
"Dama bakiyi bacci ba"? murmushi ta sakar mashi tare cewa"Nayi mana, yanzu na farka" hands É—inshi ya sanya ya tallabo fuskarta"Æ´ar kyakkyawata, Allah yabar mun ke,"
"Ameen daddy, gobe uncle da aunty zasu dawo ko sai mu tafi buzaye ? tayi tambayar tana ƙoƙarin mikewa zaune,
Girgiza mata kai yayi"Till next week nake tsammani"
Ta6e baki ta ɗanyi"daddy ka kwana ɗakina yau"yatsina fuska yayi"Gadonki yayi mun ƙanƙanta" cikin zolaya ya yi mata maganar,
Turo mashi baki tayi"To muje ɗakin ka mu kwana" maƙe mata kafaɗa yayi"A'a, kowa ya kwana a ɗakinsa," shagwa6a ta soma yi mashi, sosai ta ba shi dariya, suna Cikin Yin fira, Ya tuna da uzair, Rass yaji gaban shi Ya faɗi, Da sauri ya kali agogo, Ƙarge goma da rabi mayar da idanuwanshi kan angel yayi" ki koma ki kwanta, Sai da safe" yana ƙoƙarin mikewa tayi saurin ruƙo hannunshi da sauri kallonta ya yi idanuwanshi sun taunta sosai, ƙaƙaro murmushi ya yi don ya gane me take nufi, Kiss ya mannata mata a saman forehead ɗinta, Yasa hannu ya kwantar da ita tare da lullu6e mata jikinta da bargo, addu'a ya yi mata, kafin ya kashe hasken ɗakin,
Lokacin daya fuce daga ɗakin yana jiyo sautin muryata tana faɗin"I love u so much daddy, Allah yabar mun kai, ina matuƙar ƙaunar ka habibi" murmushi yasaki A hanzarce Ya sauko down stairs, ya faɗa ɗakin shi, daga gefen gadon shi Ya zauna tare da ɗaukar wayar shi, ya ci gaba da jaraba layin Uzair, still a kashe yake samun ta, Zuciyar shi tajima da karaya, A sukwane ya ɗaura wayar saman bedside drawer, a wannan yanayin ne Bacci ya yi awon gaba da shi, sama sama yake yin baccin na shi, 🥺🥺🥺
Sannu a hankali agogon bangon ke harbawa, yana ba da sauti tik-tik-tik. Sakamakon dare da ya tsala don time din karfe ɗaya da rabi na dare, wayar da ke ajiye saman bed side drawer ƙirar Samsung Galaxy ta soma ruri da ƙarfi gaske. A lokacin ya yi nisa a cikin barcin nasa, kusan sau uku kiran na shigowa yana katsewa. A kira na huɗu ne, sautin ya daki dodon kunnansa, a firgice ya farka yana faman ambaton sunan Allah,
Kafin ya zame hannunsa daga kan fuskarsa wani kiran ya sake shigowa wayarsa a hanzarce ya mika hannu saman drawer É—in ya É—auki wayar,
Lokacin daya kalli screen ɗin wayar Sunan Aminina ne Ya bayyana, ajiyar zuciya ya ɗan sauke dama jiran kiran shi ya ke yi, A tunanin shi ya dawo gida ne, Shiyasa ya kira shi dan ya sanar ma shi game da dawowar shi, picking call ɗin yayi tare da manna wayar a kunnansa tun kafin ya yi sallama, kunnuwansa suka jiyo masa sautin harbin bindugu. A gigice ya furta, "Aminina!" Kafin Ya ƙarasa rufe bakinsa, muryar Aminin nasa ta katse masa hanzari, a ruɗe yake faɗin,"Na ba ni na lalace, shikenan tawa ta ƙare."
A firgice ya dakatar da shi, "Ka nutsu ka yi mini bayanin me yake faruwa ne?"
Ganin babu Riba a bindiddingin su da sukeyi ne yasa Taj ya cire hannun shi, uzair kuma yasa naci Akan binciken shi, duk yadda taj ya gargaÉ—eshi amma Ya sanya kafiya, ashe ajaline ke kiran shi.
*************************
A daren Ranar Alhamis ne Wannan mummunan ƙaddarar ta riskesu wadda tayi silar rasa rayukan su,
Wuraren ƙarfe 9 na dare, Taj na zaune tsakiyar gadon shi, ya tasa laptop ɗinshi agaba yana ta ƴan danne danne acikin, har ma ya yi shirin kwanciya singlet ce ajikin shi tare da short, wani aiki ne ya tsayar da shi, Allah Allah ya ke yi ya gama aikin ya je ya kwanta, sai hamma yake yi, ba zato ba tsammani yajiyo bugun ƙopar falo,
Agogo ya kalle, Cike da mamaki Ya sauko daga saman Gadon ya fito ɗakin ya nufi cikin falon, a baƙin ƙopar ɗakin ya tsaya tare da tambayar wanene? Daga waje yajiyo muryar aneeleerh,ka bude mun kopa nice" muryarta Cikin shessheƙar yaji sautinta, jiki na rawa ya buɗe mata ƙopar har saida gaban shi ya faɗi ganin Yadda fuskar ta tayi jawur saboda kukan da ta sha, kayan Bacci ne ajikinta riga da wando sai mayafin data yafa akanta, gefen goshinta kwantaccen gashin kanta,
AruÉ—e yace"Aneelerh? Lafiya? me meya faru ne? Ya akai naganki acikin daren nan'?
Daƙyar take iya kallonshi, da runannun idanuwanta wadanda suka yi jawur da su,
"Uzair ya fita bansan inda yaje ba Cikin daren nan, na farka bangan shi ba, hankalina bai kwanta ba, na je wurin baba mai gadi don in tambaye shi ko sun yi magana da uzair kafin fitar shi, yace mun eh sunyi magana da shi kafin ya fita amma bai faɗa ma shi inda zaije ba,......" tunda ta soma magana hankalin taj ya ɗungunzuma, jikin shi ya soma kakarwa, fargabar shi kada ace uzair ya tafi Wurin mutanan nan, dama yace mashi bazai fasa bindiddiginsu ba, idan kuwa hakane to kuwa tabbas yaje yi masu leƙen asiri ne,
Jin yayi shiru bai ce mata komai ba yasa tace"ko kasan inda ya tafi ne"? girgiza mata kai yayi alamar a'a, saboda bai son ya tayar mata da hankalinta,
"Kin kira layin shi"? ya yi tambayar yana kallonta,
"Na kira shi har bansan adadi ba, Amma bai ɗaga ba, kuma kiran yana shiga"jinjina kai yayi" Bari na jaraba kiranshi, ki shigo Ciki ki zauna" yakai ƙarshen maganar yana nuna mata sofa,
Cikin sanyin murya tace"bazan Iya zama ba," tausayinta duk ya kamashi, bedroom dinshi ya koma a hanzarce Ya kai hannu ya É—auki wayar shi dake a jiye gefen laptop É—in shi, Ya shiga call logs, ya danna ma uzair kira, tana fara ringing, uzair yayi picking call É—in,
Rufe shi da faÉ—a yayi ta inda ya ke shiga bata nan yake fita ba,
"Duk inda kake ka dawo gida yanzu yanzu, kasa baiwar Allah sai kuka take yi, Saboda rashin hankali, Ka kama hanya ƙarfe tara na dare ka tafi ka barta batare da ka sanar da ita inda kaje ba, Anya kuwa kasan me ka ke yi? wai shin ina kaje ne ma.......? duk wannan suratan da taj ke yi uzair baice mashi uffan ba, A ƙarshe ma saiya yan ke kiran gaba ɗaya, jikin taj ba ƙaramin sanyi ba, tunani ya shiga yi wai shin dawa ma yake waya? idan uzair ne meyasa bai yi ma shi magana ba? kuma ya ɗaga kiran Anya kuwa ba'a samu matsala ba, sake kiran Layin ya yi a switched off ya samu wayar, Nan fa jikin shi ya mutu, hankalinshi Ya tashi
Saman bedside drawer Ya É—aura wayar, ya fito daga É—akin ya koma falon, Cike da zullumin amsar da zai ba aneelerh,
Lokacin da ya shigo falon ya ƙaraso inda take tsaye, sai ya shiga Yin ƴan kame kame,
"Bai ɗaga kiran ba ko" ta yi tambayar a ƙagare,
Muryarshi na inda inda yace"Am..um..kingane..eh..muyi waya dashi, ki kwantar da hankalin ki, Yana kan hanyar dawowa gida, yanzu ki koma ki kwanta, kada ki takura kan ki,"
Wani irin kallo yaga tana yi ma shi kallon ban yadda dakai ba, da sauri yace"kiyi hakuri ki koma gida, nan badajimawa ba zai dawo"
Jiki asanyaye Ta juya ta fuce daga falon, Ko bayan tafiyarta saida ya kuma kiranta awaya, Ya ƙara kwantar mata da hankalinta,
Kasa zama ya yi, zarya ya shiga yi tsakanin É—akin shi zuwa palour, ya rasa meke yi ma shi daÉ—i duniyar nan, duk bayan Æ´an mintuna sai ya jaraba kiran Layin Uzair don yaji in ya bude wayar amma a kashe yake samun ta,
Bawan Allah ya rasa ta zama, duk ya shiga damuwar rashin amininsa, juyawa ya yi da sauri Ya haye upstairs ɗakin angel, ya tura ƙopar ɗakin a hankali, ko'ina duhu, ya lalauba jikin bangon ya kunna switch, tare dakai idanuwanshi kanta, Sai bacci take yi, ta ƙudundune Cikin bargo, murmushi ya ɗan saki kafin ya ɗauke i danuwan shi daga kanta, ya mayar dasu kan wall ɗin dakinta, Zanunnukan da tayi ne tare da kalaman da ta rubuta ma shi, a kullum ya kallesu sai yaji farin Ciki acikin zuciyar shi, duk mun baƙin Cikin da yake ciki,
A hankali Yake tafiya cikin É—akin nata, ta 6angaren hagu ya zagaya saitin inda take kwance saman gadon, Kneel down Yayi tare dakai hannu Ya yaye blanket É—in data rufa da shi, rigar bacci ce ajikinta,
Kyakkyawar fuskarta Ya ƙurawa ido yana kallonta, Hakanan ya dinga jin bugun zuciyar shi na ƙaruwa, wani irin matsanancin faduwar gaba, a cikin zuciyarshi ya shiga ambaton Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un" ya ambaci hakan ba iyaka,
"Daddy" muryar ta ce ta katse shi, kallonta yayi ganin ta buÉ—e manyan idanuwanta a kan fuskar shi,
"Dama bakiyi bacci ba"? murmushi ta sakar mashi tare cewa"Nayi mana, yanzu na farka" hands É—inshi ya sanya ya tallabo fuskarta"Æ´ar kyakkyawata, Allah yabar mun ke,"
"Ameen daddy, gobe uncle da aunty zasu dawo ko sai mu tafi buzaye ? tayi tambayar tana ƙoƙarin mikewa zaune,
Girgiza mata kai yayi"Till next week nake tsammani"
Ta6e baki ta ɗanyi"daddy ka kwana ɗakina yau"yatsina fuska yayi"Gadonki yayi mun ƙanƙanta" cikin zolaya ya yi mata maganar,
Turo mashi baki tayi"To muje ɗakin ka mu kwana" maƙe mata kafaɗa yayi"A'a, kowa ya kwana a ɗakinsa," shagwa6a ta soma yi mashi, sosai ta ba shi dariya, suna Cikin Yin fira, Ya tuna da uzair, Rass yaji gaban shi Ya faɗi, Da sauri ya kali agogo, Ƙarge goma da rabi mayar da idanuwanshi kan angel yayi" ki koma ki kwanta, Sai da safe" yana ƙoƙarin mikewa tayi saurin ruƙo hannunshi da sauri kallonta ya yi idanuwanshi sun taunta sosai, ƙaƙaro murmushi ya yi don ya gane me take nufi, Kiss ya mannata mata a saman forehead ɗinta, Yasa hannu ya kwantar da ita tare da lullu6e mata jikinta da bargo, addu'a ya yi mata, kafin ya kashe hasken ɗakin,
Lokacin daya fuce daga ɗakin yana jiyo sautin muryata tana faɗin"I love u so much daddy, Allah yabar mun kai, ina matuƙar ƙaunar ka habibi" murmushi yasaki A hanzarce Ya sauko down stairs, ya faɗa ɗakin shi, daga gefen gadon shi Ya zauna tare da ɗaukar wayar shi, ya ci gaba da jaraba layin Uzair, still a kashe yake samun ta, Zuciyar shi tajima da karaya, A sukwane ya ɗaura wayar saman bedside drawer, a wannan yanayin ne Bacci ya yi awon gaba da shi, sama sama yake yin baccin na shi, 🥺🥺🥺
Sannu a hankali agogon bangon ke harbawa, yana ba da sauti tik-tik-tik. Sakamakon dare da ya tsala don time din karfe ɗaya da rabi na dare, wayar da ke ajiye saman bed side drawer ƙirar Samsung Galaxy ta soma ruri da ƙarfi gaske. A lokacin ya yi nisa a cikin barcin nasa, kusan sau uku kiran na shigowa yana katsewa. A kira na huɗu ne, sautin ya daki dodon kunnansa, a firgice ya farka yana faman ambaton sunan Allah,
Kafin ya zame hannunsa daga kan fuskarsa wani kiran ya sake shigowa wayarsa a hanzarce ya mika hannu saman drawer É—in ya É—auki wayar,
Lokacin daya kalli screen ɗin wayar Sunan Aminina ne Ya bayyana, ajiyar zuciya ya ɗan sauke dama jiran kiran shi ya ke yi, A tunanin shi ya dawo gida ne, Shiyasa ya kira shi dan ya sanar ma shi game da dawowar shi, picking call ɗin yayi tare da manna wayar a kunnansa tun kafin ya yi sallama, kunnuwansa suka jiyo masa sautin harbin bindugu. A gigice ya furta, "Aminina!" Kafin Ya ƙarasa rufe bakinsa, muryar Aminin nasa ta katse masa hanzari, a ruɗe yake faɗin,"Na ba ni na lalace, shikenan tawa ta ƙare."
A firgice ya dakatar da shi, "Ka nutsu ka yi mini bayanin me yake faruwa ne?"