Sashe 36
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari cikin annashuwa da farin ciki muka fita, gidan mu ya sauke ni, a cike na tarar da gidan su Anty Labiba da sauran ƙannen Mama da suka zo yinin sallah dan tun bayan da mahaifiyar su ta rasu kasancewar Mama Fauziyya da take babbar su ba'a nan suke zaune ba se Mama ta ƙwace girma ya zama duk wani haɗuwar su a nan gidan mu sukeyi. Se yamma lis muka leƙa gidan su Bilal suna dukda ni tun azahar na zabara zan tafi Anty Mimi cousin ɗin su Mama kuma matar Uncle Mudassir ce ta hanani. A bakin get muka ci karo zata shigo ni kuma zan fita ana yayyafi dan anyi ruwa be ƙarasa ɗaukewa ba tun farko ma saukar ruwan ce ta hanani tafiya dan niyyata kamar sha ɗaya haka na tafi tunda tara bata ƙarasa bama ya kaini gida naga kuma da naje zanje ɗin babu wanda yace Aa Anty Labiba cewa ma tayi ya kamata ai dana haƙura ma da zuwa gidan yau na tafi can tunda muna da suna wai ashe baƙar magana ta faɗa mun.
"Karki kuskura ki ɗauki wannan salon gaba ya dame ki, ba'a ce kar kiyi sabga da dangin mijin ki ba amma komai ya zama da iyaka babu cusa kai babu wulaƙanci biki suna ba zancen ki tafi tun wurwuri ki zauna gara ki shiga a marmarce a gama ki kama gabanki da kina da yara ne ma wannan tun safe kya iya turasu su shiga cikin yan uwansu idan yaso kya je daga baya amma gari ko gama tsanewa beyi ba kin zari mayafi zaki tafi kyaje ki rasa gurin zama yanda baki da aikin nan se kwanciya".
Ɗaki na shige jin sun mun caa ashe wai duk shiru kawai sukayi kowa da magana a bakin ta. Ni dai na kasa nutsuwa gani nake ban kyauta ba ace ana sunan ƙanwar miji na a matsayi na na matar wanta da suka ɗaki ɗaya nasan yanzu duk faccaloli na wanda mazajen su suka haɗa uba da su Bilal ai sunje se ni kaɗai ce bazanje da wuri ba. Haushin dalilin daya sa ban fara tsayawa acan ba naji yanda kasan wadda tayi laifi haka na kasa tsaye na kasa zaune daga ƙarshe ban wa kowa sallama ba na bi ta ƙofar kitchen na fice surutu ne dai zasuyi su gama kuma duk da zasu ce kar naje naga kowa idan sabgar dangin mijin ta ya tashi sune a gaba har ma su gayya ce mu shine ne za'a koya mun na wulaƙan ta nawa na kuma kashe wayata dan karma su kira ni.
Aiko abin da na guda ina zuwa yan gidan su Bilal suka mun caaa wai se yanzu harda Hajjan kuwa da yan uwanta, abin takaici gurin zama me kyau ma na rada duk da gidan ba'a cike yake ba iya su ne yan ɗakin su se yan uwan Hajjan da yayan su ko waɗan da suke uba ɗayan mutum ɗaya na gani Farisa sauran sun ce ruwa ya hana su fito. Haka na ringa raɓe raɓe daga wannan bangon zuwa wancan ga babu fuska hatta mejegon wani gani gani naga ta mun ba abun na koma gida ba na tarar da surutan su Anty Labiba a daddafe na jira akayi la'asar suma ban musu sallama ba na kama hanyar gida na.
Daga yanayin yanda Bilal ya shigo gidan na gane ba lafiya ba, be dai ce mun komai ba har na dafa masa Indomin daya buƙata. Ina shafa mai bayan na fito daga wanka ya shigo ɗakin ya zauna kan bedside drawer yana kallo na yace
"Ƙarfe nawa kika je gidan sunan ne?"
Se naji gaba na ya faɗi dukda cikin sanyi yayi maganar, a hankali ni ma nace
"Kasan anyi ruwa ga zazzaɓi kuma a jiki na se da akayi sallar azahar ruwan ya tsaya sannan na tafi". Kai ya gyaɗa kawai jin yayi shiru se na cigaba da shiri na ina satar kallon sa, har na kammala na shimfiɗa sallaya zanyi shafa'i da wutri ya sake cewa
"Ke kaɗai kika je kenan?"
"Eh ni kaɗai na tafi, sun ce na jira mu tafi naga lokaci na ƙurewa shine na tafi"
"Hajja tayi zaton tare zaku je da su Mama ai ta zaunar da mutane akan su gaisa kuma basu je ba shine wai taji babu daɗi" ya sake faɗa. Yanayin yanda yake maganar se naga kamar yana so yayi faɗa ne se dai kuma rashin hujja ko dalilin yin faɗan yasa yake fadar maganganun a sanyaye. Ban bashi amsa ba na tayar da sallaha ta dan jikina duk ciwo yake mun dan ma nayi wanka, washe gari da la'asar salaliya kuwa se ga Farisa dake akwai ƙanwar mijinta bayan layin mu itama ta haihu yau ne sunan shine ta ratso.
"Ai in gaya miki jiya karki so kiga tijarar da Hajja ta dasa a gida mara dalili. Bafa ayi girki ba banda na safe har se sanda kika zo ɗin nan fa kikaga ana kiciniyar ɗorawa ga guri ya jiƙe ni dai ana kiran sallar magriba na tafi lokacin abinci ya sauka jama'a dai sunyi wunin yunwa a gidan suna".
Farisa data gama kora zoɓo me sanyi ta faɗa. Ƙanwar Bilal ce da suke una ɗaya ita kaɗai mamanta ta haifa a gidan dan haka ta zama bakin ganga bata ɓangaren su Bilal ɗin bata gefen yan ɗaya ɗakin. Tana da kirki matsalar ta na lura ta fiya gulma da tsegumi ta ɗakko zancen wancan ta kai can aikin ta kenan.
Tun aure na da Bilal take so mu ƙulla mu'amala da na fara sake mata dana fuskanci halin ta se na janye ko a whatsapp ta mun magana se na ja kwanaki ban amsa ba dukda haka bata haƙura duk sanda tazo gidan ƙanwar mijin ta dana fahimci suna shiri se ta ratso ko ita ƙanwar mijin nata ma taso ta haɗa mu zuwan ta uku ban je mata ko sau ɗaya ba dake me hankali ce se ta janye ta rabu da ni.
Shiru nayi ban tanka mata ba ta sake cewa
"Ban da son zuciya dai irin na Babar mu, ashe ke ake ta jira zaku kawo abinci, kin san haihuwar ƙarshe da Ummi tayi bikin ku saura sati biyu Anty Murya Amaryar Yaya Khamis ce ta ɗauki nauyin abincin da aka ci a gidan sunan nan se kinga abu, shine suka saka rai kema zaku musu haka. Se gashi da kika tashi zuwa sungup ance ko abin barka baki bayar ba. Ni dai nace ko ita Ummin da kuɗin Yayanta aka mata ba wai a aljihun ta ita Anty Murjar ta zare tayi ba wlh. Haka dai aka watsa taro yan fadar Hajja marasa tsoron Allah sun tafi dake a baki har ana cewa arziƙi beyi rana ba wai ana wa Yaya Bilal murna ua samo yar masu hannu da shuni ashe duk ƙaryar banza ce babu abin".
[1/16, 11:08 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 16*
*Nayi kuskuren rubutu a page 13, ajizanci ne, abinda ke raina daban abinda alƙalamina ya rubuta daban. Ina fatan zaku mun uzuri*
Na ringa juya zancen Farisa a raina bayan ta tafi har sanda Bilal ya dawo sau biyu ina buɗe baki da niyyar tambayar sa gaskiyar abin da ta faɗa mun se na kasa daga ƙarshe na tattara zancen na watsar har ina ganin baike na dana yarda da maganar tata har na saka a raina. Ta ya ma haka zata yuwu? Kawai dai haɗa guri ne irin na Farisa amma kuma idan tayi ƙarya ta ƙulla abu mara daɗi tsakani na da dangin Bilal ribar me zata ci?
Ganin ba ni da wani takamaiman wanda zan tambaya na ji gargar ɗin maganar yasa na barta a bata faru ba naci gaba da sabgogina.
An gama bikin sallah ta wuce ta bar wawa da bashi kamar yanda hausawa suke faɗa, ranar data kama kwana bakwai dai dai da yin sallah tun da safe Bilal yace mun zamu fita da yamma. Yanda yake ta zirgilli da rawar ƙafa akan fitar yasa na ringa mamakin in da zamuje dan be gaya mun ba. Ana la'asar ya shiga azazzalata da na shirya mu tafi ni kuma gaba ɗaya naji jiki na ya mun nauyi, ina ta so na koma asibiti ma amma shauni da shiririta ya hanani. Haka dai na ƙoƙarta na shirya, atamfa na saka Holland riga da zani dan kayana sun fara matse ni da alama dai cikin kiɓa ze saka ni, ina tsaka da ɗaura ɗankwali na ya shiga ɗakin yanda kasan me shirin tafiya dinner haka ya sha kwalliya da sabuwar shadda cream color se ƙyalli take yi.
Kallon sa na ringa yi kamar yanda shima yake kallona hanci a ɗage kafin cikin faɗa faɗa yace
"Meye Halims? Wane irin kaya ne wannan kika saka kamar wadda zata je cin kasuwar ƙauye?"
"Karki kuskura ki ɗauki wannan salon gaba ya dame ki, ba'a ce kar kiyi sabga da dangin mijin ki ba amma komai ya zama da iyaka babu cusa kai babu wulaƙanci biki suna ba zancen ki tafi tun wurwuri ki zauna gara ki shiga a marmarce a gama ki kama gabanki da kina da yara ne ma wannan tun safe kya iya turasu su shiga cikin yan uwansu idan yaso kya je daga baya amma gari ko gama tsanewa beyi ba kin zari mayafi zaki tafi kyaje ki rasa gurin zama yanda baki da aikin nan se kwanciya".
Ɗaki na shige jin sun mun caa ashe wai duk shiru kawai sukayi kowa da magana a bakin ta. Ni dai na kasa nutsuwa gani nake ban kyauta ba ace ana sunan ƙanwar miji na a matsayi na na matar wanta da suka ɗaki ɗaya nasan yanzu duk faccaloli na wanda mazajen su suka haɗa uba da su Bilal ai sunje se ni kaɗai ce bazanje da wuri ba. Haushin dalilin daya sa ban fara tsayawa acan ba naji yanda kasan wadda tayi laifi haka na kasa tsaye na kasa zaune daga ƙarshe ban wa kowa sallama ba na bi ta ƙofar kitchen na fice surutu ne dai zasuyi su gama kuma duk da zasu ce kar naje naga kowa idan sabgar dangin mijin ta ya tashi sune a gaba har ma su gayya ce mu shine ne za'a koya mun na wulaƙan ta nawa na kuma kashe wayata dan karma su kira ni.
Aiko abin da na guda ina zuwa yan gidan su Bilal suka mun caaa wai se yanzu harda Hajjan kuwa da yan uwanta, abin takaici gurin zama me kyau ma na rada duk da gidan ba'a cike yake ba iya su ne yan ɗakin su se yan uwan Hajjan da yayan su ko waɗan da suke uba ɗayan mutum ɗaya na gani Farisa sauran sun ce ruwa ya hana su fito. Haka na ringa raɓe raɓe daga wannan bangon zuwa wancan ga babu fuska hatta mejegon wani gani gani naga ta mun ba abun na koma gida ba na tarar da surutan su Anty Labiba a daddafe na jira akayi la'asar suma ban musu sallama ba na kama hanyar gida na.
Daga yanayin yanda Bilal ya shigo gidan na gane ba lafiya ba, be dai ce mun komai ba har na dafa masa Indomin daya buƙata. Ina shafa mai bayan na fito daga wanka ya shigo ɗakin ya zauna kan bedside drawer yana kallo na yace
"Ƙarfe nawa kika je gidan sunan ne?"
Se naji gaba na ya faɗi dukda cikin sanyi yayi maganar, a hankali ni ma nace
"Kasan anyi ruwa ga zazzaɓi kuma a jiki na se da akayi sallar azahar ruwan ya tsaya sannan na tafi". Kai ya gyaɗa kawai jin yayi shiru se na cigaba da shiri na ina satar kallon sa, har na kammala na shimfiɗa sallaya zanyi shafa'i da wutri ya sake cewa
"Ke kaɗai kika je kenan?"
"Eh ni kaɗai na tafi, sun ce na jira mu tafi naga lokaci na ƙurewa shine na tafi"
"Hajja tayi zaton tare zaku je da su Mama ai ta zaunar da mutane akan su gaisa kuma basu je ba shine wai taji babu daɗi" ya sake faɗa. Yanayin yanda yake maganar se naga kamar yana so yayi faɗa ne se dai kuma rashin hujja ko dalilin yin faɗan yasa yake fadar maganganun a sanyaye. Ban bashi amsa ba na tayar da sallaha ta dan jikina duk ciwo yake mun dan ma nayi wanka, washe gari da la'asar salaliya kuwa se ga Farisa dake akwai ƙanwar mijinta bayan layin mu itama ta haihu yau ne sunan shine ta ratso.
"Ai in gaya miki jiya karki so kiga tijarar da Hajja ta dasa a gida mara dalili. Bafa ayi girki ba banda na safe har se sanda kika zo ɗin nan fa kikaga ana kiciniyar ɗorawa ga guri ya jiƙe ni dai ana kiran sallar magriba na tafi lokacin abinci ya sauka jama'a dai sunyi wunin yunwa a gidan suna".
Farisa data gama kora zoɓo me sanyi ta faɗa. Ƙanwar Bilal ce da suke una ɗaya ita kaɗai mamanta ta haifa a gidan dan haka ta zama bakin ganga bata ɓangaren su Bilal ɗin bata gefen yan ɗaya ɗakin. Tana da kirki matsalar ta na lura ta fiya gulma da tsegumi ta ɗakko zancen wancan ta kai can aikin ta kenan.
Tun aure na da Bilal take so mu ƙulla mu'amala da na fara sake mata dana fuskanci halin ta se na janye ko a whatsapp ta mun magana se na ja kwanaki ban amsa ba dukda haka bata haƙura duk sanda tazo gidan ƙanwar mijin ta dana fahimci suna shiri se ta ratso ko ita ƙanwar mijin nata ma taso ta haɗa mu zuwan ta uku ban je mata ko sau ɗaya ba dake me hankali ce se ta janye ta rabu da ni.
Shiru nayi ban tanka mata ba ta sake cewa
"Ban da son zuciya dai irin na Babar mu, ashe ke ake ta jira zaku kawo abinci, kin san haihuwar ƙarshe da Ummi tayi bikin ku saura sati biyu Anty Murya Amaryar Yaya Khamis ce ta ɗauki nauyin abincin da aka ci a gidan sunan nan se kinga abu, shine suka saka rai kema zaku musu haka. Se gashi da kika tashi zuwa sungup ance ko abin barka baki bayar ba. Ni dai nace ko ita Ummin da kuɗin Yayanta aka mata ba wai a aljihun ta ita Anty Murjar ta zare tayi ba wlh. Haka dai aka watsa taro yan fadar Hajja marasa tsoron Allah sun tafi dake a baki har ana cewa arziƙi beyi rana ba wai ana wa Yaya Bilal murna ua samo yar masu hannu da shuni ashe duk ƙaryar banza ce babu abin".
[1/16, 11:08 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 16*
*Nayi kuskuren rubutu a page 13, ajizanci ne, abinda ke raina daban abinda alƙalamina ya rubuta daban. Ina fatan zaku mun uzuri*
Na ringa juya zancen Farisa a raina bayan ta tafi har sanda Bilal ya dawo sau biyu ina buɗe baki da niyyar tambayar sa gaskiyar abin da ta faɗa mun se na kasa daga ƙarshe na tattara zancen na watsar har ina ganin baike na dana yarda da maganar tata har na saka a raina. Ta ya ma haka zata yuwu? Kawai dai haɗa guri ne irin na Farisa amma kuma idan tayi ƙarya ta ƙulla abu mara daɗi tsakani na da dangin Bilal ribar me zata ci?
Ganin ba ni da wani takamaiman wanda zan tambaya na ji gargar ɗin maganar yasa na barta a bata faru ba naci gaba da sabgogina.
An gama bikin sallah ta wuce ta bar wawa da bashi kamar yanda hausawa suke faɗa, ranar data kama kwana bakwai dai dai da yin sallah tun da safe Bilal yace mun zamu fita da yamma. Yanda yake ta zirgilli da rawar ƙafa akan fitar yasa na ringa mamakin in da zamuje dan be gaya mun ba. Ana la'asar ya shiga azazzalata da na shirya mu tafi ni kuma gaba ɗaya naji jiki na ya mun nauyi, ina ta so na koma asibiti ma amma shauni da shiririta ya hanani. Haka dai na ƙoƙarta na shirya, atamfa na saka Holland riga da zani dan kayana sun fara matse ni da alama dai cikin kiɓa ze saka ni, ina tsaka da ɗaura ɗankwali na ya shiga ɗakin yanda kasan me shirin tafiya dinner haka ya sha kwalliya da sabuwar shadda cream color se ƙyalli take yi.
Kallon sa na ringa yi kamar yanda shima yake kallona hanci a ɗage kafin cikin faɗa faɗa yace
"Meye Halims? Wane irin kaya ne wannan kika saka kamar wadda zata je cin kasuwar ƙauye?"