Sashe 100
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun da ta dure tagar nan , danish ya kasa motsawa tamkar an ruƙe ƙafafuwan shi, Jikin shi yai mugun sanyi tamkar wanda aka zarewa laka, idanuwan shi na akan wandonta data bar mishi ruƙe a hannun shi, Kallon shi yake yi batare da ƙyaftawar ido ba, tsabar tashin hankali ne ƙarara akan fuskarshi , babban abunda yake jima tsoro Hannun da Angel zata faɗa, ba lallai ta Iya ganewa Ginin kurkukun ba. Domin kuwa a birkice yake. Idan har ba ka da ilmi akan shi, har ta6in hankali zaka iya samu saboda ruɗanin da zaka shiga,
Muryar shi na rawa ya furta"bazan ƙyale ta ba, why angel? Dole na bi bayanki, " Yana yunƙurin haura tagar, kunnuwan shi suka jiyo mishi sautin muryar haris dake ta ƙwala ma shi kira daga can cikin ɗakin su, Aikuwa a matuƙar ruɗe Ya fasa Yunƙurin dura tagar, da sauri Ya nannaɗe wandon angel. Ya wurga shi saman tukunyar fulawar nan ta Cikin toilet ɗin, kafin ya miƙa hannu ya ɗauki fitilar da angel ta ajiye acikin toilet ɗin, Ya juya ya nufi hanyar fita, buɗe ƙopar shi keda wuya, Sai ga haris ya faɗo sashen toilet ɗin hannun shi ruƙe da fitila, Haska fuskar danish yai, ganin shi ne yasa shi sauke ajiyar zuciya, sam ya gaza runtsawa saboda tunanin mutun biyun nan batool da kuma danish, fargabar Halin da suke aciki Ya hana shi sakat.
danish ya yi mamaki zuwan haris nemanshi , bai ta6a tsammanin wani daga Cikin su zai waiwaye shi ba. Duba da irin aika aikar da ya yi musu.
Sun ɗauki tsawon mintuna suna kallon Juna, sai daga bisani haris ya jefa mashi harara tare da cewa"Ya jikin naka"? daƙyar danish ya samu ya dai daita natsuwarshi, Cikin sanyin murya yace"Da sauƙi" ta6e baki haris yae kafin ya kuma cewa"ka zo mu koma ɗaki, naga baka ci breakfast ɗinka dana ajiye maka ba, kuma nasan kana jin yunwa, tun safe har dare ko ruwa baka sha ba," yana magana yana wurga mashi harara dake nuni da cewa ba don yaso yake yi mishi maganar ba, har yanzu akwai sauran haushin shi da yake ji acikin zuciyar shi,
Danish bai motsa ba, kallon haris kawai yake yi, shi damuwarshi akan angel ne, Baya jin zai Iya bin haris su koma É—aki,
Jin yayi shiru yasa haris sake cewa"magana fa nake yi maka"? Fuskarshi a yamutse ya soma magana,
"Meyasa ka damu da ni? Duk irin abunda na aikata mu ku? Rai a6ace haris yace"ba wannan na tambaye ka ba, abinci nake magana, kazo muje ka ci" girgixa kai danish yai alamar a'a yace"Na ƙoshi, ka ƙyale ni koda yunwa zata kashe ni, bai shafe ka ba, lokacin dana buƙaci taimako awurinku, akan ku bani ruwa in sha, ka tuna abunda ka yi mani?
A fusace haris yaja dogon tsoki tare da matsawa ciki ya ruƙo hannun danish da niyar ya fusgoshi su tafi, da sauri danish ya ƙwace hannun shi, cikin kakkausar murya yace"Nace maka bazanci ba! Ka rabu dani! Babu ruwan kowa da rayuwata, tun da kun nuna cewa bani da amfani acikin ku," wani irin kallo haris yake bin shi da shi, kowannan su sai faman huci yake yi,
Shi burin shi haris ya tafi ya bashi wuri ko ya samu yaje ya taimaki angel, don yasan yanzu haka tana can tana neman É—auki ta gama furgicewa,
Haris Na ƙoƙarin buɗe baki don Ya mayar mishi da martani, Muryar Deeja Ta katse mishi Hanzarin shi, daga can cikin ɗaki Ya jiyota tana ƙwala mishi Kira, don dole ya saki hannun Danish Ya juya da gudu ya koma Cikin ɗakin,
Shigar shi ke da wuya, Ya yi arba dasu deeja gaba ɗayansu agaban gadon Azeeza, tunkafin ma ya ƙarasa shiga hankalin shi yai matuƙar tashi, Ganin azeeza rungume jikin deeja, babu numfashi, kamar matatta, Su parveen sun tasa ta gaba sai kuka suke Yi,
A bunda ya faru, Tun lokacin da azeeza ta 6oye ƙarƙashin gado ta 6oye don kada giant ya ɗauke ta, gaba ɗaya sun manta da azeeza, da ta 6oye a ƙarƙashin gadon ta, Har suka kwanta basu tuna da ita ba, sai daga baya ne deeja tana kwance saman gadonta, ta yi zurfi acikin tunaninta, kwakwalwata ta soma tariyo mata abunda ya faru kafin atafi da Batool, Nan take ta dafe ƙirji, ta miƙe zaune tana Ambaton sunan azeeza, Koda sauran ƴan uwan nasu suka ji tana kiran sunan azeeza, suma sai suka wartsake kowa Ya sauko daga saman gadon shi, A gaggauce Deeja ta ɗauko dayar fitilar data rage a ɗakin, Ta ajiye ta daga ƙasa gefen gadon Azeeza, Ta zuƙunna tana leƙa kanta ciki, Anan ne taganta xaune Kamar gunki babu abunda ke motsi ajikinta, Ta fashe da kuka Tare da kai hannu ta 6an6arota daga Jikin bangon data jingina, ta janyota wajen gadon, ta kwantar da ita saman jikinta, Su Hanna duk suka kewayesu, kowa ya zuƙunna suna ta kuka suna ambaton Sunan Azeeza, Zuciyoyinsu duk sun karaya, ganin yadda jikinta ya sandare, Cikin shessheƙar kuka hibba tace su jira ta dauko ruwa a yayyafa mata wata'ƙil su samu ta farka, tana karasa yin maganar ta miƙe ta ɗauki fitilar ta nufi gadon batool, tana laluban robobin ruwan da suka ajiye, sai dai bata samu ko ɗaya ba, duk sun ƙare, Jiki amace hibba ta dawo tana haska su da fitilar hannunta tace babu ruwa, bari naje toilet na ɗebo, har ta juya zata nufi toilet ɗin, Muryar deeja ta katse ta da cewa"Ina haris yake? Naji motsin shi ɗazu, Ya sauko daga saman gadon shi, ina tunanin toilet ya shiga, Bari na kwala mishi kira yazo," Batare da6ata lokaci ba, deeja ta shiga kwala mishi kira, Sai gashi ya faɗo Cikin ɗaki,
Haris na ƙarasawa kusa dasu, Muryarshi na ɗan rawa ya ambaci sunan azeeza tare da cewa Meya faru da ita? Nan suka sanar dashi komai, tun daga zuwan Giant, dafe kanshi yai da hannu ɗaya, idanuwanshi sunyi jajur, zuciyarshi duk ba daɗi, Yau dai gaba ɗaya basu ji daɗin ranar ba, sun yini da baƙin Ciki acikin ransu,
Kallonsu parveen yae ganin yadda suke ta yin kuka babu ƙaƙƙautawa, Cikin sigar lallashi yace"Ku kwantar da hankalin ku, azeeza zata farka suma ne tayi, bari naje na ɗebo ruwa a yayyafa mata" yakai karshen maganar tare da juyawa Ya nufi cikin ɗakin, Yana laluban Inda ya jefar da robar ruwan daya watsa ma danish ɗazu, Cikin sa'a yaci karo da ita can gefen dining carpet ɗinsu, Da azama ya je ya ɗauko bottle water ɗin Ya juya ya nufi sashen toilet ɗin su.
Lokacin daya shiga, baiga danish ba, babu shi babu alamarshi, Sai dai bai kawo komai aranshi ba, ganin ɗaya daga Cikin ƙopar toilets ɗin nasu a garƙame, sai yayi tsammanin ko yana aciki ne, ɗayan toilet ɗin ya shiga ya kunna fanfo ya tarba robar ruwan, sai da ta Cika tab, kafin Ya kashe fanfon Ya fito daga Cikin toilet ɗin Ya koma inda su deeja suke a zazzaune, Zuƙunnawa yai, bayan ya ajiye fitilar hannunshi, Ya tarba ruwan a tafin hannun shi ɗaya, Ya watsa ma azeeza saman fuskarta, Kowa ya baza ido yana jiran ganin ta farka, amma shiru ko motsi bata Yi ba, Nan fa hankulan su suka ƙara tashi matuƙa,
Cikin shessheƙar kuka suka haɗa baki suna roƙon azeeza akan ta taimaka musu ta farka, Haris dasu Javed sai lallashinsu suke Yi, ganin yadda duk suka shiga damuwa, parveen na kuka tace"tun da muke arayuwar mu ba mu ta6a fuskantar tashin hankali, irin na yau ba, An ɗauke mana batool, ga azeeza kuma taƙi farkawa, Ni tsorona ma kada ace ta mutu....." kasa ƙarasa maganar ta yi saboda kukan daya ciyota, ta kifa kanta saman gwiwarta, muryar deeja adisashe tace"dan Allah ku daina maganar mutuwa, wlh bana sonji, in sha Allah azeezan mu zata farka, babu abunda zai same ta, addu'a ya kamata muyi mata," Haris yace"wace irin addu'a? Babu abunda zata yi mana, kawai dai mu jira zuwa lokacin da zata farka," idanuwanta cike tab take ƙwalla take kallon shi,
Tsananin tausayinsu ne ya kamata haris, bayin Allah, tun safe hankalin su ba'a kwance yake ba, ga shi har dare ya ratsa basu runtsa ba,
Kusan sau uku haris yana yayyafa ma azeeza ruwa akan fuskarta amma taƙi farkawa, Jikinsu duk yai sanyi, haka suka zauna a kewaye da ita, suna kallonta yayin da hawaye ke cigaba da sauka a kan fuskar kowannan su.
"To ko dai mu yi ma tsohuwa magana tazo ta duba ta kada ta mutu" acewar yasmin, har suna haɗa baki wurin cewa"Taje ta kirawo ta," Da sauri yasmin ta miƙe ta dauki fitila ta wuce ɗakin tsohuwa, lokacin da yasmin ta bubbuga ƙopar ɗakin tsohuwa bata buɗe mata ba, kusan sau takwas tana yin knocking kamar zata 6alle ƙopar har saida haris yace mata ta dawo zai iyayiyuwa bata nan,Tukunna ta ƙyale ƙopar ta dawo wurinsu ta zuƙunna,
Magiya suka soma Yi mata akan tafarka
"Azeezan mu ki tashi dan Allah, Badan halin mu ba, wlh ba mu gaji dake ba Muna matuƙar ƙaunarki ƙaramar mu kuma babbar mu, pls wake up, kome kike so zamuyi maki, bazamu ƙara 6ata maki rai ba, kuma ba zamu bari giants su ɗaukar mana ke ba" kamar wasu sabbin mahaukata haka suka dinga yi mata sambatu akan tafarka, tun sunayin maganar da ƙwarinsu har ta kai ga muryoyinsu sun disashe, kowa yaja gefe suna matsar ƙwalla, idanuwansu duk sun kumbura saboda tsabar kukan da suka sha,
Muryar shi na rawa ya furta"bazan ƙyale ta ba, why angel? Dole na bi bayanki, " Yana yunƙurin haura tagar, kunnuwan shi suka jiyo mishi sautin muryar haris dake ta ƙwala ma shi kira daga can cikin ɗakin su, Aikuwa a matuƙar ruɗe Ya fasa Yunƙurin dura tagar, da sauri Ya nannaɗe wandon angel. Ya wurga shi saman tukunyar fulawar nan ta Cikin toilet ɗin, kafin ya miƙa hannu ya ɗauki fitilar da angel ta ajiye acikin toilet ɗin, Ya juya ya nufi hanyar fita, buɗe ƙopar shi keda wuya, Sai ga haris ya faɗo sashen toilet ɗin hannun shi ruƙe da fitila, Haska fuskar danish yai, ganin shi ne yasa shi sauke ajiyar zuciya, sam ya gaza runtsawa saboda tunanin mutun biyun nan batool da kuma danish, fargabar Halin da suke aciki Ya hana shi sakat.
danish ya yi mamaki zuwan haris nemanshi , bai ta6a tsammanin wani daga Cikin su zai waiwaye shi ba. Duba da irin aika aikar da ya yi musu.
Sun ɗauki tsawon mintuna suna kallon Juna, sai daga bisani haris ya jefa mashi harara tare da cewa"Ya jikin naka"? daƙyar danish ya samu ya dai daita natsuwarshi, Cikin sanyin murya yace"Da sauƙi" ta6e baki haris yae kafin ya kuma cewa"ka zo mu koma ɗaki, naga baka ci breakfast ɗinka dana ajiye maka ba, kuma nasan kana jin yunwa, tun safe har dare ko ruwa baka sha ba," yana magana yana wurga mashi harara dake nuni da cewa ba don yaso yake yi mishi maganar ba, har yanzu akwai sauran haushin shi da yake ji acikin zuciyar shi,
Danish bai motsa ba, kallon haris kawai yake yi, shi damuwarshi akan angel ne, Baya jin zai Iya bin haris su koma É—aki,
Jin yayi shiru yasa haris sake cewa"magana fa nake yi maka"? Fuskarshi a yamutse ya soma magana,
"Meyasa ka damu da ni? Duk irin abunda na aikata mu ku? Rai a6ace haris yace"ba wannan na tambaye ka ba, abinci nake magana, kazo muje ka ci" girgixa kai danish yai alamar a'a yace"Na ƙoshi, ka ƙyale ni koda yunwa zata kashe ni, bai shafe ka ba, lokacin dana buƙaci taimako awurinku, akan ku bani ruwa in sha, ka tuna abunda ka yi mani?
A fusace haris yaja dogon tsoki tare da matsawa ciki ya ruƙo hannun danish da niyar ya fusgoshi su tafi, da sauri danish ya ƙwace hannun shi, cikin kakkausar murya yace"Nace maka bazanci ba! Ka rabu dani! Babu ruwan kowa da rayuwata, tun da kun nuna cewa bani da amfani acikin ku," wani irin kallo haris yake bin shi da shi, kowannan su sai faman huci yake yi,
Shi burin shi haris ya tafi ya bashi wuri ko ya samu yaje ya taimaki angel, don yasan yanzu haka tana can tana neman É—auki ta gama furgicewa,
Haris Na ƙoƙarin buɗe baki don Ya mayar mishi da martani, Muryar Deeja Ta katse mishi Hanzarin shi, daga can cikin ɗaki Ya jiyota tana ƙwala mishi Kira, don dole ya saki hannun Danish Ya juya da gudu ya koma Cikin ɗakin,
Shigar shi ke da wuya, Ya yi arba dasu deeja gaba ɗayansu agaban gadon Azeeza, tunkafin ma ya ƙarasa shiga hankalin shi yai matuƙar tashi, Ganin azeeza rungume jikin deeja, babu numfashi, kamar matatta, Su parveen sun tasa ta gaba sai kuka suke Yi,
A bunda ya faru, Tun lokacin da azeeza ta 6oye ƙarƙashin gado ta 6oye don kada giant ya ɗauke ta, gaba ɗaya sun manta da azeeza, da ta 6oye a ƙarƙashin gadon ta, Har suka kwanta basu tuna da ita ba, sai daga baya ne deeja tana kwance saman gadonta, ta yi zurfi acikin tunaninta, kwakwalwata ta soma tariyo mata abunda ya faru kafin atafi da Batool, Nan take ta dafe ƙirji, ta miƙe zaune tana Ambaton sunan azeeza, Koda sauran ƴan uwan nasu suka ji tana kiran sunan azeeza, suma sai suka wartsake kowa Ya sauko daga saman gadon shi, A gaggauce Deeja ta ɗauko dayar fitilar data rage a ɗakin, Ta ajiye ta daga ƙasa gefen gadon Azeeza, Ta zuƙunna tana leƙa kanta ciki, Anan ne taganta xaune Kamar gunki babu abunda ke motsi ajikinta, Ta fashe da kuka Tare da kai hannu ta 6an6arota daga Jikin bangon data jingina, ta janyota wajen gadon, ta kwantar da ita saman jikinta, Su Hanna duk suka kewayesu, kowa ya zuƙunna suna ta kuka suna ambaton Sunan Azeeza, Zuciyoyinsu duk sun karaya, ganin yadda jikinta ya sandare, Cikin shessheƙar kuka hibba tace su jira ta dauko ruwa a yayyafa mata wata'ƙil su samu ta farka, tana karasa yin maganar ta miƙe ta ɗauki fitilar ta nufi gadon batool, tana laluban robobin ruwan da suka ajiye, sai dai bata samu ko ɗaya ba, duk sun ƙare, Jiki amace hibba ta dawo tana haska su da fitilar hannunta tace babu ruwa, bari naje toilet na ɗebo, har ta juya zata nufi toilet ɗin, Muryar deeja ta katse ta da cewa"Ina haris yake? Naji motsin shi ɗazu, Ya sauko daga saman gadon shi, ina tunanin toilet ya shiga, Bari na kwala mishi kira yazo," Batare da6ata lokaci ba, deeja ta shiga kwala mishi kira, Sai gashi ya faɗo Cikin ɗaki,
Haris na ƙarasawa kusa dasu, Muryarshi na ɗan rawa ya ambaci sunan azeeza tare da cewa Meya faru da ita? Nan suka sanar dashi komai, tun daga zuwan Giant, dafe kanshi yai da hannu ɗaya, idanuwanshi sunyi jajur, zuciyarshi duk ba daɗi, Yau dai gaba ɗaya basu ji daɗin ranar ba, sun yini da baƙin Ciki acikin ransu,
Kallonsu parveen yae ganin yadda suke ta yin kuka babu ƙaƙƙautawa, Cikin sigar lallashi yace"Ku kwantar da hankalin ku, azeeza zata farka suma ne tayi, bari naje na ɗebo ruwa a yayyafa mata" yakai karshen maganar tare da juyawa Ya nufi cikin ɗakin, Yana laluban Inda ya jefar da robar ruwan daya watsa ma danish ɗazu, Cikin sa'a yaci karo da ita can gefen dining carpet ɗinsu, Da azama ya je ya ɗauko bottle water ɗin Ya juya ya nufi sashen toilet ɗin su.
Lokacin daya shiga, baiga danish ba, babu shi babu alamarshi, Sai dai bai kawo komai aranshi ba, ganin ɗaya daga Cikin ƙopar toilets ɗin nasu a garƙame, sai yayi tsammanin ko yana aciki ne, ɗayan toilet ɗin ya shiga ya kunna fanfo ya tarba robar ruwan, sai da ta Cika tab, kafin Ya kashe fanfon Ya fito daga Cikin toilet ɗin Ya koma inda su deeja suke a zazzaune, Zuƙunnawa yai, bayan ya ajiye fitilar hannunshi, Ya tarba ruwan a tafin hannun shi ɗaya, Ya watsa ma azeeza saman fuskarta, Kowa ya baza ido yana jiran ganin ta farka, amma shiru ko motsi bata Yi ba, Nan fa hankulan su suka ƙara tashi matuƙa,
Cikin shessheƙar kuka suka haɗa baki suna roƙon azeeza akan ta taimaka musu ta farka, Haris dasu Javed sai lallashinsu suke Yi, ganin yadda duk suka shiga damuwa, parveen na kuka tace"tun da muke arayuwar mu ba mu ta6a fuskantar tashin hankali, irin na yau ba, An ɗauke mana batool, ga azeeza kuma taƙi farkawa, Ni tsorona ma kada ace ta mutu....." kasa ƙarasa maganar ta yi saboda kukan daya ciyota, ta kifa kanta saman gwiwarta, muryar deeja adisashe tace"dan Allah ku daina maganar mutuwa, wlh bana sonji, in sha Allah azeezan mu zata farka, babu abunda zai same ta, addu'a ya kamata muyi mata," Haris yace"wace irin addu'a? Babu abunda zata yi mana, kawai dai mu jira zuwa lokacin da zata farka," idanuwanta cike tab take ƙwalla take kallon shi,
Tsananin tausayinsu ne ya kamata haris, bayin Allah, tun safe hankalin su ba'a kwance yake ba, ga shi har dare ya ratsa basu runtsa ba,
Kusan sau uku haris yana yayyafa ma azeeza ruwa akan fuskarta amma taƙi farkawa, Jikinsu duk yai sanyi, haka suka zauna a kewaye da ita, suna kallonta yayin da hawaye ke cigaba da sauka a kan fuskar kowannan su.
"To ko dai mu yi ma tsohuwa magana tazo ta duba ta kada ta mutu" acewar yasmin, har suna haɗa baki wurin cewa"Taje ta kirawo ta," Da sauri yasmin ta miƙe ta dauki fitila ta wuce ɗakin tsohuwa, lokacin da yasmin ta bubbuga ƙopar ɗakin tsohuwa bata buɗe mata ba, kusan sau takwas tana yin knocking kamar zata 6alle ƙopar har saida haris yace mata ta dawo zai iyayiyuwa bata nan,Tukunna ta ƙyale ƙopar ta dawo wurinsu ta zuƙunna,
Magiya suka soma Yi mata akan tafarka
"Azeezan mu ki tashi dan Allah, Badan halin mu ba, wlh ba mu gaji dake ba Muna matuƙar ƙaunarki ƙaramar mu kuma babbar mu, pls wake up, kome kike so zamuyi maki, bazamu ƙara 6ata maki rai ba, kuma ba zamu bari giants su ɗaukar mana ke ba" kamar wasu sabbin mahaukata haka suka dinga yi mata sambatu akan tafarka, tun sunayin maganar da ƙwarinsu har ta kai ga muryoyinsu sun disashe, kowa yaja gefe suna matsar ƙwalla, idanuwansu duk sun kumbura saboda tsabar kukan da suka sha,