Sashe 131
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Har yaushe ne zaku kammala amfani da ita ku dawo mata da ita? Nasan kun gane akan wa nake magana, Ƴar uwar mu batul tana ina"? Ranta a6ace take yi musu magana, babu wanda ya motsa, tsawa ta daka musu tare da cewa"Da ku fa nake magana? Nasan kuna ji na, mugaye kawai......" jiki na 6ari danish Ya sauko daga saman gadon shi ya nufi angel ya ruƙo hannunta yana ƙoƙarin janyeta baya, gudun kada su cutar da ita, fashewa tayi da matsancin kuka, Tana bugun Danish akan ya saketa, wlh sai sun fito musu da ƴar uwarsu, Wannan maganar tayi matuƙar ɗaure ma Gabriel, da Unaiza kai, don tuni ta miƙe zaune saman gadonta, idanuwanta luhu luhu take kallonsu, Saboda sautin kukan Angel har na cikin sashen toilet dinsu saida suka fito, hankalinsu yayi matuƙar tashi ganin yadda take kuka tana ƙoƙarin kwace kanta daga hannun danish donta kaima Giants hari, A ƙarshe da ta ga dagaske Danish bazai Ƙyale ba, ta daddage ta gartsa mishi ciwo a damtsen hannun shi tare da sanya hannayenta biyu ta ingije shi gefe ɗaya, taku ɗaya zuwa biyu takai ga farantan kayan abincin da aka kawo musu, Robar ruwa ta ɗauko ta buɗe murfin, Cikin zafin nama ta watsa ma giants ruwan ajikinsu kaf ta zazzage musu shi.
waro ido waje su Parveen su ka yi ganin irin bala'en da take so taja musu, kowa yasha jinin jikin shi, Tana haki tace"Dama nasan bazaku motsa ba, saboda ku ɗin dabbo bi ne, Marasa imani, Allah dai yana ganin ku mugaye, Wlh rantsuwar ɗan musulmi, idan har wani abu ya sami batul sai kun gane ba ku da wayau, domin kuwa saina addabi rayuwarku, inyaso ku kashe ni, kai bazan ma mutu ba bi'iznillahi har sai na ga bayan ku..." Bata kai ƙarshen maganar ba, Danish Ya sake damƙota, kamar ƴar dambe sai harba ƙafarta take yi, ahaka yaja ta har zuwa saman gadonta, Ya jefar da ita, Kafin ya juya ya kalli Sauran yace dasu su je su ci abinci," da sauri suka nufi kayan abincin nasu kowa ya zauna banda Gabriel da Unaiza, kalaman angel sun yi matuƙar ɗaga musu hankali, tunani suke yi wacece batul? Meyasa aka ɗauke ta?
A gefen gadon Angel Danish ya zauna yana gadinta, gudun kada ta ƙara zuwa ta 6allo musu aiki, Shi kaɗai yasan me yae mata, da har tagaza ɗagowa, hawaye sai bin fuskarta suke yi, ta ɗaura kanta saman pillow,
Bayan sun kammala cin abinci sauran da suka rage ma waɗanda basu samun damar xuwa suci ba, acikin kwando suka adana mu su nasu, Giants na fita daga Cikin dakin, Gabriel ya soma tambayarsu wacece batul? su azeeza suka bashi amsa da cewa ƴar uwarsu da aka ɗauka, yaso ya ƙara tambayarsu dalilin dayasa aka ɗauke ta amma Danish Ya hana shi, ta hanyar
Ƙura mishi ido yana kallon shi, nan take yaji maganar ta fita aranshi, bai ƙara tada ta ba.
Yinin ranar babu daÉ—i suka yi shi, Saboda halin da suka shiga na tunawa da Æ´ar uwarsu, Kowa jikin shi yae sanyi, Har marece ya yi babu wanda ya motsa acikin su, majnun ne kaÉ—ai yake ta tsalle tsalle shi kaÉ—ai atsakiyar É—akin su.
Lokacin da marece ya nutsa, Gabriel ya bukaci yin wanka, Saukowa Yae daga saman gadon shi, Ya nufi toilet ɗinsu Ya shiga, bayan yasanya jamlock ya datse ƙopar Ya dan jingina bayanshi Jikin ƙopar, yayin da zuciyarshi ke acunkushe da tunanin abubuwan da suka faru ayau, Tabbas ya razana sosai da gidan kurkukun nan, duk da baisan komai adangane dashi ba amma yana ji aranshi cewa wani abu yana faruwa badai badai ba, Shi bakomai yafi jimawa ba face ƴar uwar shi Gabriella, maganganun da angel tayi ɗazu akan tasu ƴar uwar sun tsara mishi aranshi.
A ƙalla ya ɗauki kusan minti talatin Yana tunani acikin toilet ɗin ba tare daya ta 6uka komai ba, Sai daga bisani ne ya soma ƙoƙarin cire rigarshi, Kwatsam idanuwanshi suka sauka akan Glass window ɗin nan, A wani slow yake kallonta sai yake ganin kamar glass ɗin jikinta bai zauna dakyau ba, nan take ranshi ya bashi cewar Yaje ya duba ya gani, wata'kil ma ya samu hanyar shiga Cikin kurkukun ko dan yaje ya ɗauko ƴar uwarshi, ba tare da yayi shawara da zuciyarshi ba, Ya fasa cire rigar ya nufi tagar, Yakai hannu ya tatta6a jikin glass ɗin Yaji yana girgiɗi, ya daddage ya zame shi daga jikin tagar ya sauke shi ƙasa, wani irin farin ciki ne ya mamaye zuciyarci, bakomai yake hange ba face fuskar sister ɗinshi.
Rashin sani yafi dare duhu, cike da ƙwarin gwiwa Gabriel ya dura tagar ya faɗo ta cikin wannan hanyar da angel ta tsinci kanta lokacin da ta ta6a durawa, hada saurin shi wurin miƙar hanyar, babu wadataccen haske, amma yana iya gani dakyau, yana kaiwa ƙarshenta, Ya faɗo cikin wannan babban filin mai ɗauke da dogayen benayen nan, A hankali yake ƙarewa ginin kallo, bai ta6a ganin wuri mai matuƙar ruɗarwa ba irin wannan wurin, hakanan ya dinga jin faɗuwar gaba, tun daga kan hauwa na farko har zuwa na biyu, a ƙarshe ya tsayar da idanuwanshi kan hawa na uku, ba zato ba tsammani idanuwanshi suka hango mashi kyakkyawar matashiyar budurwa tana gudun ceton rai saman hawa na uku, fara fat kamar fatalwa, Jikinta sanye da riga ja, wadda bata kai gwiwarta ba, fararen cinyoyinta santala santala, daga gani babu hankali atattare da ita, tana gudu tana waiwayon bayanta, ga uban gashin kanta dake yarfowa harta saman idanuwanta, hakan yasa ta dinga faɗuwa ƙasa tana miƙewa saboda bata ganin gabanta dakyau, wani irin tsorone ya ziyarci zuciyar Gabriel, Ganin tana saukowa daga saman benan mai hawa talatin, Girgiza kanshi ya dinga yi, zufa tako ina saman fuskarshi, Ya rasa gane shin mutunce ita ko aljan, ko kuma fatalwa ce, Idanuwanshi ne suka dinga nuna mashi kamar sister ɗinshi ce, sai dai akwai banbanci sosai, Ƴar uwarshi ba fara bace, kuma bata da tsayin sumar kai da yawa irin na wannan yarinyar, ' A tsorace ya juya zai koma hanyar daya fito, A lokacin harta ƙarasa saukowa saman benan, sai miƙa mishi hannu ta ke Yi, tana magana sautin muryarta sam baya fita, ranshi ne ya bashi cewar Ya juya ya kalle ta, ya ɗan dakata ya waiwayo baya yana kallonta, sai jan ƙafarta take yi, saboda nauyin da tayi mata, Taya zai iya yarda cewa mutunce ita? Bai gama yanke shawara da zuciyarshi ba, yaga ta faɗi ƙasa kanta ya bugu, ' Gaba ɗaya sumar kanta ta rufe mata fuskarta, Tsananin tausayinta ne ya kama gabriel, koma dai aljana ce wannan ba ƙaramin jiki taji ba, sai motsi take yi alamar tana son ɗagowa da kanta amma ta kasa, kuma duk da tana kwance ƙasa hakan baisa ta fasa miƙa mishi hannunta ba, yayi niyar yaje wurinta amma sai yaga Benayen dake awurin sun soma motsi suna yin sama da ƙasa, Ya zazaro ido ganin suna tunkaro shi, aiko da gudu ya juya ya bi ta hanyar daya fito Ko waiwaye babu ya koma bakin tagar nan, Allah ne ya taimake shi bai 6ace hanyar ba, Jiki na kerma ya haura tagar Ya dura Cikin toilet ɗinsu Yana ta haki, Sai da ya samu natsuwa tukunna yakai hannu ya ɗauki glass ɗin daya jingine jikin bango ya maida shi jikin tagar kamar yadda ya ganshi,
Kamar amafarki yake tariyo abubuwan da suka faru Cikin ƙanƙanin lokaci, zuciyarshi cike fal da tunanin matashiyar yarinyar nan daya gani .............."!
💋PRISONERS💋
Ya jima tsaye jikin tagar ba tare daya motsa ba, zuciyarshi na raya mashi akan ya koma ya taimake ta, sai dai tsoro ya hana shi yin hakan, Ajiyar zuciya ya sauke tare nufar cikin toilet ɗin, wankan ma da ya shigo da niyar yi ya fasa, ƙopa kawai ya buɗe ya fito ya shiga ɗakin su.
A zazzaune ya same su saman gadajen su, angel ce kaɗai kwance saman nata gadon da alama bacci ya ɗauke ta, tunda Gabriel ya shigo idanuwanshi na akan kowannan su, damuwace danƙare akan fuskokinsu, In ka cire mutun uku, Majnun da jamima da ke ta yin rawa tsakiyar ɗakin su, yau ta biye mishi suna wasa a tare, duk da a shekaru Majnun ya girmi Jamimah.
bayan su sai Sarah dake yanke akaifar hannunta da nail cutter ɗinsu, tana zaune saman shimfidarta dake a ƙasan gado, don ita tuni ta yafe hawa gado, komai nata a ƙasa take zama ta yi shi, Hankalin ta kwance babu damuwa akan fuskarta, Danish yana daga kishingiɗe saman bed ɗinsa, ya ɗan lumshe eyes ɗinta, sam babu walwala akan fuskar shi, Azeeza tana zaune saman gadon parveen, ta ɗaura kanta saman shoulder dinta, magana su ke yi ƙasa ƙasa a takaninsu, haris da deeja suna fuskantar juna, sun nutsa cikin tattaunarsu duk dai akan Batul ne, idan muka koma 6angaren su Hanna ita da hibba da Yasmin da eve da rubina kowaccensu na kwance saman gadonta, sun yi likimo kamar masu yin bacci, Zuciya ce ba daɗi, dole jiki yai sanyi, yar gida daddy kuwa bacci ta ke yi sai dai ga dukkan alamu babu lafiya ajikinta, kamar zata faɗo daga saman gadonta, a cikin bacci take murza cikinta da hannunta na dama, idanuwanta sun kumbura, ga sahun marin da Danish yai mata gefen fuskarta kamar jini ya kwanta.
waro ido waje su Parveen su ka yi ganin irin bala'en da take so taja musu, kowa yasha jinin jikin shi, Tana haki tace"Dama nasan bazaku motsa ba, saboda ku ɗin dabbo bi ne, Marasa imani, Allah dai yana ganin ku mugaye, Wlh rantsuwar ɗan musulmi, idan har wani abu ya sami batul sai kun gane ba ku da wayau, domin kuwa saina addabi rayuwarku, inyaso ku kashe ni, kai bazan ma mutu ba bi'iznillahi har sai na ga bayan ku..." Bata kai ƙarshen maganar ba, Danish Ya sake damƙota, kamar ƴar dambe sai harba ƙafarta take yi, ahaka yaja ta har zuwa saman gadonta, Ya jefar da ita, Kafin ya juya ya kalli Sauran yace dasu su je su ci abinci," da sauri suka nufi kayan abincin nasu kowa ya zauna banda Gabriel da Unaiza, kalaman angel sun yi matuƙar ɗaga musu hankali, tunani suke yi wacece batul? Meyasa aka ɗauke ta?
A gefen gadon Angel Danish ya zauna yana gadinta, gudun kada ta ƙara zuwa ta 6allo musu aiki, Shi kaɗai yasan me yae mata, da har tagaza ɗagowa, hawaye sai bin fuskarta suke yi, ta ɗaura kanta saman pillow,
Bayan sun kammala cin abinci sauran da suka rage ma waɗanda basu samun damar xuwa suci ba, acikin kwando suka adana mu su nasu, Giants na fita daga Cikin dakin, Gabriel ya soma tambayarsu wacece batul? su azeeza suka bashi amsa da cewa ƴar uwarsu da aka ɗauka, yaso ya ƙara tambayarsu dalilin dayasa aka ɗauke ta amma Danish Ya hana shi, ta hanyar
Ƙura mishi ido yana kallon shi, nan take yaji maganar ta fita aranshi, bai ƙara tada ta ba.
Yinin ranar babu daÉ—i suka yi shi, Saboda halin da suka shiga na tunawa da Æ´ar uwarsu, Kowa jikin shi yae sanyi, Har marece ya yi babu wanda ya motsa acikin su, majnun ne kaÉ—ai yake ta tsalle tsalle shi kaÉ—ai atsakiyar É—akin su.
Lokacin da marece ya nutsa, Gabriel ya bukaci yin wanka, Saukowa Yae daga saman gadon shi, Ya nufi toilet ɗinsu Ya shiga, bayan yasanya jamlock ya datse ƙopar Ya dan jingina bayanshi Jikin ƙopar, yayin da zuciyarshi ke acunkushe da tunanin abubuwan da suka faru ayau, Tabbas ya razana sosai da gidan kurkukun nan, duk da baisan komai adangane dashi ba amma yana ji aranshi cewa wani abu yana faruwa badai badai ba, Shi bakomai yafi jimawa ba face ƴar uwar shi Gabriella, maganganun da angel tayi ɗazu akan tasu ƴar uwar sun tsara mishi aranshi.
A ƙalla ya ɗauki kusan minti talatin Yana tunani acikin toilet ɗin ba tare daya ta 6uka komai ba, Sai daga bisani ne ya soma ƙoƙarin cire rigarshi, Kwatsam idanuwanshi suka sauka akan Glass window ɗin nan, A wani slow yake kallonta sai yake ganin kamar glass ɗin jikinta bai zauna dakyau ba, nan take ranshi ya bashi cewar Yaje ya duba ya gani, wata'kil ma ya samu hanyar shiga Cikin kurkukun ko dan yaje ya ɗauko ƴar uwarshi, ba tare da yayi shawara da zuciyarshi ba, Ya fasa cire rigar ya nufi tagar, Yakai hannu ya tatta6a jikin glass ɗin Yaji yana girgiɗi, ya daddage ya zame shi daga jikin tagar ya sauke shi ƙasa, wani irin farin ciki ne ya mamaye zuciyarci, bakomai yake hange ba face fuskar sister ɗinshi.
Rashin sani yafi dare duhu, cike da ƙwarin gwiwa Gabriel ya dura tagar ya faɗo ta cikin wannan hanyar da angel ta tsinci kanta lokacin da ta ta6a durawa, hada saurin shi wurin miƙar hanyar, babu wadataccen haske, amma yana iya gani dakyau, yana kaiwa ƙarshenta, Ya faɗo cikin wannan babban filin mai ɗauke da dogayen benayen nan, A hankali yake ƙarewa ginin kallo, bai ta6a ganin wuri mai matuƙar ruɗarwa ba irin wannan wurin, hakanan ya dinga jin faɗuwar gaba, tun daga kan hauwa na farko har zuwa na biyu, a ƙarshe ya tsayar da idanuwanshi kan hawa na uku, ba zato ba tsammani idanuwanshi suka hango mashi kyakkyawar matashiyar budurwa tana gudun ceton rai saman hawa na uku, fara fat kamar fatalwa, Jikinta sanye da riga ja, wadda bata kai gwiwarta ba, fararen cinyoyinta santala santala, daga gani babu hankali atattare da ita, tana gudu tana waiwayon bayanta, ga uban gashin kanta dake yarfowa harta saman idanuwanta, hakan yasa ta dinga faɗuwa ƙasa tana miƙewa saboda bata ganin gabanta dakyau, wani irin tsorone ya ziyarci zuciyar Gabriel, Ganin tana saukowa daga saman benan mai hawa talatin, Girgiza kanshi ya dinga yi, zufa tako ina saman fuskarshi, Ya rasa gane shin mutunce ita ko aljan, ko kuma fatalwa ce, Idanuwanshi ne suka dinga nuna mashi kamar sister ɗinshi ce, sai dai akwai banbanci sosai, Ƴar uwarshi ba fara bace, kuma bata da tsayin sumar kai da yawa irin na wannan yarinyar, ' A tsorace ya juya zai koma hanyar daya fito, A lokacin harta ƙarasa saukowa saman benan, sai miƙa mishi hannu ta ke Yi, tana magana sautin muryarta sam baya fita, ranshi ne ya bashi cewar Ya juya ya kalle ta, ya ɗan dakata ya waiwayo baya yana kallonta, sai jan ƙafarta take yi, saboda nauyin da tayi mata, Taya zai iya yarda cewa mutunce ita? Bai gama yanke shawara da zuciyarshi ba, yaga ta faɗi ƙasa kanta ya bugu, ' Gaba ɗaya sumar kanta ta rufe mata fuskarta, Tsananin tausayinta ne ya kama gabriel, koma dai aljana ce wannan ba ƙaramin jiki taji ba, sai motsi take yi alamar tana son ɗagowa da kanta amma ta kasa, kuma duk da tana kwance ƙasa hakan baisa ta fasa miƙa mishi hannunta ba, yayi niyar yaje wurinta amma sai yaga Benayen dake awurin sun soma motsi suna yin sama da ƙasa, Ya zazaro ido ganin suna tunkaro shi, aiko da gudu ya juya ya bi ta hanyar daya fito Ko waiwaye babu ya koma bakin tagar nan, Allah ne ya taimake shi bai 6ace hanyar ba, Jiki na kerma ya haura tagar Ya dura Cikin toilet ɗinsu Yana ta haki, Sai da ya samu natsuwa tukunna yakai hannu ya ɗauki glass ɗin daya jingine jikin bango ya maida shi jikin tagar kamar yadda ya ganshi,
Kamar amafarki yake tariyo abubuwan da suka faru Cikin ƙanƙanin lokaci, zuciyarshi cike fal da tunanin matashiyar yarinyar nan daya gani .............."!
💋PRISONERS💋
Ya jima tsaye jikin tagar ba tare daya motsa ba, zuciyarshi na raya mashi akan ya koma ya taimake ta, sai dai tsoro ya hana shi yin hakan, Ajiyar zuciya ya sauke tare nufar cikin toilet ɗin, wankan ma da ya shigo da niyar yi ya fasa, ƙopa kawai ya buɗe ya fito ya shiga ɗakin su.
A zazzaune ya same su saman gadajen su, angel ce kaɗai kwance saman nata gadon da alama bacci ya ɗauke ta, tunda Gabriel ya shigo idanuwanshi na akan kowannan su, damuwace danƙare akan fuskokinsu, In ka cire mutun uku, Majnun da jamima da ke ta yin rawa tsakiyar ɗakin su, yau ta biye mishi suna wasa a tare, duk da a shekaru Majnun ya girmi Jamimah.
bayan su sai Sarah dake yanke akaifar hannunta da nail cutter ɗinsu, tana zaune saman shimfidarta dake a ƙasan gado, don ita tuni ta yafe hawa gado, komai nata a ƙasa take zama ta yi shi, Hankalin ta kwance babu damuwa akan fuskarta, Danish yana daga kishingiɗe saman bed ɗinsa, ya ɗan lumshe eyes ɗinta, sam babu walwala akan fuskar shi, Azeeza tana zaune saman gadon parveen, ta ɗaura kanta saman shoulder dinta, magana su ke yi ƙasa ƙasa a takaninsu, haris da deeja suna fuskantar juna, sun nutsa cikin tattaunarsu duk dai akan Batul ne, idan muka koma 6angaren su Hanna ita da hibba da Yasmin da eve da rubina kowaccensu na kwance saman gadonta, sun yi likimo kamar masu yin bacci, Zuciya ce ba daɗi, dole jiki yai sanyi, yar gida daddy kuwa bacci ta ke yi sai dai ga dukkan alamu babu lafiya ajikinta, kamar zata faɗo daga saman gadonta, a cikin bacci take murza cikinta da hannunta na dama, idanuwanta sun kumbura, ga sahun marin da Danish yai mata gefen fuskarta kamar jini ya kwanta.