Sashe 163
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ya ku ke so tayi da ranta ne? Kalaman ku zasu iya sanyawa ta zauce, itama fa tana jin raɗaɗin da mu ke ji, saboda ta ɗaurawa kanta nauyin kula da rayuwar mu, so ku ke ku ƙara sanya mata damuwa har zuciyarta ta buga mu rasa ta? Meyasa za ku yi kokwanto akan addinin da tazo mana dashi? Saboda kun ji shiru har yau Allah bai kawo mana ɗauki ba? Ƙaddarar mu ce tazo a haka, ba lallai bane mu moriya rayuwar duniyar nan ba, amma ku tuna abunda Angel ta faɗa mana, ko kun manta ne, zai iya yiwuwa namu jin daɗin ba anan yake ba, sai ranar da muka koma ga mahaliccin mu! Itafa wannan rayuwar duniyar ƙanƙanuwa ce jin daɗinta na wucin gadi ne, kowa zai mutu ne, damu da wanda ke rayuwa awajen kurkukun nan da waɗanda suka azabtar da rayuwar mu, kaf zamu koma agare shi ne, mutuwa dole ce, zamu mutu zamu koma ga Allah, za'ayi mana hisabi tsakanin mu dasu! Allah zai bi mana haƙƙin mu, zasu ɗanɗani kuɗarsu, Ai mu abun farin ciki ne agare mu, Haƙƙinmu ya rataya akan wuyan waɗanda suke sarrafa rayuwar mu, don haka daga yau bana son wani ya ƙara yin kukan mutuwa acikin mu, Mu sanya wa ranmu cewa dole mu rasa wani acikin mu, ko muna so ko ba mu so, dole mu mutu, Mu zama masu tawakkali kada mu butulce wa Ubangijinmu, Abun da na fahimta wanda ba lallai bane ku fahince shiba, Allah shine ya ƙaddara zuwan Angel a gidan kurkukun nan donta sanar damu komai agame dashi, yanzu mu musulmai ne, kuma munyi imani da Allah, don haka babu gudu babu ja da baya, Duk runtsi duk wuya kada mu kuskura Mu rasa ƙwarin giwar da mu ke da shi, tsakanin mu da Angel sai godiya, Allah ya saka mata alkhairi, Allah ya bata ikon cigaba da taimakon mu...."
Kalaman Deeja sun sanyaya zuciyar Angel, Jikin kowan nan su Ya yi sanyi, sun yi danasanin maganganun da suka soma gaya mata, kusan atare suka haɗa baki suna bata haƙuri haɗi da lallashinta, hakan ba ƙaramin kwantar mata da hankalinta yayi ba, har lokacin bata ɗago da kanta daga saman ƙirjin batul ba'
Deeja tace masu su share hawayensu, Su yi rayuwar su tamkar babu abunda ya faru dasu, suka masa mata da toh, Duk da sun san abune mai wuya su dawo kamar yarda suke ada, A ranar sun ɗan samu sunci abincin Da Jamimah ta ajiye masu a cikin kwando, Bayan sun kammala ci, Kowan nan su ya yi wanka, A saman gadajen su suka kwakkwanta, zuciyoyin su a ƙuntace.
Rayuwar prisoners ta zama abun tausayi Cikin kwanakin nan, jimamin rashin ƴan uwansu ya hanasu sakat, Babu wasa babu dariya, kullum fuskokin su a bushe su ke, abu ɗaya ne su ke yi su ji daɗin shi, su kuma samu natsuwa da kwanciyar Hankali, Karatun qur'ani da Angel ta ke yi masu tsakar dare, a lokacin da take samun damar yin shi murya abuɗe ba tare da ta samu targarɗa ba, tasha ware kanta ita kaɗai, Ta ke6e a sashen toilet ɗinsu, ta ɗaga hannayenta sama hawaye nabin fuskarta, ta dinga roƙon Allah akan ya taimaka mata, kada yasa taji kunya a idanuwansu, ya agaza masu yajiƙan su, Ya kawo masu mafita ko dan taci ka masu alƙawarin data ɗaukar masu na ku6utar dasu daga Cikin kurkukun ƙaddara!
Ta zama abun tausayi, ga duk mai imani idan yaga yadda ta ke roƙon Allah sai ya matse mata ƙwalla. dukkan wasu ladubban yin addu'a ta iyasu, Saboda an koyar da ita, mutun biyun nan sun bata gudummuwa a cikin rayuwarta, shiyasa bazata ta6a mantawa dasu ba, mutun na farko Mahaifinta Tajuddeen, nagartaccen uba wanda ya tsaya mata tsayin daka don ta nemi duniyarta da lahirarta, lokacin da Unaiza ta bata labarin nata uban daya tarwatsa rayuwarta, sai taji ta ƙara ƙaunar daddynta, kuma har aranta taji cewa Mahaifinta bazai ta6a iya sadaukar da ita ba, ɗan adam ba abun yarda bane, amma ita ta yarda dashi har cikin ranta, saboda tasan halin daddynta ita shaida ce akan shi, ko dabba bazai Iya sadaukar ba balle ita da ya ɗauke ta tamkar ranshi! Mutum na biyu da bazata ta6a mantawa ba, ANEELERH CE, matsayin da ta bata a cikin zuciyarta na mahaifiyarta ne data gudu tabarta, Aneelerh uwace ta gari agare ta, dayawa wasu abubuwan da Angel ta iya da suka shafi addini da rayuwar duniya, Aneelerh ce ta koyar da ita su, hatta karatun makaranta idan aka yi mata, Aneelerh ce ke ƙara koya mata shi idan daddynta bai nan, Tana matuƙar son aunty aneelerh, kuma bata zarginta cikin waɗanda su ka sadaukar da ita! bayan aunty aneelerh da daddynta babu wani shege da take tunanin zata ɗaga ma ƙafa, muddin ta fita daga cikin kurkukun nan sun shiga uku, Hatta hajiya Adama da uncle Abdallah, da Alhaji ubaid kakanta, da maigadin gidansu, da abokan dadynta na wurin aiki, da makwabtan dake a kusa da gidansu kaf ɗinsu abun zargine awurinta, Ba wanda ta cire a cikinsu, dama kawai take jira ta samu, duk wani mai hannu acikin sadaukar da su, sai ta binciko su, alwashine ta ɗaukarwa kanta, shiyasa bata son ta dawwama agidan kurkukun saboda idan har tana aciki bazata ta6a Iya gano su wanene shuwagabannin kurkukun ba, Dole sai tana awaje zata samu damar gano munafukan, ta ci buri akan su, musamman mahaifin Unaiza JAN WUYA, wannan ɗan tahalikin duk ranar daya bari Angel ta dira ƙafarta daga cikin kurkuku, sunanshi matacce, muddin ta gano shi.
Tuntuni Angel ta ɗauko Jotter ɗin unaiza da ta ajiye mata a cikin toilet ɗinsu, tare da pant ɗin data bata kyauta, tana matuƙar son pant ɗin musamman da ya fito daga hannun Unaiza, yanzu haka pant ɗin yana sanye a jikinta ko wanke shi ba ta yi ba, saboda ta shaida tsaftar da ke a jikin shi, daga gani ranar da za'a kawota kurkukun ta sanya shi a jikinta, saboda sabuntakar shi. a cikin backpact ɗin Unaiza ta sanya jotter ɗin tare da biro din duka ta tura su ciki ta zage zip ɗinta, tana fatan Allah ya bata damar isar da wasiyyarta.
Bayin Allah sun zubama sarautar Allah ido, almost two month Yau, babu labarin su Haris, Danish kuwa yafi kowa daÉ—ewa don Yana acikin wata na uku da aka tafi dashi, tsakaninsu dasu addu'ace wadda ba fashi, kullum ne sai sunyi masu ita tare da waÉ—an da su ka rasu.
💔PRISONERS💔
Wuraren marece, Angel tana kwance saman gadonta, ta rungume pillow a ƙirjinta, ba zaka ta6a gane awani hali ta ke a ciki ba, ta lumshe idanuwanta tamkar mai yin bacci, Azeeza ce kwance a gefenta saman gadonta, Jamimah tana asaman bayanta ta haye ta ɗaura kanta, sun zamar mata alaƙaƙai, Kullum suna atare da ita, tana matuƙar son jinsu a tare da ita, babu mai yin magana a cikinsu, Parveen tana a kuɗundune cikin bargo saman gadon majnoon, kullum nan take kwana, da hannunta ta wanke jinin da ke abargon shi, ta gyara gadon taci gaba da kwana saman shi, saboda ƙaunar da ta ke yiwa majnoon ɗinta, wani lokacin har pillown shi ta ke yi ma wasa a matsayin majnoon kamar mai ta6in hankali.
Sarah na a zaune saman shimfiÉ—arta tare da Hibba da eve sai yasmin da rubina, babu mai magana acikin su duk sun yi zugudum, Deeja tana a kwance saman gadon Haris idonta na fuskantar ceilling, kowa dai da abunda ke damun shi, itama Hanna tana a naÉ—e saman gadonta.
Saukowa batul ta yi daga saman gadonta, Ta nufi sashen toilet ɗinsu, ba tare da kowa Ya ankara da ita ba, shigarta ke da wuya Angel ta buɗe idanuwanta muryarta asanyaye tace da jimamah ta sauka zata miƙe, zame jikinta ta yi daga na jamimah ta sauko daga saman gadon, Jikin ta duk ba ƙwari ga ramar da ta yi.
Sashen toilet ɗinsu ta nufa, tana shiga ta soma jin shessheƙar kukan batul, Hankalinta yai mugun tashi, bata zo da niyar tabi bayanta ba, tunawa da furennin dake a cikin tukunyar fulawar nan ne yasa ta zo sashen makewayin nasu, tun bayan rasuwar Unaiza babu wanda ke ba furennin ruwa saboda halin da su ka shiga, Cikin sanɗa ta nufi ƙopar toilet ɗin da batul ta shiga, A hankali ta tura ƙopar tare da Leƙa kanta ciki, karaf idanuwanta su ka sauka akan Batul da ke ta faman leƙa cikin wandonta da ta zame kamar wani abu ta ke dubawa,
Jin motsin shigowar mutun yasa ta firgice ta É—ago da idanuwanta fuskarta sharkaf da hawaye suna haÉ—a ido da Angel tasha jinin jikinta, da sauri ta gyara zaman wandon jikin ta.
"Batul me ya ke damun ki? Na jiyo shessheƙar kukan ki ne," wahalallan yawu ta haɗi, ba tare data furta mata komai ba.
Hakan ba ƙaramin ɗaga ma Angel hankali yai ba, fargabarta kar ace wani abu ne ya sami gabanta shiyasa ta ke kuka
"Ƴar uwata rabin raina, dan Allah ki faɗamin meke damun ki, Na yi maki alƙawarin bazan faɗama kowa ba, Hankalina ya tashi dana ga kina duba wandon Jikin ki, ina tsoron ace wani abu ne ke damun ki"
Ta ƙarasa maganar yayin da take nufar batul, girgiza mata kai ta dinga yi muryarta Ƙasa ƙasa take faɗin"Kada ki matso kusa dani Angel, babu abunda ke damuna, lafiyata qalau....." adabarbarce ta yi maganar.
Kalaman Deeja sun sanyaya zuciyar Angel, Jikin kowan nan su Ya yi sanyi, sun yi danasanin maganganun da suka soma gaya mata, kusan atare suka haɗa baki suna bata haƙuri haɗi da lallashinta, hakan ba ƙaramin kwantar mata da hankalinta yayi ba, har lokacin bata ɗago da kanta daga saman ƙirjin batul ba'
Deeja tace masu su share hawayensu, Su yi rayuwar su tamkar babu abunda ya faru dasu, suka masa mata da toh, Duk da sun san abune mai wuya su dawo kamar yarda suke ada, A ranar sun ɗan samu sunci abincin Da Jamimah ta ajiye masu a cikin kwando, Bayan sun kammala ci, Kowan nan su ya yi wanka, A saman gadajen su suka kwakkwanta, zuciyoyin su a ƙuntace.
Rayuwar prisoners ta zama abun tausayi Cikin kwanakin nan, jimamin rashin ƴan uwansu ya hanasu sakat, Babu wasa babu dariya, kullum fuskokin su a bushe su ke, abu ɗaya ne su ke yi su ji daɗin shi, su kuma samu natsuwa da kwanciyar Hankali, Karatun qur'ani da Angel ta ke yi masu tsakar dare, a lokacin da take samun damar yin shi murya abuɗe ba tare da ta samu targarɗa ba, tasha ware kanta ita kaɗai, Ta ke6e a sashen toilet ɗinsu, ta ɗaga hannayenta sama hawaye nabin fuskarta, ta dinga roƙon Allah akan ya taimaka mata, kada yasa taji kunya a idanuwansu, ya agaza masu yajiƙan su, Ya kawo masu mafita ko dan taci ka masu alƙawarin data ɗaukar masu na ku6utar dasu daga Cikin kurkukun ƙaddara!
Ta zama abun tausayi, ga duk mai imani idan yaga yadda ta ke roƙon Allah sai ya matse mata ƙwalla. dukkan wasu ladubban yin addu'a ta iyasu, Saboda an koyar da ita, mutun biyun nan sun bata gudummuwa a cikin rayuwarta, shiyasa bazata ta6a mantawa dasu ba, mutun na farko Mahaifinta Tajuddeen, nagartaccen uba wanda ya tsaya mata tsayin daka don ta nemi duniyarta da lahirarta, lokacin da Unaiza ta bata labarin nata uban daya tarwatsa rayuwarta, sai taji ta ƙara ƙaunar daddynta, kuma har aranta taji cewa Mahaifinta bazai ta6a iya sadaukar da ita ba, ɗan adam ba abun yarda bane, amma ita ta yarda dashi har cikin ranta, saboda tasan halin daddynta ita shaida ce akan shi, ko dabba bazai Iya sadaukar ba balle ita da ya ɗauke ta tamkar ranshi! Mutum na biyu da bazata ta6a mantawa ba, ANEELERH CE, matsayin da ta bata a cikin zuciyarta na mahaifiyarta ne data gudu tabarta, Aneelerh uwace ta gari agare ta, dayawa wasu abubuwan da Angel ta iya da suka shafi addini da rayuwar duniya, Aneelerh ce ta koyar da ita su, hatta karatun makaranta idan aka yi mata, Aneelerh ce ke ƙara koya mata shi idan daddynta bai nan, Tana matuƙar son aunty aneelerh, kuma bata zarginta cikin waɗanda su ka sadaukar da ita! bayan aunty aneelerh da daddynta babu wani shege da take tunanin zata ɗaga ma ƙafa, muddin ta fita daga cikin kurkukun nan sun shiga uku, Hatta hajiya Adama da uncle Abdallah, da Alhaji ubaid kakanta, da maigadin gidansu, da abokan dadynta na wurin aiki, da makwabtan dake a kusa da gidansu kaf ɗinsu abun zargine awurinta, Ba wanda ta cire a cikinsu, dama kawai take jira ta samu, duk wani mai hannu acikin sadaukar da su, sai ta binciko su, alwashine ta ɗaukarwa kanta, shiyasa bata son ta dawwama agidan kurkukun saboda idan har tana aciki bazata ta6a Iya gano su wanene shuwagabannin kurkukun ba, Dole sai tana awaje zata samu damar gano munafukan, ta ci buri akan su, musamman mahaifin Unaiza JAN WUYA, wannan ɗan tahalikin duk ranar daya bari Angel ta dira ƙafarta daga cikin kurkuku, sunanshi matacce, muddin ta gano shi.
Tuntuni Angel ta ɗauko Jotter ɗin unaiza da ta ajiye mata a cikin toilet ɗinsu, tare da pant ɗin data bata kyauta, tana matuƙar son pant ɗin musamman da ya fito daga hannun Unaiza, yanzu haka pant ɗin yana sanye a jikinta ko wanke shi ba ta yi ba, saboda ta shaida tsaftar da ke a jikin shi, daga gani ranar da za'a kawota kurkukun ta sanya shi a jikinta, saboda sabuntakar shi. a cikin backpact ɗin Unaiza ta sanya jotter ɗin tare da biro din duka ta tura su ciki ta zage zip ɗinta, tana fatan Allah ya bata damar isar da wasiyyarta.
Bayin Allah sun zubama sarautar Allah ido, almost two month Yau, babu labarin su Haris, Danish kuwa yafi kowa daÉ—ewa don Yana acikin wata na uku da aka tafi dashi, tsakaninsu dasu addu'ace wadda ba fashi, kullum ne sai sunyi masu ita tare da waÉ—an da su ka rasu.
💔PRISONERS💔
Wuraren marece, Angel tana kwance saman gadonta, ta rungume pillow a ƙirjinta, ba zaka ta6a gane awani hali ta ke a ciki ba, ta lumshe idanuwanta tamkar mai yin bacci, Azeeza ce kwance a gefenta saman gadonta, Jamimah tana asaman bayanta ta haye ta ɗaura kanta, sun zamar mata alaƙaƙai, Kullum suna atare da ita, tana matuƙar son jinsu a tare da ita, babu mai yin magana a cikinsu, Parveen tana a kuɗundune cikin bargo saman gadon majnoon, kullum nan take kwana, da hannunta ta wanke jinin da ke abargon shi, ta gyara gadon taci gaba da kwana saman shi, saboda ƙaunar da ta ke yiwa majnoon ɗinta, wani lokacin har pillown shi ta ke yi ma wasa a matsayin majnoon kamar mai ta6in hankali.
Sarah na a zaune saman shimfiÉ—arta tare da Hibba da eve sai yasmin da rubina, babu mai magana acikin su duk sun yi zugudum, Deeja tana a kwance saman gadon Haris idonta na fuskantar ceilling, kowa dai da abunda ke damun shi, itama Hanna tana a naÉ—e saman gadonta.
Saukowa batul ta yi daga saman gadonta, Ta nufi sashen toilet ɗinsu, ba tare da kowa Ya ankara da ita ba, shigarta ke da wuya Angel ta buɗe idanuwanta muryarta asanyaye tace da jimamah ta sauka zata miƙe, zame jikinta ta yi daga na jamimah ta sauko daga saman gadon, Jikin ta duk ba ƙwari ga ramar da ta yi.
Sashen toilet ɗinsu ta nufa, tana shiga ta soma jin shessheƙar kukan batul, Hankalinta yai mugun tashi, bata zo da niyar tabi bayanta ba, tunawa da furennin dake a cikin tukunyar fulawar nan ne yasa ta zo sashen makewayin nasu, tun bayan rasuwar Unaiza babu wanda ke ba furennin ruwa saboda halin da su ka shiga, Cikin sanɗa ta nufi ƙopar toilet ɗin da batul ta shiga, A hankali ta tura ƙopar tare da Leƙa kanta ciki, karaf idanuwanta su ka sauka akan Batul da ke ta faman leƙa cikin wandonta da ta zame kamar wani abu ta ke dubawa,
Jin motsin shigowar mutun yasa ta firgice ta É—ago da idanuwanta fuskarta sharkaf da hawaye suna haÉ—a ido da Angel tasha jinin jikinta, da sauri ta gyara zaman wandon jikin ta.
"Batul me ya ke damun ki? Na jiyo shessheƙar kukan ki ne," wahalallan yawu ta haɗi, ba tare data furta mata komai ba.
Hakan ba ƙaramin ɗaga ma Angel hankali yai ba, fargabarta kar ace wani abu ne ya sami gabanta shiyasa ta ke kuka
"Ƴar uwata rabin raina, dan Allah ki faɗamin meke damun ki, Na yi maki alƙawarin bazan faɗama kowa ba, Hankalina ya tashi dana ga kina duba wandon Jikin ki, ina tsoron ace wani abu ne ke damun ki"
Ta ƙarasa maganar yayin da take nufar batul, girgiza mata kai ta dinga yi muryarta Ƙasa ƙasa take faɗin"Kada ki matso kusa dani Angel, babu abunda ke damuna, lafiyata qalau....." adabarbarce ta yi maganar.