← Book details Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 159 OF 179

Sashe 159

Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Angel na kwaɗaitu da son yin irin rayuwarki, labarin ki da kika bani ya fahimtar dani game da cin zalun da iyaye na su ka yi min, ashe duk Soyayyar da su ke nuna min ƙiyayya ce ba ƙauna ta su ke yi ba, nayi asarar rayuwata, gashi yanzu komai ya qare min, lokaci ya qure min da zan iya......" bata kai ga ƙarasa maganar ba, Angel ta yi saurin sanya tafin hannunta wurin toshe mata baki, Jikinta wani irin zafi na fitar hayyaci, idanuwan su cikin na juna, hawaye na bin fuskokin su,

"Lokaci bai ƙure maki ba Unaiza! Tunda har kina numfashi to kina da sauran damar da zaki iya gyara rayuwar ki, inaso ki bamu dama ni da ƴan uwana mu nuna maki tsantsar soyayya, mu baki kulawa ta musamman har kiji sauƙi, nayi maki alƙawarin zan taimaka maki wurin gyara rayuwarki in sha Allah, saboda inaso ki rayu kodan saboda ki yi tozali da idon mugun mahaifinki, ki maida mashi martani sannan ki fille mashi kai da adda,"

Cikin ƙunar rai Unaiza ta furta "Bazaki fahimce ni bane, komai ya qare min, bazan iya rayuwa ba, Nifa matatta ce, maganar da nake yi maki a yanzu ji nake kamar an bani umarni ne in sanar dake kafin rai na ya fita daga jikina,......." numfashi taja, idanuwanta sun ciza launinsu, Baiwar Allah ita kaɗai tasan raɗaɗin azabar da take ji, Ga ciwon jiki ga ciwon zuciyar da mahaifinta ya dasa manta, hakika ya karya mata zuciya.

"Bayan an ɗauke ni daga cikin ku, bana acikin hayyacina, amma zan iya tuna abubuwan da suka faru, Angel naga tashin hankalin da ban ta6a gani ba a rayuwata, na shiga firgici da tsoro kamar zan haɗiyi zuciya in mutu, mutun shidda akaina ba ƙananun mutane ba, kuma ba su kasance a suffar mutane ba, sai da su ka rikiɗa suka koma wata irin mummunar halitta tukunna suka soma yin sex dani, nayi kukan nayi ihun babu mai jina, har a bakina saida suka zuba min sperm ɗinsu mai ƙarni da zafi......" a gigice Angel ta ke kallonta Zuciyarta ta soma tashi...unaiza bata dakata ba taci gaba da cewa tun ina haɗiyewa ta ƙarfi har ya cika min bakina na fita hayyacina, Angel tsawon kwanaki shidda da nake cikin yin menstruation amfani aka dinga yi dani, sun rabani da abun da nake alfahari dashi,

Ta yi maganar tare da sanya hannayenta biyu da niyar ta ɗaga mata rigar ta gani, da sauri Angel ta damƙi hannayenta, tana kuka tace"ba sai kin nuna min ba unaiza wlh na yarda da maganar ki, ashe dama abun da suke yi mana kenan, na jima da zargin hakan ban tabbatar ba sai yanzu da kika faɗamin........"

"Angel bani da isasshen lokaci, inaso nabar maki wasiya ki kaima daddyna idan har Allah ya ba ku damar fita daga cikin kurkuku........"

Girgiza kai Angel ta yi a yayin da zuciyarta ke tafarfasa tace "a'a unaiza dan Allah ki daina faÉ—in zaki rubuta min wasiyya, gani nake kamar mutuwa za ki yi, Wlh bana so ki mutu ba tare da kin É—auki fansar abinda mahaifinki yayi maki ba,"

murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, muryarta asanyaye tace "Ɗaukar fansa ba dole saini zanyi ta ba, tun da ina dake bani da damuwa, Unaisa da Unaiza kusan abu ɗaya ne banbancin kaɗan ne na rayuwar mu, kinyi dacen uba wanda ya tsaya maki tsakani da Allah, don ki nemi duniyarki da lahirarki, Yayin da ni kuma nayi rashin dacen uba, ko ince iyaye, sun tauye min haƙƙina, Angel inaso ki yi min alƙawarin cewa Zaki ɗaukar min fansa! Inaso kiyi amfani da hannayen ki wurin sare kan mahaifina da gatari bayan ya kammala karanta wasiƙar da zan rubuta maki......." rurruƙe hannayenta Angel tayi acikin nata "ni bani zan ɗaukar maki fansa ba, ke zaki ɗauki fansa da hannayen ki, inaso ya ganki a matsayin musulma da ranki da lafiyarki, Ki fayyace mashi duk irin zaluncin da yayi maki, ki tofa mashi yawu akan fuskar shi kafin ki sare kanshi da gatari" sosai Unaiza ta fashe da kuka tana faɗin "ba zaki fahimce ni ba, Nifa matattace a yanzu haka, nayi fatan ace zan iya yin yadda kika fadamin sai dai ba zan iya ba Angel, shiyasa na rataya nauyin yin hakan akan wuyanki, ke nakeso ki kashe min shi da hannayenki tare da mahaifiyata, Angel koda ace sun ganni ba zasu damu ba saboda dabbobine su, babu zuciya a ƙirjinsu, sufa ne suka haifeni suka raine ni cikin so da ƙauna, amma hakan baisa sun ƙaunace ni ba, tayaya kike tunanin zasu ji zafi idan su ka yi tozali dani...'?

ta jefa mata tambayar, Kafin ta cigaba da yi mata magiya akan ta É—auko mata Jotter da biro don ta rubuta mata wasiyya.

Jiki ba ƙwari Angel ta miƙe, tana tafiya ta nufi ƙopa ta buɗe ta fita tana jiyo shessheƙar kukan Unaiza ta cikin toilet, ji ta ke kamar in tayi nesa da ita zata dawo ne ta taras da gawarta, Lokacin da ta shiga Cikin ɗakin su, A kewaye da gadon Majnoon ta taras dasu Hanna, Yana kwance sun lullu6e shi tare da jamimah, da alama bacci ya ɗauke shi,

Jin motsin tafiyar ta ne yasa duk suka ɗago da idanuwan su zuwa ga dubanta damuwace ƙarara akan fuskokin su, tasan dole su jiyo shessheƙar kukan unaiza, da sauri su Deeja suka tunkareta tare da batul da sauran ƴan uwan nasu, suna tambayar ta lafiya mai ya faru da unaiza......."

Muryarta a disashe ta ce masu "Ku je ku duba jikinta, ku lallashe ta yanzu zan dawo" Da gudu suka nufi sashen toilet ɗin, mutun biyu ya rage Azeeza sai jamimah dake rungume da majnoon, kallonsu Angel tayi na ɗan wani lokaci kafin ta nufi table ɗin ɗakin su, inda unaiza ta ɗaura backpack ɗinta tun da jimawa, ta sanya hannu ta zuge zip ɗin jakar tare da ciro jotter da biro da sauri ta juyo ta nufi toilet ɗin, tunkan ta ƙarasa ta soma juyo sautin muryoyin su Deeja suna ta lallashinta, tana ƙarasa shiga ciki ta same su Zuƙunne agaban Unaiza da ke a rungume saman ƙirjin batul, ta ɗaura hannayenta saman sumar kanta tana shafata cikin sigar lallashi,

"Angel bata da lafiya, Jikinta zafi sosai yakamata musan abun yi tun kan ciwon yaci ƙarfinta" deeja ce tai maganar, jin ta ambaci sunan Angel yasa Unaiza ɗagowa da kanta, tana kallonta, Miƙa mata jotter ɗin tayi da biro, bayan ta kar6a ta ɗaurata saman laps ɗinta yatsun hannunta na kerma ta soma rubutu cikin harshen turanci,

"Idan ba zaki iya rubutun ba, ki fada min ni saina rubuta" Angel ce tayi maganar, unaiza ta girgiza mata kai tare da cewa "Nafi so yaga handwritting ɗina, zaifi gane cewa ni ce da kaina na rubuta mashi" kusan shafi uku ta cika da rubutun, biyu na daddynta ɗaya na mommynta, bayan ta kammala ta rufe jotter ɗin, fuskarta ɗauke da murmushi ta ke kallon fuskokin su ɗaya bayan ɗaya, damuwace ƙarara akan nasu fuskokin, duk sun sha jinin jikin su ganin irin kallon da take bin su dashi, mai wuyar fassaruwa,

"Zan mutu ina farin ciki, saboda samun ku da nayi acikin rayuwata, ku ne mutane na farko da suka fara nuna min soyayya ta gaskiya kuma na tabbatar da hakan, naga damuwa akan fuskokin ku duk don saboda ni, dole inyi farin ciki na samun ƴan uwa masu ƙaunata, zanyi kewarku sosai, bansan dame zan saka maku ba, saboda bani da komai a yanzu, Amma ina da backpack, tare da earrings ɗina na gold tun a washe garin ranar da aka kawo ni prison na cire su daga kunne na, na ajiye su a cikin backpack ɗita, Na mallaka maku su, wata rana za su yi maku amfani idan Allah ya baku damar fita daga cikin kurkukun nan..." tun sautin kukansu na fita har takai ga muryoyin su sun disashe sai kallon ta su ke yi,

É—agowa ta yi da Rinannun idanuwanta akan fuskar Angel da ke kallonta,
Miƙa mata pant ɗin dake a dunƙule cikin tafin hannunta ta yi tare da cewa

"na baki shi kyauta Angel, dan Allah kada ki ce min baki so, inaso ku dinga tunawa dani acikin rayuwar ku, kodan saboda in samu masu yi min addu'a idan na mutu.

fashewa su kayi da matsanancin kuka, Hannu biyu angel ta sanya wurin kar6ar pant ɗin da unaiza ke miƙo mata, sosai ta matse shi acikin tafin hannunta muryarta na rawa tace"nah..na kar6a Unaiza, kuma zanyi amfani dashi, nagode sosai," Murmushi ne ya bayyana akan fuskar unaiza,

"Inaso ku bayyana min irin ƙaunar da kuke yi min," Atare suka haɗa baki wurin furta"wlh bazamu iya misalta maki irin ƙaunar da mu ke yi maki ba, muna son ki ƴar uwarmu, bamu ta6a ƙin ki ba, muna fatan mu kasance atare da ke har ƙarshen rayuwar mu,"

Dariyar farin ciki Unaiza ta saki, fararen haƙoranta kamar gonar auduga, Nan ta ke gaban su ya faɗi ganin Jinin dake gangarowa ta cikin ƙofofin hancinta, wata irin zufa ta fitar hayyaci ta soma tsastsafo mata, agigice suke kallonta sun kasa motsawa, ta tsakanin cinyoyinta jini ya shiga kurɗaɗowa, idanuwanta suka kaɗa jawur dasu, ta soma cizon la66anta, Da sauri Batul ta sanya hannu ta ruƙo ƙasan rigarta ta janye ta, Hankalinsu yai mugun tashi ganin yadda gabanta ya 6urma wurin ya jagwale sai uban rami, basu ta6a ganin tashin hankali irin na yau ba, gaban unaiza ya lalace, Da ƙarfi suka shiga ambaton “Inna lillahi wa inna ilayhir raji'un” tsabar fargabar abun da su ka gani yasa mutun huɗu daga cikin su suka sume nan take,

Angel ce ta yi ƙoƙarin biya mata, Kalmatusshahada ita da Deeja suka dinga maimaita mata, itama batul ta ɗauka atare suke karanto mata ita, A lokacin Allah ne ya nufi Unaiza zata furta kalmar nan saboda takai matakin ƙarshe, Harshenta yana dab da karyewa muryarta da wani irin sauti ta furta kalmar shahada, tana ƙarasawa murmushi ya bayyana akan kyakkyawar fuskarta idanuwanta a buɗe kanta ya faɗa saman kafadar batul dake a kusa da ita, rai yayi halinsa.

Kullu nafsin za'ikatul maut, Rest in jannatul firddaus Unaiza rai yayi halin shi, munayi mata fatan dacewa.........."
Chapter 159 · 0% Book details