Sashe 153
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
"dagaske mutunce kwance saman gadon batul É—in mu"! Jin wannan maganar da Parveen ta yi ne yasa Angel ware idanuwanta, ta sanya hannu tare da janye su Azeeza daga Jikinta.
Ta yunƙura ta miƙe jikinta na rawa ta nufi gadon Itama Deeja tabi bayanta, Ya rage saura azeeza da jamimah, sun fi kowa tsorata, rungume juna su ka yi kamar zasu haɗe jikinsu ya zama ɗaya.
A kewaye da gadon suka tsaitsaya curko curko, suna ƙare mata kallo, farat ɗaya Angel ta gane wacece muryarta na rawa ta ambaci sunanta da ƙarfi
* "BATOOL!" *
Ras! Gaban kowan nan su Ya faɗi, a ruɗe su ke kallonta, Basu tabbatar cewa ita bace, har sai da Angel ta hau saman gadon, Jiki na rawa ta sanya hannayenta biyu ta yaye sumar kanta gefe ɗaya, kyakkyawar fuskar batul ta bayyana, zazzare idanuwansu waje su ka yi, abun ne da basu tsammace shi ba, ba zaka iya tantance yanayin da su ke a ciki ba, suna so su yi farin ciki sai dai suna fargabar ace batul ɗinsu wani abu ya same ta, tun daga kan fuskarta su ka shaida hakan, kamar an ninka hasken fatarta, dama fara ce sol kamar Angel ko tabo babu a jikinta, hatta gwiwar ƙafarta jawur ta ke, ta canza masu sosai ta rame kamar an ɗibi naman jikinta, brownish lips ɗinta sun ciza sun bushe ƙamas, hankalinta a kwance ta ke fitar da numfashi sai dai kamar a firgice ta ke.
Halin da suka shiga furta shi 6ata baki ne, Zuciyoyin su sun karaya, Jiki yayi la'asar, Idanuwan kowannansu hawaye ne kwance a cikin su.
Muryar Angel cikin shessheƙar kuka ta furta"Ya Allah kasa ba mafarki na ke yi ba, Batul ɗina ce ta koma haka? Waye ya dawo mana da ita? Ta ina ta shigo? Dama dagaske ne abunda Gabriel ya faɗa min na cewa yaga matashiyar yarinya tana gudu asaman third floor! Batul ɗina ce kenan! ' Zuciyarta a hautsine ta yi maganar, ita kanta batasan ta furta hakan ba. yayin da idanuwanta ke akan jikin batul.
Hawaye ne masu ɗumi suka wanke fuskarta, ta ɗaura hannayenta biyu saman kafaɗunta, ta ɗago da ita, tare da kwantar da ita saman ƙirjinta, nan take taji wani irin yanayi mara misaltuwa ya ratsa jikinta, hakan ya ƙara tabbatar mata da cewa Batul ɗinta ce babu tantama, cikin rauni na murya ta shiga faɗin"wlh itace! Batul ɗin mu ce aka dawo mana da ita, tsawon wata uku, till today ashe da rabon zamu sake yin tozali da ƴar uwar mu! Alhamdulillah ya Allah bazan iya misalta farin cikin da nake a ciki ba........" Sosai ta fashe da matsanancin ku ka tamkar ranta zai fita, suma sauran ƴan uwan nasu suka kama yin kukan farin ciki.
A gefe da gefen gadonta kowannan su Ya zauna, wasu ma saman gadon suka haye, kamar sun samu tv suna kuka suna kallon ƴar uwarsu dake a kwance jikin Angel, don tunda ta ƙanƙameta bata saketa ba, sosai ta yi tighting ɗinta a jikinta kamar zata mayar da ita cikin cikinta, Allah sarki tsohuwar zuma, Gaba ɗaya sautin shesshekar kukansu Ya karaɗe cikin ɗakin, bakomai yasa su yin kukan nan ba face tsabar farin cikin da su ke aciki, sai dai duk da hakan akwai fargaba acan ƙasan zuciyoyin su, saboda ba su san me aka yi mata ba, na tsawon lokacin da ta ɗauka a hannun su.
suna matuƙar jin fargabar abunda zasu ji daga gare ta, wani abu da ya ƙara tada masu hankali, Taƙi farkawa, duk wannan koke koken da su ke yi baisa ta buɗe idanuwanta ba, Azeeza dake rungume da jamimah tun da taji muryar Angel tana ambaton sunan Batul, tabi ta ruɗe ta shiga laluban hanyar da zata kai ta gare su, sai dai takasa, sai rarrafe ta ke yi a tsakiyar ɗakin tana ambaton sunan batul.
Jamimah ce ta taso itama tuni ta daina yin kukan jin cewa ƴar uwar su ce ba Aljanna, sai taji hankalin ta ya kwanta, tafiya tayi zuwa inda azeeza ta ke a zuƙunne ta ruƙo hannunta ta miƙar da ita, tare da yi mata jagora zuwa gaban gadon batul inda su Angel su ke a zazzaune, da taimakon Hannah ta samu ta haye gadon bayan sun matsa mata hanya, muryarta da zumuɗin ta ke faɗin ina batul ɗin ta ke ne? Dagaske itace aka dawo musu da ita?
fuskarta sharkaf da hawaye ta ke yi masu tambayar.
Makanta ba ta yi ba, idanuwanta akansu Angel saidai bata iya ganin su, ganin yadda take ta sharar ƙwalla tana ambaton sunan batul, Yasa deeja ta ruƙo hannunta ta ɗaura shi saman sumar kan batul data cika bayanta.
shafa gashin ta dinga yi da hannunta, muryar hanna a sanyaye tace mata"azeeza bacci ta ke yi, bata farka ba, tana rungume ne a jikin Angel ne" koda hanna ta yi mata magana, bata haƙura da laluban jikinta ba, har saida ta ɗaura hancinta a saman bayan batul, ta tabbatar da cewa ita ɗinta ce, tukunna hankalinta ya kwanta, farin ciki ya cika zuciyarta, sai zabga murmushi ta ke yi, Angel fa taƙi basu damar su rungumi ƴar uwarsu, tunda ta ƙanƙameta a jikinta taƙi sakinta, yadda kasan uwa da ƴarta, hannayenta biyu daddafe da bayanta, ko lokacin da azeeza take shasshafa sumar kan batul duk tana ji, sai dai bata motsa ba, gani take kamar in ta saketa za'a ƙara rabata da ita ne, Angel na matuƙar ƙaunar batul, fiye da tunanin mai tunani, irin ƙaunar da ta ke yi mata bata da banbanci data uwa da ɗanta, ji take kamar ciki ɗaya suka fito da batul.
Sarah da ke a tsaye tun ɗazu tana kallonsu, bata furta komai ba, sai dai da alama itama ta tayasu kukan don hada hawaye kan fuskarta, bakomai ne ya ta6a zuciyarta ba, face yarda taga sunata kuka, da kuma yarda Angel ta ƙanƙame ƴar uwar ta su a jikinta, hakan ya tabbatar mata da irin son da su ke yi mata, duk da batasan wacece batul ba, amma tana yawan jin suna ambaton sunanta, ta shaida irin ƙaunar da suke yi mata, ba ƙaramin burgeta su ka yi ba.
"Angel har yanzu bata farka ba? Ya za'ae muna so musan awani hali take ciki, A ƙagare muke da mu rungumi ƴar uwar mu, muji ɗuminta a jikin mu, tsawon lokaci bama a tare" Deeja ce tai magnar, fuskarta a yamutse don hankalinta ba'a kwance yake ba.
Dare ya koma masu tamkar da rana, babu mai jin bacci a cikin su, dama sun sha bacci yau.
"Bari na ɗebo ruwa a yayyafa mata ko mun samu ta farka" acewar rubina, kafin tayi yunƙurin mikewa Yasmin ta dakatar da ita ta hanyar yi mata magana"ai ba suma tayi ba, bacci ta ke yi, bana so mu takura mata, tunda tana nunfashi mu jira har zuwa time da zata farka"! Fasa zuwa ɗebo ruwan rubina tayi,
Cikin sanyin murya parveen tace"Allah yasa kada ta farka tana jin yunwa, wlh da ace mun san yau za'a dawo mana da ita, ai da mun ajiye mata abinci dayawa," ta yi maganar tana matse ƙwallar idonta, ɗakin yai tsit masu yin shessheƙar kukan duk sun dakata.
Sun yi zugudum kamar masu zaman makoki, kowa da abunda yake saƙawa a cikin ranshi dangane da tsintar batul da su ka yi a cikin su, Damuwace ƙarara akan fuskokinsu, fatansu Allah yasa ba acutar masu da ita ba, duba da irin baccin da take yi mai nauyin gaske, deeja ce tai tunanin yi magana akan suje su kwanta.
"Yakamata kuje ku kwanta ku yi bacci, dare ne sosai, nasan kafin gobe da safe in sha Allah zata farka......" tun kan ta kai ƙarshen maganar, su ka haɗa baki wurin cewa"ai bazamu iya runtsawa ba, idan har ƴar uwar mu bata farka ba, kusan wata uku bamu atare da ita, till today aka dawo mana da ita, Ta yaya kike tunanin zamu iya yin bacci? Ba tare da mun gana da juna ba"
Ita kanta Deeja ta yi masu maganar ne kawai, don tasan ba kwanciyar za su yi ba, duk wannan maganganun da suke yi Angel bata fahimtar su, domin kuwa hankalinta na akan batul ɗinta, dake kwance saman ƙirjinta, ta natsu tana sauraron bugun zuciyarta, sai faman lumshe idanuwanta ta ke yi, waɗanda suka canza launi saboda kukan da tasha, har yanzu hawayen basu daina gangarowa ta cikin idanuwanta ba.
"pls Angel ki kwantar mana da ita, yadda zamu samu damar ganin fuskarta da kyau, munyi kewarta sosai" Acewar eve, shiru Angel bata motsa ba, babu alamun zata kwantar da ita, hannu Deeja ta kai saman bayan Angel ta É—an bubbugata don ta dawo hayyacinta.
"Angel muna son ganin fuskarta, ki kwantar mana da ita" deeja ce tai maganar, still bata tanka masu ba.
"Ko dai ta yi bacci ne"? Hibba ce tai tambayar, Sarah dake a tsaye ta matso kusa da gadon, ta sanya hannayenta biyu da niyar ta raba jikin batul daga na Angel, amma ta kasa, Lamarin ya ɗaure masu kai, suka dinga kiran sunanta taƙi amsa masu, kuma ba bacci ta ke yi ba.
Parveen da Deeja ne suka haɗa hannu wurin ƙoƙarin 6an6are batul daga jikinta, abun ya ɗaure masu kai, yadda taƙi sakinta, kamar su fashe da kuka saboda yadda suka ƙagara da son ganin fuskarta.
"Bani na ruƙe ta ba, itace ta ruƙe ni"
Muryar Angel ce ta yi masu magana, abunda basu sani ba, tun lokacin da Angel ta rungumo batul a jikinta ta farka daga baccin, koda taji jikin ƴar uwarta ne, ta ƙanƙameta sosai, hannayen batul na abayan Angel ta zagayo da su, sumar kan Angel ce ta rufe su shiyasa basu lura da cewar itace ta matse ta a jikinta ba, tun da farko da su ka buƙaci ganin fuskarta, Angel tai ƙoƙarin sakinta, sai dai ita batul ɗin taƙi bari ta raba jikinta daga nata, that mean batul ta farka daga bacci tuntuni.
Sun yi mamakin jin abunda Angel tace masu, na cewa itace ta ruƙeta, muryar Deeja a sanyaye tace"Batul, idan kina jin mu ki juyo ki fuskance mu, mu ma minyi missing ɗin ki sosai, muna buƙatar mu yi hugging ɗin ki a jikin mu......."
Ta yunƙura ta miƙe jikinta na rawa ta nufi gadon Itama Deeja tabi bayanta, Ya rage saura azeeza da jamimah, sun fi kowa tsorata, rungume juna su ka yi kamar zasu haɗe jikinsu ya zama ɗaya.
A kewaye da gadon suka tsaitsaya curko curko, suna ƙare mata kallo, farat ɗaya Angel ta gane wacece muryarta na rawa ta ambaci sunanta da ƙarfi
* "BATOOL!" *
Ras! Gaban kowan nan su Ya faɗi, a ruɗe su ke kallonta, Basu tabbatar cewa ita bace, har sai da Angel ta hau saman gadon, Jiki na rawa ta sanya hannayenta biyu ta yaye sumar kanta gefe ɗaya, kyakkyawar fuskar batul ta bayyana, zazzare idanuwansu waje su ka yi, abun ne da basu tsammace shi ba, ba zaka iya tantance yanayin da su ke a ciki ba, suna so su yi farin ciki sai dai suna fargabar ace batul ɗinsu wani abu ya same ta, tun daga kan fuskarta su ka shaida hakan, kamar an ninka hasken fatarta, dama fara ce sol kamar Angel ko tabo babu a jikinta, hatta gwiwar ƙafarta jawur ta ke, ta canza masu sosai ta rame kamar an ɗibi naman jikinta, brownish lips ɗinta sun ciza sun bushe ƙamas, hankalinta a kwance ta ke fitar da numfashi sai dai kamar a firgice ta ke.
Halin da suka shiga furta shi 6ata baki ne, Zuciyoyin su sun karaya, Jiki yayi la'asar, Idanuwan kowannansu hawaye ne kwance a cikin su.
Muryar Angel cikin shessheƙar kuka ta furta"Ya Allah kasa ba mafarki na ke yi ba, Batul ɗina ce ta koma haka? Waye ya dawo mana da ita? Ta ina ta shigo? Dama dagaske ne abunda Gabriel ya faɗa min na cewa yaga matashiyar yarinya tana gudu asaman third floor! Batul ɗina ce kenan! ' Zuciyarta a hautsine ta yi maganar, ita kanta batasan ta furta hakan ba. yayin da idanuwanta ke akan jikin batul.
Hawaye ne masu ɗumi suka wanke fuskarta, ta ɗaura hannayenta biyu saman kafaɗunta, ta ɗago da ita, tare da kwantar da ita saman ƙirjinta, nan take taji wani irin yanayi mara misaltuwa ya ratsa jikinta, hakan ya ƙara tabbatar mata da cewa Batul ɗinta ce babu tantama, cikin rauni na murya ta shiga faɗin"wlh itace! Batul ɗin mu ce aka dawo mana da ita, tsawon wata uku, till today ashe da rabon zamu sake yin tozali da ƴar uwar mu! Alhamdulillah ya Allah bazan iya misalta farin cikin da nake a ciki ba........" Sosai ta fashe da matsanancin ku ka tamkar ranta zai fita, suma sauran ƴan uwan nasu suka kama yin kukan farin ciki.
A gefe da gefen gadonta kowannan su Ya zauna, wasu ma saman gadon suka haye, kamar sun samu tv suna kuka suna kallon ƴar uwarsu dake a kwance jikin Angel, don tunda ta ƙanƙameta bata saketa ba, sosai ta yi tighting ɗinta a jikinta kamar zata mayar da ita cikin cikinta, Allah sarki tsohuwar zuma, Gaba ɗaya sautin shesshekar kukansu Ya karaɗe cikin ɗakin, bakomai yasa su yin kukan nan ba face tsabar farin cikin da su ke aciki, sai dai duk da hakan akwai fargaba acan ƙasan zuciyoyin su, saboda ba su san me aka yi mata ba, na tsawon lokacin da ta ɗauka a hannun su.
suna matuƙar jin fargabar abunda zasu ji daga gare ta, wani abu da ya ƙara tada masu hankali, Taƙi farkawa, duk wannan koke koken da su ke yi baisa ta buɗe idanuwanta ba, Azeeza dake rungume da jamimah tun da taji muryar Angel tana ambaton sunan Batul, tabi ta ruɗe ta shiga laluban hanyar da zata kai ta gare su, sai dai takasa, sai rarrafe ta ke yi a tsakiyar ɗakin tana ambaton sunan batul.
Jamimah ce ta taso itama tuni ta daina yin kukan jin cewa ƴar uwar su ce ba Aljanna, sai taji hankalin ta ya kwanta, tafiya tayi zuwa inda azeeza ta ke a zuƙunne ta ruƙo hannunta ta miƙar da ita, tare da yi mata jagora zuwa gaban gadon batul inda su Angel su ke a zazzaune, da taimakon Hannah ta samu ta haye gadon bayan sun matsa mata hanya, muryarta da zumuɗin ta ke faɗin ina batul ɗin ta ke ne? Dagaske itace aka dawo musu da ita?
fuskarta sharkaf da hawaye ta ke yi masu tambayar.
Makanta ba ta yi ba, idanuwanta akansu Angel saidai bata iya ganin su, ganin yadda take ta sharar ƙwalla tana ambaton sunan batul, Yasa deeja ta ruƙo hannunta ta ɗaura shi saman sumar kan batul data cika bayanta.
shafa gashin ta dinga yi da hannunta, muryar hanna a sanyaye tace mata"azeeza bacci ta ke yi, bata farka ba, tana rungume ne a jikin Angel ne" koda hanna ta yi mata magana, bata haƙura da laluban jikinta ba, har saida ta ɗaura hancinta a saman bayan batul, ta tabbatar da cewa ita ɗinta ce, tukunna hankalinta ya kwanta, farin ciki ya cika zuciyarta, sai zabga murmushi ta ke yi, Angel fa taƙi basu damar su rungumi ƴar uwarsu, tunda ta ƙanƙameta a jikinta taƙi sakinta, yadda kasan uwa da ƴarta, hannayenta biyu daddafe da bayanta, ko lokacin da azeeza take shasshafa sumar kan batul duk tana ji, sai dai bata motsa ba, gani take kamar in ta saketa za'a ƙara rabata da ita ne, Angel na matuƙar ƙaunar batul, fiye da tunanin mai tunani, irin ƙaunar da ta ke yi mata bata da banbanci data uwa da ɗanta, ji take kamar ciki ɗaya suka fito da batul.
Sarah da ke a tsaye tun ɗazu tana kallonsu, bata furta komai ba, sai dai da alama itama ta tayasu kukan don hada hawaye kan fuskarta, bakomai ne ya ta6a zuciyarta ba, face yarda taga sunata kuka, da kuma yarda Angel ta ƙanƙame ƴar uwar ta su a jikinta, hakan ya tabbatar mata da irin son da su ke yi mata, duk da batasan wacece batul ba, amma tana yawan jin suna ambaton sunanta, ta shaida irin ƙaunar da suke yi mata, ba ƙaramin burgeta su ka yi ba.
"Angel har yanzu bata farka ba? Ya za'ae muna so musan awani hali take ciki, A ƙagare muke da mu rungumi ƴar uwar mu, muji ɗuminta a jikin mu, tsawon lokaci bama a tare" Deeja ce tai magnar, fuskarta a yamutse don hankalinta ba'a kwance yake ba.
Dare ya koma masu tamkar da rana, babu mai jin bacci a cikin su, dama sun sha bacci yau.
"Bari na ɗebo ruwa a yayyafa mata ko mun samu ta farka" acewar rubina, kafin tayi yunƙurin mikewa Yasmin ta dakatar da ita ta hanyar yi mata magana"ai ba suma tayi ba, bacci ta ke yi, bana so mu takura mata, tunda tana nunfashi mu jira har zuwa time da zata farka"! Fasa zuwa ɗebo ruwan rubina tayi,
Cikin sanyin murya parveen tace"Allah yasa kada ta farka tana jin yunwa, wlh da ace mun san yau za'a dawo mana da ita, ai da mun ajiye mata abinci dayawa," ta yi maganar tana matse ƙwallar idonta, ɗakin yai tsit masu yin shessheƙar kukan duk sun dakata.
Sun yi zugudum kamar masu zaman makoki, kowa da abunda yake saƙawa a cikin ranshi dangane da tsintar batul da su ka yi a cikin su, Damuwace ƙarara akan fuskokinsu, fatansu Allah yasa ba acutar masu da ita ba, duba da irin baccin da take yi mai nauyin gaske, deeja ce tai tunanin yi magana akan suje su kwanta.
"Yakamata kuje ku kwanta ku yi bacci, dare ne sosai, nasan kafin gobe da safe in sha Allah zata farka......" tun kan ta kai ƙarshen maganar, su ka haɗa baki wurin cewa"ai bazamu iya runtsawa ba, idan har ƴar uwar mu bata farka ba, kusan wata uku bamu atare da ita, till today aka dawo mana da ita, Ta yaya kike tunanin zamu iya yin bacci? Ba tare da mun gana da juna ba"
Ita kanta Deeja ta yi masu maganar ne kawai, don tasan ba kwanciyar za su yi ba, duk wannan maganganun da suke yi Angel bata fahimtar su, domin kuwa hankalinta na akan batul ɗinta, dake kwance saman ƙirjinta, ta natsu tana sauraron bugun zuciyarta, sai faman lumshe idanuwanta ta ke yi, waɗanda suka canza launi saboda kukan da tasha, har yanzu hawayen basu daina gangarowa ta cikin idanuwanta ba.
"pls Angel ki kwantar mana da ita, yadda zamu samu damar ganin fuskarta da kyau, munyi kewarta sosai" Acewar eve, shiru Angel bata motsa ba, babu alamun zata kwantar da ita, hannu Deeja ta kai saman bayan Angel ta É—an bubbugata don ta dawo hayyacinta.
"Angel muna son ganin fuskarta, ki kwantar mana da ita" deeja ce tai maganar, still bata tanka masu ba.
"Ko dai ta yi bacci ne"? Hibba ce tai tambayar, Sarah dake a tsaye ta matso kusa da gadon, ta sanya hannayenta biyu da niyar ta raba jikin batul daga na Angel, amma ta kasa, Lamarin ya ɗaure masu kai, suka dinga kiran sunanta taƙi amsa masu, kuma ba bacci ta ke yi ba.
Parveen da Deeja ne suka haɗa hannu wurin ƙoƙarin 6an6are batul daga jikinta, abun ya ɗaure masu kai, yadda taƙi sakinta, kamar su fashe da kuka saboda yadda suka ƙagara da son ganin fuskarta.
"Bani na ruƙe ta ba, itace ta ruƙe ni"
Muryar Angel ce ta yi masu magana, abunda basu sani ba, tun lokacin da Angel ta rungumo batul a jikinta ta farka daga baccin, koda taji jikin ƴar uwarta ne, ta ƙanƙameta sosai, hannayen batul na abayan Angel ta zagayo da su, sumar kan Angel ce ta rufe su shiyasa basu lura da cewar itace ta matse ta a jikinta ba, tun da farko da su ka buƙaci ganin fuskarta, Angel tai ƙoƙarin sakinta, sai dai ita batul ɗin taƙi bari ta raba jikinta daga nata, that mean batul ta farka daga bacci tuntuni.
Sun yi mamakin jin abunda Angel tace masu, na cewa itace ta ruƙeta, muryar Deeja a sanyaye tace"Batul, idan kina jin mu ki juyo ki fuskance mu, mu ma minyi missing ɗin ki sosai, muna buƙatar mu yi hugging ɗin ki a jikin mu......."