Sashe 149
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Angel ta zame hannayenta da ga jikin Jamima, ta yi zumbur ta miƙe zaune, ɗagowa jamimah ta yi fuskarta jawur da ita ƴan kumatun sun yi suntum da su, Suna haɗa ido da Angel, ta zazzaro idanuwanta waje jikinta ya hau kerma a gigice ta duro daga saman gadon tare da ɗaura hannayenta sama ta fashe da wani irin matsanancin kuka na tashin hankali.
Lamarin yayi matuƙar girgiza Angel tasan bai wuci a bun da ya faru jiya bane yasa ta tsorata da ita, Jikinta ba ƙaramin sanyi ya yi ba, Saukowa tai daga saman gadonta tana tunkarar jamima tare da miƙa mata hannu muryarta na ɗan rawa tace"Jamima nice fa Angel ɗin ki, meyasa kike gudu na"? Girgiza kai ta dinga ki bakinta ƙumshe da kuka ta shiga faɗin"Ni ba Angel ɗita bace, Saboda baki son mu, Jiya kamar zaki kashe ni, kika cire min haƙorina,' ta yi maganar tare da zura yatsanta ɗaya cikin bakinta don taji idan dagaske ba haƙorin, rushewa ta kuma yi na wani sabon kukan jin gi6in da ke a bakinta, Tuni hawaye sun wanke fuskar Angel, tsananin tausayinta ne ya kamata.
"Bana son ki Angel! i hate you! I don't want to see you, because you're not human, you're a genie!"
Cikin shessheƙar ku ka Jamimah ta furta maganar, yayin da ta ke ƙoƙarin ja da baya ganin Angel na tunkaro ta, A jikin bango Jamima ta manne tana girgiza mata kai, alamar karta kuskura tazo wurin ta, zuciyar Angel ba ƙaramar karaya ta yi ba, ta rasa ina zata tsoma ranta ne taji daɗi, a gaban jamimah ta zuƙunna saman gwiwowinta, ba tare da ta iya furta komai ba.
Duk wannan abun da ke faruwa akan kunnuwan masu bacci waɗanda tuni sun jima da farkawa tun lokacin da Jamima ta rushe da kuka, Sautin ya daki dodon kunnuwan su, Tashin su kenan, hankalinsu gaba ɗaya akan Jamima da Angel, Azeeza ce ta soma shessheƙar kuka tana zaune saman gadonta, idanuwanta akan yatsun hannayenta da su ka jigata, duk sun faffashe sai sai babu ɗigon jini ko raɗaɗi, muryar ta adisashe ta ke yin magana.
"Na gaza yarda da abunda idanuwana su ka nuna min, bazan zargi Angel ba, amma meyasa ta take min yatsun hannuna? Meyasa ta buge mu? Laifin me mu ka mata"? Sosai ta fashe da matsanancin ku ka, Hakan ba ƙaramin rikita Angel yai ba, tana fama da jamimah ga su Azeeza sun ɗauka su ma.
Idanuwan kowannan su acike yake tab da ƙwalla, zuciyoyin su ba ƙaramin karaya su ka yi ba, Muryar Hanna tamkar zata fashe da kuka tace"Duk irin haƙurin da nake baki Angel baki saurareni ba, har cewa nayi ki haɗa da bugun da za ki yi ma jamimah ki yi min amma shine kika ƙi saurarena, ki ka haɗamu duka ni da ita, kika buga mu ƙasa har saida haƙorinta ya cire, ko ita baki tausaya mawa ba, ita da ta ke ƙarama"
Gaba ɗaya suna neman zautar da ita, sam ta kasa juyawa ta kallesu saboda nauyin haɗa ido da su ta ke ji, still bata motsa ba, tana a zuƙunne gaban Jamima dake ta shessheƙar kuka, Abun ya ta6a zuciyoyin su, sun kasa fahimtar cewa ba yin kanta bane, dama zai yi wuya su fahimci hakan, kawai sun yi imani da abunda idanuwansu suka nuna musu ne.
"Da yanzu na mutu babu ni babu ƙara cin abinci, mu fa biyu Angel ta haɗa dani da hibba ta buga mu ga ƙasa, hakan bai isheta ba, sai da ta taɗiye ƙafar rubina ta kife ƙasa tukunna hankalinta ya kwanta.........." parveen bata ƙarasa maganar ba saboda kukan daya ciyota, Angel taga haza, Zuciyarta sai tafarfasa ta ke yi, ta runtse idanuwanta sosai, tana sauraron kowannan su
"Har yanzu ƙuguna ba dai dai ya ke ba, ni banma san ya akai na dawo saman gado ba, Angel taso naƙasa min rayuwa" Acewar Sarah, tana magana tana dafe qugunta da hannu ɗaya........
Eve da ke ta matse ƙwalla ido jawur tace"Haka muma ta haɗa kawunan mu nida Yasmin Ta buga mu jikin bango, daga nan ma ni ban ƙara sanin meya faru ba" Sai da ta kammala sauraron kowan nan su, gwiwowinta duk sun sage, har wani jiri ta ke gani acikin idanuwanta, sunan Allah take ta ambato acikin bakinta, a daddafe ta samu ta miƙe tsaye tare da juyawa tana fuskantar su.
A Yayin da hawaye ke cigaba da yin sintiri saman fuskarta, sai faman jinjina kanta ta ke yi tana kallonsu da rinannun idanuwanta, babu wanda ya motsa daga saman gadon shi, duk suna a zaune suna kallonta, Kamar yarda idanuwan ta ke fitar da hawaye haka suma nasu ke tsiyaya, magana ta ke so ta yi amma ta kasa, wani irin raɗaɗi ta ke ji acan cikin zuciyarta, ga maƙoshinta da ke a bushe sai ƙaiƙayi ya ke mata.
"Kun yarda cewa ANGEL zata iya cutar da ku!"? Muryar Deeja ce ta janyo hankalin su zuwa ga dubanta, ta yi masu tambayar ne a yayin da ta ke saukowa daga saman gadonta, Tafiya take yi kamar babu wadataccen jini a jikinta, a tsakiyar É—akin nasu ta tsaya tana bin faces É—insu da kallo, ta É—aura da cewa"Tambayar ku na ke yi, ba ku bani amsa ba, jiya da abun ya faru me ya zo maku acikin ran ku"?
Azeeza ce ta fara yin magana acikin su"ni dai nasan Angel baza ta ta6a iya cutar da wani acikin mu ba, amma narasa gane meyasa ta yi mana hakan"? tai tambayar tana kallon Deeja,
Kamar yarda azeeza ta ce, suma sauran duk haka su ka ce, sun san bazata Iya cutar dasu ba, Angel koda wani ta gani zai cutar dasu bazata ƙyale shi ba, balle kuma ace ita da kanta ne ta yi musu hakan, abunda ya sanya musu kokwanto ya ruɗar dasu shine taya akai ta yi musu Jahilin bugun nan da kanta kuma da hannayenta!
Juyawa Deeja ta yi ta fuskanci Angel da ke atsaye kamar an dasa mata aya, Jikinta sai kerma yake yi.
"Ba laifin ta ba ne, kuma ba yin kanta bane, bakowa bane Ya jawo hakan fa ce muguwar matar nan, tsohuwa Zafreen! Itace silar komai, Idan har ba za ku manta ba, akan idon ku ta ɗaura mata sanda saman ƙirjinta, ni dama tun a lokacin raina ya bani cewar wani mugun abun ne za ta yi mata, dama tace bamu ta6a gabza faɗa a tsakanin mu ba, kuma wai a dokar prison ba'a amince ma kowani prisoner yaji daɗin rayuwar shi ba, Allah ya isa tsakanin mu da tsohuwa Zafreen, wlh ban ta6a danasanin tafiyar Tsohuwa Tamira ba irin na jiya, Mun yi babban rashi, ƙwara ita da daɗi da ba daɗi wani lokacin tana yi mana mutunci in taso"
Babu wanda jikin shi bai yi sanyi ba, yanzu sun fahimci cewa Ba yin kanta bane, dama basu yarda cewa zata iya yi musu hakan ba, Angel ɗin da take matuƙar ƙaunar su, in dai a kansu ne har ranta zata iya badawa don ta fanshe su, Ni shaida ce akan hakan!
Atare suka hada baki wurin bata haƙuri, tace masu basu ne ya kamata su bata haƙuri ba, duk da ba yin kanta bane, Ita ya dace ace ta basu haƙuri tun da da ita a ka yi amfani wurin cutar da su, don haka tana me neman yafiya agare su, su yi hakuri su yafe mata, kuma in sha Allah hakan ba zata ƙara faruwa ba, ita kanta ta yi mamakin yarda akai Sihirin tsohuwa Zafreen Ya kama jikinta, duk da shi sirihi gaskiya ne, kuma babu wanda yafi ƙarfin ya shiga jikin shi sai wanda Allah ya tsare! Shiyasa ake so bawa ya kasance mai neman tsari awurin ubangiji, ba dole sai abu ya risƙe ka ba, kace zaka fara roƙon Allah, a'a a koda yaushe ka kasance cikin neman tsari daga gare shi, addu'ar nan itace takobin mumini, after that azhkar na safe dana marece, mutun ya dage da yin shi ba fashi, da wuya kaga wanda ke yin azhkar mummunan abu ya faru dashi ba tare da Allah ya tsare shi ba!, Allah dai yasa mu dace.
Bayan Angel ta nemi yafiyar su Hankalin kowannan su ya kwanta banda mutun É—aya, Jamima itafa har ga Allah tsoron Angel ta ke ji,
Abun ka ga yaro Ta ƙame jikin bango sai kuka take yi musu tana faɗin itafa bata son ganin Angel, cos she's a genie ba mutun bace, ba zata zauna a ɗaki ɗaya da ita ba, sai dai su rufe ta a cikin toilet, idan an kawo abinci su dinga kai mata acan tana ci, idan har ba su yi hakan ba, ita zata koma da yin rayuwa acikin toilet ɗinne, Abu kamar wasa ta sanya musu rigima, babu wanda bai lallashe ta ba acikin su akan ta yi haƙuri amma taƙiya, ƴar tahalikar nan har bayani su ka yi mata yadda zata fahinci cewa ba laifin Angel bane amma tace musu tasan me ta ke yi, su daina ganinta ƴar ƙarama kar take kallon su, Har ita za su yi ma wayau, so su ke ta zauna tare da Angel ɗaki ɗaya don ta samu damar ƙarasa 6alle mata sauran haƙoranta da suka rage abakinta.
Maganganun Jamimah sun yi matuƙar basu dariya, ita abunda yafi 6ata mata rai, Haƙorinta ɗaya da Angel ta cire mata, Angel har ce mata ta yi ta kwantar da hankalinta, ita yarinya ce ba ta gama fanfara ba, wani haƙorin zai fito mata, amma taƙi yarda da zancenta, Ko kusa da ita taƙi bari Angel ta je, Tsabar yarda take zabgawa Angel harara kamar idonta zai faɗo ƙasa.
Har tambayar Angel su ka yi ya akai Jiya suka dawo saman gadajen su? Sannan ya a kai basu ga jinin su da ya yi bleeding ba, a jikin bango da ƙasan ɗakin, sannan kuma ya akai Basu tashi da raɗaɗin ciwon su ba, Deeja ce ta basu amsa da cewa"Allah ne ya kawo mana ɗauki, narasa ya zanyi a lokacin saina roƙe shi, akan ya bani mafita, kuma cikin ikon Allah Sai gashi kowannan mu ya tashi babu ciwo a jikin mu,"
Lamarin yayi matuƙar girgiza Angel tasan bai wuci a bun da ya faru jiya bane yasa ta tsorata da ita, Jikinta ba ƙaramin sanyi ya yi ba, Saukowa tai daga saman gadonta tana tunkarar jamima tare da miƙa mata hannu muryarta na ɗan rawa tace"Jamima nice fa Angel ɗin ki, meyasa kike gudu na"? Girgiza kai ta dinga ki bakinta ƙumshe da kuka ta shiga faɗin"Ni ba Angel ɗita bace, Saboda baki son mu, Jiya kamar zaki kashe ni, kika cire min haƙorina,' ta yi maganar tare da zura yatsanta ɗaya cikin bakinta don taji idan dagaske ba haƙorin, rushewa ta kuma yi na wani sabon kukan jin gi6in da ke a bakinta, Tuni hawaye sun wanke fuskar Angel, tsananin tausayinta ne ya kamata.
"Bana son ki Angel! i hate you! I don't want to see you, because you're not human, you're a genie!"
Cikin shessheƙar ku ka Jamimah ta furta maganar, yayin da ta ke ƙoƙarin ja da baya ganin Angel na tunkaro ta, A jikin bango Jamima ta manne tana girgiza mata kai, alamar karta kuskura tazo wurin ta, zuciyar Angel ba ƙaramar karaya ta yi ba, ta rasa ina zata tsoma ranta ne taji daɗi, a gaban jamimah ta zuƙunna saman gwiwowinta, ba tare da ta iya furta komai ba.
Duk wannan abun da ke faruwa akan kunnuwan masu bacci waɗanda tuni sun jima da farkawa tun lokacin da Jamima ta rushe da kuka, Sautin ya daki dodon kunnuwan su, Tashin su kenan, hankalinsu gaba ɗaya akan Jamima da Angel, Azeeza ce ta soma shessheƙar kuka tana zaune saman gadonta, idanuwanta akan yatsun hannayenta da su ka jigata, duk sun faffashe sai sai babu ɗigon jini ko raɗaɗi, muryar ta adisashe ta ke yin magana.
"Na gaza yarda da abunda idanuwana su ka nuna min, bazan zargi Angel ba, amma meyasa ta take min yatsun hannuna? Meyasa ta buge mu? Laifin me mu ka mata"? Sosai ta fashe da matsanancin ku ka, Hakan ba ƙaramin rikita Angel yai ba, tana fama da jamimah ga su Azeeza sun ɗauka su ma.
Idanuwan kowannan su acike yake tab da ƙwalla, zuciyoyin su ba ƙaramin karaya su ka yi ba, Muryar Hanna tamkar zata fashe da kuka tace"Duk irin haƙurin da nake baki Angel baki saurareni ba, har cewa nayi ki haɗa da bugun da za ki yi ma jamimah ki yi min amma shine kika ƙi saurarena, ki ka haɗamu duka ni da ita, kika buga mu ƙasa har saida haƙorinta ya cire, ko ita baki tausaya mawa ba, ita da ta ke ƙarama"
Gaba ɗaya suna neman zautar da ita, sam ta kasa juyawa ta kallesu saboda nauyin haɗa ido da su ta ke ji, still bata motsa ba, tana a zuƙunne gaban Jamima dake ta shessheƙar kuka, Abun ya ta6a zuciyoyin su, sun kasa fahimtar cewa ba yin kanta bane, dama zai yi wuya su fahimci hakan, kawai sun yi imani da abunda idanuwansu suka nuna musu ne.
"Da yanzu na mutu babu ni babu ƙara cin abinci, mu fa biyu Angel ta haɗa dani da hibba ta buga mu ga ƙasa, hakan bai isheta ba, sai da ta taɗiye ƙafar rubina ta kife ƙasa tukunna hankalinta ya kwanta.........." parveen bata ƙarasa maganar ba saboda kukan daya ciyota, Angel taga haza, Zuciyarta sai tafarfasa ta ke yi, ta runtse idanuwanta sosai, tana sauraron kowannan su
"Har yanzu ƙuguna ba dai dai ya ke ba, ni banma san ya akai na dawo saman gado ba, Angel taso naƙasa min rayuwa" Acewar Sarah, tana magana tana dafe qugunta da hannu ɗaya........
Eve da ke ta matse ƙwalla ido jawur tace"Haka muma ta haɗa kawunan mu nida Yasmin Ta buga mu jikin bango, daga nan ma ni ban ƙara sanin meya faru ba" Sai da ta kammala sauraron kowan nan su, gwiwowinta duk sun sage, har wani jiri ta ke gani acikin idanuwanta, sunan Allah take ta ambato acikin bakinta, a daddafe ta samu ta miƙe tsaye tare da juyawa tana fuskantar su.
A Yayin da hawaye ke cigaba da yin sintiri saman fuskarta, sai faman jinjina kanta ta ke yi tana kallonsu da rinannun idanuwanta, babu wanda ya motsa daga saman gadon shi, duk suna a zaune suna kallonta, Kamar yarda idanuwan ta ke fitar da hawaye haka suma nasu ke tsiyaya, magana ta ke so ta yi amma ta kasa, wani irin raɗaɗi ta ke ji acan cikin zuciyarta, ga maƙoshinta da ke a bushe sai ƙaiƙayi ya ke mata.
"Kun yarda cewa ANGEL zata iya cutar da ku!"? Muryar Deeja ce ta janyo hankalin su zuwa ga dubanta, ta yi masu tambayar ne a yayin da ta ke saukowa daga saman gadonta, Tafiya take yi kamar babu wadataccen jini a jikinta, a tsakiyar É—akin nasu ta tsaya tana bin faces É—insu da kallo, ta É—aura da cewa"Tambayar ku na ke yi, ba ku bani amsa ba, jiya da abun ya faru me ya zo maku acikin ran ku"?
Azeeza ce ta fara yin magana acikin su"ni dai nasan Angel baza ta ta6a iya cutar da wani acikin mu ba, amma narasa gane meyasa ta yi mana hakan"? tai tambayar tana kallon Deeja,
Kamar yarda azeeza ta ce, suma sauran duk haka su ka ce, sun san bazata Iya cutar dasu ba, Angel koda wani ta gani zai cutar dasu bazata ƙyale shi ba, balle kuma ace ita da kanta ne ta yi musu hakan, abunda ya sanya musu kokwanto ya ruɗar dasu shine taya akai ta yi musu Jahilin bugun nan da kanta kuma da hannayenta!
Juyawa Deeja ta yi ta fuskanci Angel da ke atsaye kamar an dasa mata aya, Jikinta sai kerma yake yi.
"Ba laifin ta ba ne, kuma ba yin kanta bane, bakowa bane Ya jawo hakan fa ce muguwar matar nan, tsohuwa Zafreen! Itace silar komai, Idan har ba za ku manta ba, akan idon ku ta ɗaura mata sanda saman ƙirjinta, ni dama tun a lokacin raina ya bani cewar wani mugun abun ne za ta yi mata, dama tace bamu ta6a gabza faɗa a tsakanin mu ba, kuma wai a dokar prison ba'a amince ma kowani prisoner yaji daɗin rayuwar shi ba, Allah ya isa tsakanin mu da tsohuwa Zafreen, wlh ban ta6a danasanin tafiyar Tsohuwa Tamira ba irin na jiya, Mun yi babban rashi, ƙwara ita da daɗi da ba daɗi wani lokacin tana yi mana mutunci in taso"
Babu wanda jikin shi bai yi sanyi ba, yanzu sun fahimci cewa Ba yin kanta bane, dama basu yarda cewa zata iya yi musu hakan ba, Angel ɗin da take matuƙar ƙaunar su, in dai a kansu ne har ranta zata iya badawa don ta fanshe su, Ni shaida ce akan hakan!
Atare suka hada baki wurin bata haƙuri, tace masu basu ne ya kamata su bata haƙuri ba, duk da ba yin kanta bane, Ita ya dace ace ta basu haƙuri tun da da ita a ka yi amfani wurin cutar da su, don haka tana me neman yafiya agare su, su yi hakuri su yafe mata, kuma in sha Allah hakan ba zata ƙara faruwa ba, ita kanta ta yi mamakin yarda akai Sihirin tsohuwa Zafreen Ya kama jikinta, duk da shi sirihi gaskiya ne, kuma babu wanda yafi ƙarfin ya shiga jikin shi sai wanda Allah ya tsare! Shiyasa ake so bawa ya kasance mai neman tsari awurin ubangiji, ba dole sai abu ya risƙe ka ba, kace zaka fara roƙon Allah, a'a a koda yaushe ka kasance cikin neman tsari daga gare shi, addu'ar nan itace takobin mumini, after that azhkar na safe dana marece, mutun ya dage da yin shi ba fashi, da wuya kaga wanda ke yin azhkar mummunan abu ya faru dashi ba tare da Allah ya tsare shi ba!, Allah dai yasa mu dace.
Bayan Angel ta nemi yafiyar su Hankalin kowannan su ya kwanta banda mutun É—aya, Jamima itafa har ga Allah tsoron Angel ta ke ji,
Abun ka ga yaro Ta ƙame jikin bango sai kuka take yi musu tana faɗin itafa bata son ganin Angel, cos she's a genie ba mutun bace, ba zata zauna a ɗaki ɗaya da ita ba, sai dai su rufe ta a cikin toilet, idan an kawo abinci su dinga kai mata acan tana ci, idan har ba su yi hakan ba, ita zata koma da yin rayuwa acikin toilet ɗinne, Abu kamar wasa ta sanya musu rigima, babu wanda bai lallashe ta ba acikin su akan ta yi haƙuri amma taƙiya, ƴar tahalikar nan har bayani su ka yi mata yadda zata fahinci cewa ba laifin Angel bane amma tace musu tasan me ta ke yi, su daina ganinta ƴar ƙarama kar take kallon su, Har ita za su yi ma wayau, so su ke ta zauna tare da Angel ɗaki ɗaya don ta samu damar ƙarasa 6alle mata sauran haƙoranta da suka rage abakinta.
Maganganun Jamimah sun yi matuƙar basu dariya, ita abunda yafi 6ata mata rai, Haƙorinta ɗaya da Angel ta cire mata, Angel har ce mata ta yi ta kwantar da hankalinta, ita yarinya ce ba ta gama fanfara ba, wani haƙorin zai fito mata, amma taƙi yarda da zancenta, Ko kusa da ita taƙi bari Angel ta je, Tsabar yarda take zabgawa Angel harara kamar idonta zai faɗo ƙasa.
Har tambayar Angel su ka yi ya akai Jiya suka dawo saman gadajen su? Sannan ya a kai basu ga jinin su da ya yi bleeding ba, a jikin bango da ƙasan ɗakin, sannan kuma ya akai Basu tashi da raɗaɗin ciwon su ba, Deeja ce ta basu amsa da cewa"Allah ne ya kawo mana ɗauki, narasa ya zanyi a lokacin saina roƙe shi, akan ya bani mafita, kuma cikin ikon Allah Sai gashi kowannan mu ya tashi babu ciwo a jikin mu,"