Sashe 99
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zama yayi sosai dan da a tsugunne yake ya ce
"Ai Umma munyi magana da ita tace kince ba sai anyi lefe ba kawai ayi mata kayan ɗaki da kuɗin". Yanda ta zaburo tace
"Inji ubanwa? Yaushe mukayi haka da ita?" Sai da abin ya bashi mamaki domin a iya saninsa da ita kullum muryarta a ƙasa take fuskarta washe da fara'a. Itan ma da sauri ta gyara zama bayan da ta fahimci abinda tayi ta shiga kame kame tana cewa
"Na rasa yaushe Zulai ta koyi magana biyu, ni bamu taɓa zancen lefe da ita ba, Mijin Nuratu dai da ya ce ko yayi mata kayan ɗaki a madadin lefen to kuma yayyina suka ce Aa ai ba'a haka, za'a mata daidai ƙarfin mu duk abinda bai masa ba daga baya ya sake mata toh ni dai iya zancen da nasan anyi kenan shine ta canza magana ashe ta gaya maka haka ni yarinyar nan ganinta nake kwana biyu ma kamar wacce iskoki suke taɓawa yanzu zata birkice ta fara masifa abunda ba halinta ba ko kuma duk zullumin auren ne ban sani ba".
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 42*
A yayinda muke shirin kammala wannan littafi idan har kin san kina karantawa ba tareda kin siya ba kiyi ƙoƙari ki sauke nauyi domin babu lallai in yafe haƙƙina 🙏🏽🙏🏽
Cike da ƙaguwa da zancen ya ce
"Yanzu dai Umma wanne ake so a ciki? Lefen ko kuma kuɗin za'a bayar ko ayi mata kayan yanda tace?"
"To ai ni ba na ce ba, kaga ita Nuratu dai kayan tace tana so to ita ya kamata ka tambaya itama kaji wanne tafi so" ta bashi amsa sai ya girgiza kai ya ce
"Ai na gaya miki yanda mukayi da ita, dama kuma ni na ɗauka ma kunyi shawarane shiyasa ban tuntuɓe ki ba dan har na bayar da aikinma, kawai ki faɗi wanda za'ayi a ciki tunda kince tariyar Nuratu nan da sati biyu kamata yayi duka a haɗa ai ba wai ayi daban daban ba"
"Toh inaga a bayar da kuɗin ko dan naji Nuratu nata ƙorafi kayan duk masu duhu aka aka saka mata inaga ya manta bai faɗawa musu haɗo kayan baƙa bace" ta faɗa tana yar dariya, wayarsa ya zaro yana cewa
"Toh idan akwai account ɗin wanda za'a turawa kuɗin a kusa a kawo idan babu kuma sai ta tura mun in fara saka mata wani abu kafin ƙarshen sati na cika dan na rigada na bayar da kuɗin kayan Wallahi yanzu kuma ko nace musu na fasa ba zasu dawowa mun da kuɗin ba sai dai na nemi wani ya siya tunda kamfani ne"
"Ai ka tura mata a Opay ɗin ta kawai tunda tareda Habiba ƙanwata zasuje kasuwar dama" cewar Umman, sai yayi murmushi yace
"Ai kuɗin da yaww Umma idan aka saka mata a opay rufewa zasuyi account ɗin nata ba zai ɗauki kuɗi da yawa ba"
"Ai kuwa yana ɗauka kwanaki can naji tace anyi buɗa mata shi har maliyoyi ma za'a iya sakawa a ciki yanzu amma bari dai tazo muji kar ayi gwari" Umman ta sake faɗa kafin ta shiga ƙwalawa Zulaiha dake laɓe tsakar gida duk tana sauraronsu kira. Sum sum ta shigo ta tsugunna daga bakin ƙofa, Umman ta ce
"Wai akawun ɗinki nace kamar naji kwanaki kince an buɗa miki shi zai iya ɗaukar kuɗi da yawa?" Da kai ta amsa ganin Bilal ɗin yana kallonta, danne danne yayi a waya ya ɗago ya cewa Umman
"Na tura da miliyan biyu, idan na samu yanda nake so zuwa ƙarshen sati zan ƙara mata miliyan ɗaya idan kuma bata samu ba zan saka ɗari biyar amma fa duka da kuɗin lefe dana sallamar amarya". Yanda kasan Umman zata kwanta tsabar murna ne ko meye oho haka ta baza hijabi ta shiga masa godiya ƙarshe ta fashe da kuka tana jera masa addu'a. Sai da ya sake ajiye mata cash na dubu ashirin daya ruƙo dama zai mata ihisani kafin suka fita tareda Zulaiha zata rakashi.
Rungumeta yayi da suka isa soro ta janye tana wani ɓata fuska, bai haƙura ba ya sake kamota yana dariya ta kuma janyewa tana cewa
"Ni dai bana so ni da kacewa yar iska daga gwada abinda aka ce idan ina maka zaka ƙara so na"
Ya ruƙo hannunta ya ce
"Banda sharri mana baby a yaushe nace miki haka? Kuma ai gaskiya aka faɗa idan kina mun hakan zan ƙara sonki kawai na jiye miki tsoro ne kar na kasa riƙe kaina na haɗa Umma da gashin amarya" ya ƙarasa yana kashe mata ido ɗaya, rufe fuska tayi da hijabinta cikin jin kunya tana dariya ya saketa yayi waje tabi bayansa, sai da suka isa gurin mota ta sake haɗe fuska. Da mamaki yace
"Wai menene haka kuma? Minti kaɗan kina fara'a anjima ki haɗe rai ko dai dagaske ne da Umma tace tana zargin iskoki suna taɓa ki?"
Baki ta tunzura tace
"Ni ba wasu iskoki kaine kayi mun laifi" sai ya tattara hankalinsa kanta ya ce
"Ni kuma? Yaushe?"
Bubbuga ƙafa ta shigayi kamar yarinya tana cewa
"Ba kaine kawai ka tashi ka haɗa kuɗin kayan lefe da na sallamar amarya ba? Yanzu wlh sai iya abinda suka ga sama suka bani ni dai da kayi shawara dani Allah ba haka za'ayi ba".
Ajiyar zuciya ya sauke dan ji yayi hankalinsa ya tashi da tace wai ya mat laifi, shi fa baya son ɓacin ranta Allah ma ya sani. Hannayenta ya kamo cikin kwantar da murya ya ce
"Shikenan kuma sai ki ɗaga mun hankali kice wai nayi miki laifi akan ɗan wannan maganar?"
"Oh yar magana ce ma a gurinka kenan?" Ta faɗa tana taɓe baki kamar me Shirin yin kuka. Zagaywa yayi da ita ya buɗe mata sit ɗin mai zaman banza kafin ya dawo ya shiga driver sit ya tayar da motar suka fita daga layin. Gadon ƙaya sukaje ya siyo mata shawarmar daya san tana so a hanya suka sasanta bayan da suka daddale akan sai dai fa ya bayar da 3M ɗin nan idan ya so ta ɗauki 500k na hidimarta dan ta san duk kashe kuɗin zasuyi ba za'a bata komai ba. Sauketa yayi ya juya yana tafe a ransa yana mamakin dama Zulaiha ta san kuɗi haka?
A sanin sa da ita ko kyautar 20k ya mata a dunƙule sai tace sunyi yawa ya rage shiyasa idan ya tashi kawai yake siya mata duk wani abu da yasan zata siya da kuɗi idan ya bata idan ta kama zai bata kuɗin kuma baya wuce 5k tunda tun tana 200L ya samar mata mai Adaidaita da yake kaita makaranta ya kuma ɗakko kuma yana saka mata Airtime da Data kusan duk sati dan haka ba wani abu zatayi da kuɗi ba amma ita ce yau suke ja'inja har tana cewa 500k ɗin ma manaji zatayi dan ba isarta zatayi ba. Kamar ya biya gidan Hajja sai kuma ya fasa dan ɗazu da safe da yaje ko arziƙin amsa sallamar sa ba tayi ba daga ƙarshe ma ɗaki ta shige ta barshi fushi take bilhaƙƙi dashi amma ya san zata sakko nan ba da daɗewa ba dan Hajjan bata iya dogon fushi dashi.
Halima ta faɗo masa a rai yayi ƙaramin tsaki a fili, idan so samu ne ta dawo kafin Zulaiha ta tare amma kuma yaga tana nema ta kawo masa wasa itama sannan ga Hajja yanda take akan tsini yanzu bata huce daga wannan fushin ba amma kuma gara tayi lokaci ɗaya ta gama a wuce gurin tunda dai gaskiya a wannan karon sai dai tayi haƙuri amma ba zai iya sakin Halima ba ya san kuma har a gurin Allah baiyi laifi ba tunda dai Haliman nan babu abinda tayi mata. Shi yanzu duk kewar yaransa ce ma take addabarsa dan tun ranar daya kaisu gidan bai sake ganinsu ba, Al'amin ma a bakin malamin makarantarsu yaji wai anzo an karɓar masa transfer sai ƙarya ya gilla masa ya ce eh ya koma can gidan kakanninsa ne da zama.
Daya isa gida falon Halima ya shiga, gurin tsaf tamkar tana ciki dan duk bayan kwana biyu sai ya share ya goge ko ina ya kuma kunna turaren wuta dake winduna a rufe suke kuma babu zurga zurga sai turaren ya sake kama gurin sosai. Ɗakinsa na nan ya shiga ya cire bedsheet ɗin kan Gadon ya canza wani dan yau ɗin kawai yaji a nan yake son kwanciya, wanka ya shiga yana Allah Allah ya fito ya kirata yana wankan yana shirya maganganun da zai faɗa mata a ransa, yana jiyo wayarsa na ƙara ya san ba zai wuce Zulaiha ce take kira ba, sai da ya gama shiryawa kafin ya ɗauki wayar ya tarar da missed calls uku na Zulaiha ɗaya sai na Jalilah guda biyu.
Murmushi yayi yabi bayan kiran Jalilan, dole ce kawai zata raba shi da ita ba dan yana so ba amma Jalilan hannunsa ce ta kowanne ɓangare kuma da ce yana da tabbacin shi kaɗai take kulawa da zai iya danne zuciyarsa ya aureta dukda ya san ba zai taɓa samun nutsuwa ba saboda kullum zuciyarsa zata ringa saƙa masa ko da auren nasa zata iya bin wani a waje amma kuma wasu ɓangarorin da yake morarta ya saka yake jin kamar zai iya haƙuri ya zauna da ita a hakan.
"Ai Umma munyi magana da ita tace kince ba sai anyi lefe ba kawai ayi mata kayan ɗaki da kuɗin". Yanda ta zaburo tace
"Inji ubanwa? Yaushe mukayi haka da ita?" Sai da abin ya bashi mamaki domin a iya saninsa da ita kullum muryarta a ƙasa take fuskarta washe da fara'a. Itan ma da sauri ta gyara zama bayan da ta fahimci abinda tayi ta shiga kame kame tana cewa
"Na rasa yaushe Zulai ta koyi magana biyu, ni bamu taɓa zancen lefe da ita ba, Mijin Nuratu dai da ya ce ko yayi mata kayan ɗaki a madadin lefen to kuma yayyina suka ce Aa ai ba'a haka, za'a mata daidai ƙarfin mu duk abinda bai masa ba daga baya ya sake mata toh ni dai iya zancen da nasan anyi kenan shine ta canza magana ashe ta gaya maka haka ni yarinyar nan ganinta nake kwana biyu ma kamar wacce iskoki suke taɓawa yanzu zata birkice ta fara masifa abunda ba halinta ba ko kuma duk zullumin auren ne ban sani ba".
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 42*
A yayinda muke shirin kammala wannan littafi idan har kin san kina karantawa ba tareda kin siya ba kiyi ƙoƙari ki sauke nauyi domin babu lallai in yafe haƙƙina 🙏🏽🙏🏽
Cike da ƙaguwa da zancen ya ce
"Yanzu dai Umma wanne ake so a ciki? Lefen ko kuma kuɗin za'a bayar ko ayi mata kayan yanda tace?"
"To ai ni ba na ce ba, kaga ita Nuratu dai kayan tace tana so to ita ya kamata ka tambaya itama kaji wanne tafi so" ta bashi amsa sai ya girgiza kai ya ce
"Ai na gaya miki yanda mukayi da ita, dama kuma ni na ɗauka ma kunyi shawarane shiyasa ban tuntuɓe ki ba dan har na bayar da aikinma, kawai ki faɗi wanda za'ayi a ciki tunda kince tariyar Nuratu nan da sati biyu kamata yayi duka a haɗa ai ba wai ayi daban daban ba"
"Toh inaga a bayar da kuɗin ko dan naji Nuratu nata ƙorafi kayan duk masu duhu aka aka saka mata inaga ya manta bai faɗawa musu haɗo kayan baƙa bace" ta faɗa tana yar dariya, wayarsa ya zaro yana cewa
"Toh idan akwai account ɗin wanda za'a turawa kuɗin a kusa a kawo idan babu kuma sai ta tura mun in fara saka mata wani abu kafin ƙarshen sati na cika dan na rigada na bayar da kuɗin kayan Wallahi yanzu kuma ko nace musu na fasa ba zasu dawowa mun da kuɗin ba sai dai na nemi wani ya siya tunda kamfani ne"
"Ai ka tura mata a Opay ɗin ta kawai tunda tareda Habiba ƙanwata zasuje kasuwar dama" cewar Umman, sai yayi murmushi yace
"Ai kuɗin da yaww Umma idan aka saka mata a opay rufewa zasuyi account ɗin nata ba zai ɗauki kuɗi da yawa ba"
"Ai kuwa yana ɗauka kwanaki can naji tace anyi buɗa mata shi har maliyoyi ma za'a iya sakawa a ciki yanzu amma bari dai tazo muji kar ayi gwari" Umman ta sake faɗa kafin ta shiga ƙwalawa Zulaiha dake laɓe tsakar gida duk tana sauraronsu kira. Sum sum ta shigo ta tsugunna daga bakin ƙofa, Umman ta ce
"Wai akawun ɗinki nace kamar naji kwanaki kince an buɗa miki shi zai iya ɗaukar kuɗi da yawa?" Da kai ta amsa ganin Bilal ɗin yana kallonta, danne danne yayi a waya ya ɗago ya cewa Umman
"Na tura da miliyan biyu, idan na samu yanda nake so zuwa ƙarshen sati zan ƙara mata miliyan ɗaya idan kuma bata samu ba zan saka ɗari biyar amma fa duka da kuɗin lefe dana sallamar amarya". Yanda kasan Umman zata kwanta tsabar murna ne ko meye oho haka ta baza hijabi ta shiga masa godiya ƙarshe ta fashe da kuka tana jera masa addu'a. Sai da ya sake ajiye mata cash na dubu ashirin daya ruƙo dama zai mata ihisani kafin suka fita tareda Zulaiha zata rakashi.
Rungumeta yayi da suka isa soro ta janye tana wani ɓata fuska, bai haƙura ba ya sake kamota yana dariya ta kuma janyewa tana cewa
"Ni dai bana so ni da kacewa yar iska daga gwada abinda aka ce idan ina maka zaka ƙara so na"
Ya ruƙo hannunta ya ce
"Banda sharri mana baby a yaushe nace miki haka? Kuma ai gaskiya aka faɗa idan kina mun hakan zan ƙara sonki kawai na jiye miki tsoro ne kar na kasa riƙe kaina na haɗa Umma da gashin amarya" ya ƙarasa yana kashe mata ido ɗaya, rufe fuska tayi da hijabinta cikin jin kunya tana dariya ya saketa yayi waje tabi bayansa, sai da suka isa gurin mota ta sake haɗe fuska. Da mamaki yace
"Wai menene haka kuma? Minti kaɗan kina fara'a anjima ki haɗe rai ko dai dagaske ne da Umma tace tana zargin iskoki suna taɓa ki?"
Baki ta tunzura tace
"Ni ba wasu iskoki kaine kayi mun laifi" sai ya tattara hankalinsa kanta ya ce
"Ni kuma? Yaushe?"
Bubbuga ƙafa ta shigayi kamar yarinya tana cewa
"Ba kaine kawai ka tashi ka haɗa kuɗin kayan lefe da na sallamar amarya ba? Yanzu wlh sai iya abinda suka ga sama suka bani ni dai da kayi shawara dani Allah ba haka za'ayi ba".
Ajiyar zuciya ya sauke dan ji yayi hankalinsa ya tashi da tace wai ya mat laifi, shi fa baya son ɓacin ranta Allah ma ya sani. Hannayenta ya kamo cikin kwantar da murya ya ce
"Shikenan kuma sai ki ɗaga mun hankali kice wai nayi miki laifi akan ɗan wannan maganar?"
"Oh yar magana ce ma a gurinka kenan?" Ta faɗa tana taɓe baki kamar me Shirin yin kuka. Zagaywa yayi da ita ya buɗe mata sit ɗin mai zaman banza kafin ya dawo ya shiga driver sit ya tayar da motar suka fita daga layin. Gadon ƙaya sukaje ya siyo mata shawarmar daya san tana so a hanya suka sasanta bayan da suka daddale akan sai dai fa ya bayar da 3M ɗin nan idan ya so ta ɗauki 500k na hidimarta dan ta san duk kashe kuɗin zasuyi ba za'a bata komai ba. Sauketa yayi ya juya yana tafe a ransa yana mamakin dama Zulaiha ta san kuɗi haka?
A sanin sa da ita ko kyautar 20k ya mata a dunƙule sai tace sunyi yawa ya rage shiyasa idan ya tashi kawai yake siya mata duk wani abu da yasan zata siya da kuɗi idan ya bata idan ta kama zai bata kuɗin kuma baya wuce 5k tunda tun tana 200L ya samar mata mai Adaidaita da yake kaita makaranta ya kuma ɗakko kuma yana saka mata Airtime da Data kusan duk sati dan haka ba wani abu zatayi da kuɗi ba amma ita ce yau suke ja'inja har tana cewa 500k ɗin ma manaji zatayi dan ba isarta zatayi ba. Kamar ya biya gidan Hajja sai kuma ya fasa dan ɗazu da safe da yaje ko arziƙin amsa sallamar sa ba tayi ba daga ƙarshe ma ɗaki ta shige ta barshi fushi take bilhaƙƙi dashi amma ya san zata sakko nan ba da daɗewa ba dan Hajjan bata iya dogon fushi dashi.
Halima ta faɗo masa a rai yayi ƙaramin tsaki a fili, idan so samu ne ta dawo kafin Zulaiha ta tare amma kuma yaga tana nema ta kawo masa wasa itama sannan ga Hajja yanda take akan tsini yanzu bata huce daga wannan fushin ba amma kuma gara tayi lokaci ɗaya ta gama a wuce gurin tunda dai gaskiya a wannan karon sai dai tayi haƙuri amma ba zai iya sakin Halima ba ya san kuma har a gurin Allah baiyi laifi ba tunda dai Haliman nan babu abinda tayi mata. Shi yanzu duk kewar yaransa ce ma take addabarsa dan tun ranar daya kaisu gidan bai sake ganinsu ba, Al'amin ma a bakin malamin makarantarsu yaji wai anzo an karɓar masa transfer sai ƙarya ya gilla masa ya ce eh ya koma can gidan kakanninsa ne da zama.
Daya isa gida falon Halima ya shiga, gurin tsaf tamkar tana ciki dan duk bayan kwana biyu sai ya share ya goge ko ina ya kuma kunna turaren wuta dake winduna a rufe suke kuma babu zurga zurga sai turaren ya sake kama gurin sosai. Ɗakinsa na nan ya shiga ya cire bedsheet ɗin kan Gadon ya canza wani dan yau ɗin kawai yaji a nan yake son kwanciya, wanka ya shiga yana Allah Allah ya fito ya kirata yana wankan yana shirya maganganun da zai faɗa mata a ransa, yana jiyo wayarsa na ƙara ya san ba zai wuce Zulaiha ce take kira ba, sai da ya gama shiryawa kafin ya ɗauki wayar ya tarar da missed calls uku na Zulaiha ɗaya sai na Jalilah guda biyu.
Murmushi yayi yabi bayan kiran Jalilan, dole ce kawai zata raba shi da ita ba dan yana so ba amma Jalilan hannunsa ce ta kowanne ɓangare kuma da ce yana da tabbacin shi kaɗai take kulawa da zai iya danne zuciyarsa ya aureta dukda ya san ba zai taɓa samun nutsuwa ba saboda kullum zuciyarsa zata ringa saƙa masa ko da auren nasa zata iya bin wani a waje amma kuma wasu ɓangarorin da yake morarta ya saka yake jin kamar zai iya haƙuri ya zauna da ita a hakan.