Sashe 133
Kurkukun Kaddara Takun Farko Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saukowa Angel tayi daga saman gadonta, da sauri ta nufi sashen toilet ɗinsu azeeza tabi bayanta, Suna shiga Cikin toilet ɗin da Unaiza take suka same ta kwance ƙasa, idanuwanta sun juye, Hankalin angel ba ƙaramin tashi yai ba, zuƙunnawa tayi agabanta tare da sanya hannayenta biyu ta ruƙo kafaɗunta, ta ɗago da ita zuwa ƙirjinta, ta faɗa, nan take angel taji zafin da ke ajikin unaiza na fitar hayyaci, hatta nunfashinta da hucin zafi yake fita, ta rasa gane wani irin ciwo ne ke damunta, kamar hada zazza6i, raba jikin su tai daga na juna, ta sanya hannu ta tallabo fuskarta, muryarta na kerma tace"Unaiza meke damun ki? Wani irin ciwo ne wannan"? Biji biji ta ke kallon angel, duk da tana acikin mawuyacin hali, sai da tayi mamakin ganinta, don bata ta6a tsammanin wani daga cikinsu zai iya taimaka mata ba, motsi ta soma yi da la66anta, sunan allura ne take faɗa musu wadda ake yi mata agida, idan ciwon ya tashi, sai dai sun gaza fahimtar me take cewa, koda ace ma sun gane, basu da hanyar da zasu iya samo mata allurar,
"Azeeza ɗauko min mayafin nan na kayan mu," ta amsa mata da toh, ɗaki azeeza ta shiga ta ɗauko Cotton scarve ɗinta, ta dawo ta miƙa ma angel bayan ta kar6a, tace ma azeeza ta zauƙunna ta ruƙe unaiza ajikinta, a cikin bokiti Angel ta tsoma mayafin cikin sauran ruwan da azeeza ta kora aman unaiza, sai da ya jiƙa ta matse shi, ta ɗaura shi saman jikin unaiza, ta dinga goga mata shi, ta ko'ina, ta yi mata hakan ne don ta samu relief ɗin zafin jikin ta.
sai nishi take yi tana fitar da numfashi awahalce, duk in ta ɗaura mayafin ajikinta sai ta zabura, alamar bata son ruwan jikin mayafin na ta6a jikin ta, bayan ta kammala, ta miƙe taje bakin igiyar toilet ɗinsu ta shanya Mayafin, Kafin ta dawo ta sanya hannu biyu ta ruƙo unaiza ta miƙar da ita, jikin ta babu ƙwari, dama ba wata ƙibar kirki ke gareta ba, a haka taja ta zuwa cikin ɗakinsu,
Suna shiga ciki, idanuwansu Hanna suka dawo kansu, gadon unaiza angel ta wuce da ita, tare da kwantar da ita sama, ta juya ta nufi akwati nansu, ta buÉ—e ta É—auko tissue ta koma saman gadon unaiza.
Dashi tai amfani wurin goge mata sauran jinin dake a hancinta, bayan ta kammala ta nannaɗe wanda ta goge jini da shi ta cusa su acikin wanda ta kuma yagowa, ta miƙa ma azeeza tace taje ta zuba a acikin trash can, ta amsa mata da toh, bayan ta kar6a ta juya ta nufi toilet dinsu, bada jimawa ba, Azeeza ta dawo ɗakin, gefen gadon unaiza ta koma ta zauna, ya kasance su biyu ne akusa da ita, jikinta ya ɗanyi sauƙi, ta ɗaura kanta saman pillow, still bata daina nishi ba, hannayenta na asaman mararta, addu'o'e angel ta karanto mata ta tottofa mata saman fuskarta da jikinta.
Hankalin Gabriel gaba ɗaya yana akan angel, yayin da shi kuma Danish nashi hankalin ke akan Gabriel, Ya kafe shi da ido ba tare da ƙyaftawa ba, sarai gabriel ya lura da kallon tuhumar da Danish ke yi mishi, amma sai ya basar.
Saukowa yai daga saman gadon shi ya nufi angel, da sauri Danish Ya miƙa shima Ya nufi gadon Unaiza, atare suka tsaya bakin gadon, har suna haɗa kafaɗa, Kallon mamaki Gabriel yai ma Danish, fuskar angel a yamutse ta kalle su, harara ta watsa ma Danish, muryarta ƙasa ƙasa tace"Shi ne ku na ganin bata da lafiya amma an rasa wanda zai taimaka mata acikin ku sai Azeeza"? Gabriel ne yace"Bansan time da ta farka daga bacci ba, hankalina baya akanta,"Danish yace"saboda ke yasa ban je wurin ta ba" ta6e baki ta ɗanyi, tare da juyar da kanta, Ta kalli su Hanna tunkafin ta yi magana parveen tace"ae kin hana mu zuwa wurinta saboda mayyace zata shanye mana jini, shiyasa mu ka ƙi taimakon ta"
Numfasawa tayi yayin da take kallonsu, Acan cikin zuciyarta tana tunanin taya zata fahimtar dasu cewa ba mayya ba ce? Kada su ɗauke ta maƙaryaciya, tun da ita ta faɗa mu su hakan da bakinta.
"Ae bance kada ku taimaka mata ba, idan bata da lafiya, a bun dana hana ku shi ne ku daina bari tana ta6a jikin ku, saboda babu kyau, wani ya kalli tsiraicin ka koya ta6a shi, Itama don batasan babu kyau ba ne shiyasa take yi, amma in muka ja ta ajikin mu mu ka fahimtar da ita zata daina ne....." tun kan ta rufe baki, Rubina tace"Hada jinin zata daina sha"? Ɗaga mata kai angel tai alamar eh, su ka ce toh zamu dinga taimakonta daga yanzu, amma itama kija mata kunne ta daina rashin jin magana, kuma ta daina yi mana gorin ƙirji," angel tace musu toh, zata ja mata kunne.
Mayar da idanuwanta ta yi akan su Danish dake atsaye, kowannan su ita ya ke kallo, ta rasa gane dililin yin tsayuwar na su akanta.
"Lafiya"? Tai tambayar tana jiran jin amsar su, kusan atare suka haÉ—a baki wurin cewa ba komai," juyawa gabriel yai tare da komawa gefen gadon shi ya zauna, shi ma danish ya koma nashi gadon ya zauna.
Duk wani motsin Gabriel Akan idon Danish, Ya hana shi sakat, Abu kamar wasa, Ko toilet Angel zata shiga sai Danish yabi bayanta, lamarin ya ɗaure mata kai, a bakin ƙopar toilet ɗin zai tsaya har saita fito sannan yaja hannunta su koma ɗaki, hakan ba ƙaramin 6ata ma Gabriel rai yai ba, shi burin shi su zauna da ita su tsara yarda zasu ɗauko ƴan uwansu, da kuma yarda zasu gudu daga Cikin kurkukun tun da yaji cewa itama tana da wannan ƙudirin aranta, Sai dai ga dukkan alamu, akwai mutun ɗaya da baison hakan ta faruwa, shiyasa ya hana shi sukuni, dama can bai yarda da Danish ba, tun zuwanshi, daga gani yana da wayau, akwai abunda yake 6oye musu, kuma yasan komai akan gidan kurkukun kallon su kawai ya ke yi.
Lokacin da dare ya yi kowannansu yai shirin kwanciya, mutun biyu ne babu alamun zasu runtsa.
Jikin Unaiza ya É—an lafa, da taimakon su azeeza taci abinci kaÉ—an, tun É—azu bacci yayi awon gaba da ita.
A tsakiyar ɗakin Gabriel ya dinga sintiri yana jiran bacci ya ɗauki Danish, Ko ya samu yaje su yi magana da Angel, amma ɗan tahalikin nan Yaƙi kwanciya, ƙarshe ma daya ga dagaske Gabriel ba bacci zaiyi ba, sai ya ɗauki pillow ɗinshi, Ya koma saman gadon Angel da ke kwance tana yin bacci, Ya ɗaura pillow ɗinsa saman mattress ɗinta, ya hau ya zauna tare da jingina bayan shi jikin pillow ɗin,' mamaki ƙarara akan fuskar gabriel, Ganin wani iko na Allah, a dole ya haƙura ya koma kan nashi gadon ya kwanta zuciyarshi acunkushe da tunani kala kala,.
Dare Ya nutsa sosai, Sunyi nisan kiwo acikin baccin su, har time ɗin Danish na zaune saman gadon angel, ahaka bacci yai awon gaba dashi, Ba zato ba tsammani, Unaiza tafarka tana ihu tana daddafe cikinta, wata irin kururuwa kamar ana zare ranta, a matuƙar firgice masu bacci suka soma farkawa Kowa Yana faman zazzare idanuwanshi, Haƙiƙa sunyi matuƙar firgita, ɗaya bayan ɗaya suka soma saukowa daga saman gadonsu suna tunkarar gadonta, mutun biyu ne basu farka ba, Jamima da majnun, kamar matattu sai sharar baccin su su ke yi, A kewaye da gadon unaiza suka tsaitsaya curko curko suna kallonta hankalin su yai matuƙar tashi, suka dinga tambayarta lafiya meke damunta, amma ta kasa buɗe baki ta basu amsa, Sai cizon la6en ta take yi, yayi suntum dashi, Angel tafi kowa shiga damuwa tsoranta, har ga Allah bata son wani abu ya samu unaiza duk da baƙin halinta tana ƙaunarta.
"Yanzu ya zamuyi da ita? Danish ba wani taimako da zaka iya yi mata? Angel ce tai maganar tana kallon shi, yae shiru bai ce mata komai ba,
Haris yace"ni fa inaga kamar kalar ciwon da su Hanna suka ta6a yi ne" gabansu ne yai wani irin mugun bugu jin abunda Haris yace, muryar deeja na arude tace"In sha Allah ba shi bane," Azeeza tuni ta fashe musu da kuka, tana zaune saman gadonta, ta kasa saukowa gudun kada ta faɗi ƙasa saboda lalurarta, tana jiyo muryoyinsu acikin kunnuwanta
Suna Cikin yin maganar nan, sautin motsin buɗe ƙopa ya karaɗe kunnuwasu, hankalin su ya ƙara tashi, nan take ransu ya basu cewa Anzo atafi da ita ne' jikin su duk yai sanyi, lokacin da su ka yi arba da Giant ɗin dake saukowa saman benan, basamudan ƙato, Mai ɗauke da star 1 agaban rigarshi, tunkan ya ƙaraso ciki, suka bashi hanya, Ya sanya hannu biyu ya ɗauki unaiza saman kafaɗarshi ya juya ya fuce da ita daga Cikin ɗakin, kamar wasu sakarkaru haka suka bi bayan shi da kallo har ya 6ace ma ganin su, Suna jiyo datse ƙopar ɗakin nasu da akayi, shi kenan an tafi da Ƴar gidan daddy, Gabriel yaso ya tambaye su ina za'a kai ta? Sai kuma ranshi ya bashi cewar wata'ƙil zasu kaita inda zasu duba lafiyarta ne, hakan yasa shi dakatawa da yin tambayar tashi, dama bai shirya yinta ba agaban Danish, don zai ƙara sa mashi ido ne.
Ba su ta6a tunanin zasu zubar mata da ƙwalla ba, saboda babu shaƙuwa atsakanin su da ita, Amma sai gashi yau saboda ita sun gaza runtsawa, a gefe da gefen gadonta matan su ka zauna shiru babu mai magana, Babu yadda haris baiyi dasu ba akan su koma su kwanta saman gadajen su, amma suka ƙiya, A ƙarshe nan suka kwana.
"Azeeza ɗauko min mayafin nan na kayan mu," ta amsa mata da toh, ɗaki azeeza ta shiga ta ɗauko Cotton scarve ɗinta, ta dawo ta miƙa ma angel bayan ta kar6a, tace ma azeeza ta zauƙunna ta ruƙe unaiza ajikinta, a cikin bokiti Angel ta tsoma mayafin cikin sauran ruwan da azeeza ta kora aman unaiza, sai da ya jiƙa ta matse shi, ta ɗaura shi saman jikin unaiza, ta dinga goga mata shi, ta ko'ina, ta yi mata hakan ne don ta samu relief ɗin zafin jikin ta.
sai nishi take yi tana fitar da numfashi awahalce, duk in ta ɗaura mayafin ajikinta sai ta zabura, alamar bata son ruwan jikin mayafin na ta6a jikin ta, bayan ta kammala, ta miƙe taje bakin igiyar toilet ɗinsu ta shanya Mayafin, Kafin ta dawo ta sanya hannu biyu ta ruƙo unaiza ta miƙar da ita, jikin ta babu ƙwari, dama ba wata ƙibar kirki ke gareta ba, a haka taja ta zuwa cikin ɗakinsu,
Suna shiga ciki, idanuwansu Hanna suka dawo kansu, gadon unaiza angel ta wuce da ita, tare da kwantar da ita sama, ta juya ta nufi akwati nansu, ta buÉ—e ta É—auko tissue ta koma saman gadon unaiza.
Dashi tai amfani wurin goge mata sauran jinin dake a hancinta, bayan ta kammala ta nannaɗe wanda ta goge jini da shi ta cusa su acikin wanda ta kuma yagowa, ta miƙa ma azeeza tace taje ta zuba a acikin trash can, ta amsa mata da toh, bayan ta kar6a ta juya ta nufi toilet dinsu, bada jimawa ba, Azeeza ta dawo ɗakin, gefen gadon unaiza ta koma ta zauna, ya kasance su biyu ne akusa da ita, jikinta ya ɗanyi sauƙi, ta ɗaura kanta saman pillow, still bata daina nishi ba, hannayenta na asaman mararta, addu'o'e angel ta karanto mata ta tottofa mata saman fuskarta da jikinta.
Hankalin Gabriel gaba ɗaya yana akan angel, yayin da shi kuma Danish nashi hankalin ke akan Gabriel, Ya kafe shi da ido ba tare da ƙyaftawa ba, sarai gabriel ya lura da kallon tuhumar da Danish ke yi mishi, amma sai ya basar.
Saukowa yai daga saman gadon shi ya nufi angel, da sauri Danish Ya miƙa shima Ya nufi gadon Unaiza, atare suka tsaya bakin gadon, har suna haɗa kafaɗa, Kallon mamaki Gabriel yai ma Danish, fuskar angel a yamutse ta kalle su, harara ta watsa ma Danish, muryarta ƙasa ƙasa tace"Shi ne ku na ganin bata da lafiya amma an rasa wanda zai taimaka mata acikin ku sai Azeeza"? Gabriel ne yace"Bansan time da ta farka daga bacci ba, hankalina baya akanta,"Danish yace"saboda ke yasa ban je wurin ta ba" ta6e baki ta ɗanyi, tare da juyar da kanta, Ta kalli su Hanna tunkafin ta yi magana parveen tace"ae kin hana mu zuwa wurinta saboda mayyace zata shanye mana jini, shiyasa mu ka ƙi taimakon ta"
Numfasawa tayi yayin da take kallonsu, Acan cikin zuciyarta tana tunanin taya zata fahimtar dasu cewa ba mayya ba ce? Kada su ɗauke ta maƙaryaciya, tun da ita ta faɗa mu su hakan da bakinta.
"Ae bance kada ku taimaka mata ba, idan bata da lafiya, a bun dana hana ku shi ne ku daina bari tana ta6a jikin ku, saboda babu kyau, wani ya kalli tsiraicin ka koya ta6a shi, Itama don batasan babu kyau ba ne shiyasa take yi, amma in muka ja ta ajikin mu mu ka fahimtar da ita zata daina ne....." tun kan ta rufe baki, Rubina tace"Hada jinin zata daina sha"? Ɗaga mata kai angel tai alamar eh, su ka ce toh zamu dinga taimakonta daga yanzu, amma itama kija mata kunne ta daina rashin jin magana, kuma ta daina yi mana gorin ƙirji," angel tace musu toh, zata ja mata kunne.
Mayar da idanuwanta ta yi akan su Danish dake atsaye, kowannan su ita ya ke kallo, ta rasa gane dililin yin tsayuwar na su akanta.
"Lafiya"? Tai tambayar tana jiran jin amsar su, kusan atare suka haÉ—a baki wurin cewa ba komai," juyawa gabriel yai tare da komawa gefen gadon shi ya zauna, shi ma danish ya koma nashi gadon ya zauna.
Duk wani motsin Gabriel Akan idon Danish, Ya hana shi sakat, Abu kamar wasa, Ko toilet Angel zata shiga sai Danish yabi bayanta, lamarin ya ɗaure mata kai, a bakin ƙopar toilet ɗin zai tsaya har saita fito sannan yaja hannunta su koma ɗaki, hakan ba ƙaramin 6ata ma Gabriel rai yai ba, shi burin shi su zauna da ita su tsara yarda zasu ɗauko ƴan uwansu, da kuma yarda zasu gudu daga Cikin kurkukun tun da yaji cewa itama tana da wannan ƙudirin aranta, Sai dai ga dukkan alamu, akwai mutun ɗaya da baison hakan ta faruwa, shiyasa ya hana shi sukuni, dama can bai yarda da Danish ba, tun zuwanshi, daga gani yana da wayau, akwai abunda yake 6oye musu, kuma yasan komai akan gidan kurkukun kallon su kawai ya ke yi.
Lokacin da dare ya yi kowannansu yai shirin kwanciya, mutun biyu ne babu alamun zasu runtsa.
Jikin Unaiza ya É—an lafa, da taimakon su azeeza taci abinci kaÉ—an, tun É—azu bacci yayi awon gaba da ita.
A tsakiyar ɗakin Gabriel ya dinga sintiri yana jiran bacci ya ɗauki Danish, Ko ya samu yaje su yi magana da Angel, amma ɗan tahalikin nan Yaƙi kwanciya, ƙarshe ma daya ga dagaske Gabriel ba bacci zaiyi ba, sai ya ɗauki pillow ɗinshi, Ya koma saman gadon Angel da ke kwance tana yin bacci, Ya ɗaura pillow ɗinsa saman mattress ɗinta, ya hau ya zauna tare da jingina bayan shi jikin pillow ɗin,' mamaki ƙarara akan fuskar gabriel, Ganin wani iko na Allah, a dole ya haƙura ya koma kan nashi gadon ya kwanta zuciyarshi acunkushe da tunani kala kala,.
Dare Ya nutsa sosai, Sunyi nisan kiwo acikin baccin su, har time ɗin Danish na zaune saman gadon angel, ahaka bacci yai awon gaba dashi, Ba zato ba tsammani, Unaiza tafarka tana ihu tana daddafe cikinta, wata irin kururuwa kamar ana zare ranta, a matuƙar firgice masu bacci suka soma farkawa Kowa Yana faman zazzare idanuwanshi, Haƙiƙa sunyi matuƙar firgita, ɗaya bayan ɗaya suka soma saukowa daga saman gadonsu suna tunkarar gadonta, mutun biyu ne basu farka ba, Jamima da majnun, kamar matattu sai sharar baccin su su ke yi, A kewaye da gadon unaiza suka tsaitsaya curko curko suna kallonta hankalin su yai matuƙar tashi, suka dinga tambayarta lafiya meke damunta, amma ta kasa buɗe baki ta basu amsa, Sai cizon la6en ta take yi, yayi suntum dashi, Angel tafi kowa shiga damuwa tsoranta, har ga Allah bata son wani abu ya samu unaiza duk da baƙin halinta tana ƙaunarta.
"Yanzu ya zamuyi da ita? Danish ba wani taimako da zaka iya yi mata? Angel ce tai maganar tana kallon shi, yae shiru bai ce mata komai ba,
Haris yace"ni fa inaga kamar kalar ciwon da su Hanna suka ta6a yi ne" gabansu ne yai wani irin mugun bugu jin abunda Haris yace, muryar deeja na arude tace"In sha Allah ba shi bane," Azeeza tuni ta fashe musu da kuka, tana zaune saman gadonta, ta kasa saukowa gudun kada ta faɗi ƙasa saboda lalurarta, tana jiyo muryoyinsu acikin kunnuwanta
Suna Cikin yin maganar nan, sautin motsin buɗe ƙopa ya karaɗe kunnuwasu, hankalin su ya ƙara tashi, nan take ransu ya basu cewa Anzo atafi da ita ne' jikin su duk yai sanyi, lokacin da su ka yi arba da Giant ɗin dake saukowa saman benan, basamudan ƙato, Mai ɗauke da star 1 agaban rigarshi, tunkan ya ƙaraso ciki, suka bashi hanya, Ya sanya hannu biyu ya ɗauki unaiza saman kafaɗarshi ya juya ya fuce da ita daga Cikin ɗakin, kamar wasu sakarkaru haka suka bi bayan shi da kallo har ya 6ace ma ganin su, Suna jiyo datse ƙopar ɗakin nasu da akayi, shi kenan an tafi da Ƴar gidan daddy, Gabriel yaso ya tambaye su ina za'a kai ta? Sai kuma ranshi ya bashi cewar wata'ƙil zasu kaita inda zasu duba lafiyarta ne, hakan yasa shi dakatawa da yin tambayar tashi, dama bai shirya yinta ba agaban Danish, don zai ƙara sa mashi ido ne.
Ba su ta6a tunanin zasu zubar mata da ƙwalla ba, saboda babu shaƙuwa atsakanin su da ita, Amma sai gashi yau saboda ita sun gaza runtsawa, a gefe da gefen gadonta matan su ka zauna shiru babu mai magana, Babu yadda haris baiyi dasu ba akan su koma su kwanta saman gadajen su, amma suka ƙiya, A ƙarshe nan suka kwana.