Sashe 58
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To dai ko bamu da dangi daga ni har Bilal ɗin ace yau ana suna a gidan mu ya ci a ce mun tattaro maƙwafta sun rufa mana asiri balle daga ni har shi babu wanda za'a yiwa gorin yawan zuri'a amma ace ko ƙuda babu da sunan ya zo taya mu murna. Muryar Baba Jummai da na ji ta sa na shiga share hawayen da suka fara saukar mun da sauri, ta wuce ni, tukunyar da ke kan gas ta buɗe bayan ta ɗebo kwanuka ta shiga zuba miya, na ringa kallon ta da mamaki ita dai bata ko kalle ni ba har ta gama zuba miyar ta jera a try ta fita da su kafin ta dawo ta zuba tuwo shima ta haɗa da ruwa ta fitar musu da shi. Tabbas da na farka na ji gidan na ƙamshin miya amma ban gasgata ba. Bayan tafiyar su Maman Yusuf dan basu ci tuwon ba juye musu tayi suka tafi da shi ta ce na lissafa mata gidajen da za'a aika da tuwon. Baki na kamar ze tsage dan farin ciki na ce
"Baba yaushe kika yi tuwon nan?"
"Ba dai ke sakarya ba ce a garin ki rufawa miji asiri zaki tonawa kanki asiri banda haka a ina kika taɓa ganin irin wannan rashin lissafin na ki? Yanzu ba dan nayi dabarar tashi da duku duku na yi tuwon nan ba yanda mutanen nan suka shigo da me zasu fita su bada labari? Dama salin alin da an gama kai abincin nan ki saka kayanki da na yaron nan a yar jaka mu tafi can gidan in ya so ma dawo da dare dan ni dai tunda uwata ta haife ni ban taɓa ganin irin wannan kalan tsiya ba.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 24*
A ƙaramar akwati na zuba mana duk abun da na san zamu buƙata a yinin, Baba Jummai ta goya Al'amin tana tsaye tana jiran na yafa gyale na da na ajiye a gefe. Zama na yi a gefen gado ina rarraba ido kamar wadda ta yiwa sarki ƙarya, ta kalle ni ta ce
"Ya kuma kika zauna? Tun da dai an kaiwa maƙwaftan nan abinci se ki tashi mu tafi kuma su ce zasu shigo yinin suna".
"Baba ban gayawa Bilal ba" na faɗa ba tare da na kalle ta ba,
"Naga abinda ya ishe ni ni Hasana, yanzu gidan ku ɗin da zaki tafi shine kike cewa baki gaya masa ba? Me ze miki? Naga tun farar asuba ya fice ya bar miki gidan gashi har sha biyu ta taho ko ɗan tsako be leƙo gidan nan daga dangin sa ba, kar kiyi ta kanki kin ji. Ni dai idan ma ba zaki tafi ba se in yi gaba abu na in ya so ki saka ce gidan duk bugun da za'a yi karki buɗe tun da dai baki da abun bawa ma su shigo mikin" Cewar Baba Jummai. Se na miƙe na yafa mayafin jiki a sanyaye, ta nufi ƙofa tana cewa
"Jira na taro mana ɗan sahu ba ma fita haka da akwati ana kallon mu ba" ta fita. Komawa na yi na zauna na yi tagumi hannu biyu, ko a waya ba wanda ya kira ni se kace wata mara galihu. Tunanin in da Bilal ya tafi na shiga yi, gashi ba waya a hannun sa balle na kira shi kuma gaskiya zan so na tafi can gidan nima tun da zamana a nan dai a yau ba shi da wani amfani. Muryar Baba Jummai da na jiyo da wani da ban gane ko waye ba ya sa na fita tsakar gida na tarar da ita tare da Abubakar da Saleh suna ƙoƙarin saƙale Rago a jikin window ɗakin tsakar gida.
"Yanzu da ze yi yankan tun farar safiya ba'a yi ba se yanzu da rana ta take?" Na jiyo ta tana faɗa, su dai ba su tanka mata ba suka gama ɗaure shi kafin suka shigo falon muka gaisa a tsatstsaye suka wuce. A falon na zauna Baba Jummai kuma ta kwance Al'amin ta hau aikin gyara kayan ciki tana yi tana mita duk ta cika mun kunne se kawai na koma cikin ɗaki na rufo ƙofa ta. Har bacci ya fara ɗiba na sama sama hayaniya ta tashe ni, kamar na doka tsallen murna ganin su Amal da sauran cousins ɗina kusan su goma. Zuwan su ya wartsakar da ni musamman da na gansu da tulin ruwa da lemo katan katan ga wasu kuloli da suka ce saƙon Anty Labiba ne ta ce kar wanda ya taɓa se ta zo. Zuwa la'asar gida ya gama cika taf da dangi na kusa da na nesa ana ta harkokin arziƙi har sannan kuma yan cikin gidan su Bilal babu wanda ya zo.
Babu ce kawai Anty Labiba bata dafo ta kawo ba tun daga kan abinci zuwa snacks da abubuwan sha iri iri. Nan gurin dining ɗina ta sa aka tura shi gefe ta zuba kayan suka ringa serving, daga yanda taƙi matsawa ko nan da can daga kan abincin na fahimci ta shirya wani abu shi yasa har zuciya ta nayi farin ciki da rashin zuwan dangin Bilal dan dai na san koma menene saboda su ne. Biyar da wani abu na shiga canza kaya saboda me ɗaukar hoto da ya zo se ga yan gudan su Bilal zuga guda yan ɗakin su da kuma yan uwan Hajja babu dai dangin Baban su ko ɗaya ko matan yayyen sa a ciki.
Dama tun da Khausar ƙanwar Mijin Fainusa ta zo take tambayar bata ƙaraso ba ne na ce mata eh bata zauna ba kuma ta tafi dama jiki na ya bani sai ta kira Fainusan ilai kuwa se gasu manya da yara Anty Amina ce kawai babu.
Falo na suka fara shiga suka gaisa da yan uwana da ke zaune kafin Fadila da Fainusa suka iske ni ɗaki, Fadilan ta ce na basu key ɗin can falon Bilal tun da nan ɗin ya cika da mutane. Ban musa ba na ɗauka na bata dan zan fi so su ware gefen.
A can na same su muka gaisa mai hoton ya fara shiga can muka yi hotunan kafin na dawo tsakar gida muka cigaba. Na ɗauka za'a samu wanda zai yi tunanin basu abinci shi yasa na cigaba da sabgogina, Ummi yar Anty Sauda yayar su ta biyu tazo tayi kira na wai inji Maman su. Na tarar da su kowacce fuska a ɗaure kamar zasu rufe ni da duka. A gadarance ta ce mun
"Da alama kin manta muna zaune a nan ko Halima?"
Duk da na fahimci in da maganar ta ta dosa dan banga ko ledar ruwa an ajiye musu ba amma na ce mata
"Na san kuna nan mana Anty"
"Iskanci ne wato ya saka aka barmu a gantale ko kuwa jira ake mu fito mu ɗibi abincin da kanmu?" Anty Hauwa, ƙanwa ce gurin Hajja abokanan wasa suke ta faɗa. Se na miƙe ina cewa
"Kuyi haƙuri, ina ga sun shafa'a ne bari na je na musu magana, yanzu za'a kawo muku" na fita daga falon ina ji suna bi na da ƙananun maganganu. Rasa ta yanda zan tunkari Anty Labiba na yi dan haka na ja Amal gefe na ce ta ɗauki manyan kuloli a kitchen ta zuzzuba abinci idan Anty Labiba ta tambaye ta ta ce ƙawaye na da zasu zo an jima za'a ajiyewa se ta kai mun ɗakin Bilal ta ajiye. Shiru shiru kusan minti goma sai gata, da sauri na tare ta ina tambayar ina abincin ta ce mun Anty Labiban ta ce ba ze ƙare ba duk wanda ze zo ma ze samu. Ban ji daɗi ba, na ringa jele tsakanin falon da ɗaki amma na kasa yi mata magana. Bana so na yiwa wani babba maganar ta ce na kai ƙarar ta ko wani abu amma kuma a take taken ta naga alamar ta shirya yi musu wulaƙanci ne kawai tun da ai taga zuwan su har gaisawa suka yi kuma ita idan ta haihu naga ai tun ma kafin a fara rabawa mutane abinci take ware na dangin mijin ta.
Hansa'u na jawo akan ta yiwa Anty Labiban magana ta ce wlh babu ruwanta. Na kasa tsaye na kasa zaune ga Ummi tsaye bakin ƙofa na san kuma ba ze wuce sake aiko ta akayi karɓar abincin ba kuma tana ji Anty Labiban na yekuwar idan da me buƙatar ƙarin wani abu ya zo ya karɓa, ina kallo ta jinjina kai irin zata je ta kai rahoto ta juya se kawai na yanke shawarar yin shahada na mata magana. Ina matsawa gurin na jiyo Mama Sa'a matar kawun su Mama tana tambayar ta an kai wa dangin miji na abinci kuwa?
Anty Labiban ta ce
"Aa ba'a kai musu ba, na manta". Na sauke ajiyar zuciya a filiz na san ba ƙaramin mutunchin Mama Sa'ar take gani ba da har ta bata amsa me daɗi haka, ina ji ta wuce tana ce mata
"Baba yaushe kika yi tuwon nan?"
"Ba dai ke sakarya ba ce a garin ki rufawa miji asiri zaki tonawa kanki asiri banda haka a ina kika taɓa ganin irin wannan rashin lissafin na ki? Yanzu ba dan nayi dabarar tashi da duku duku na yi tuwon nan ba yanda mutanen nan suka shigo da me zasu fita su bada labari? Dama salin alin da an gama kai abincin nan ki saka kayanki da na yaron nan a yar jaka mu tafi can gidan in ya so ma dawo da dare dan ni dai tunda uwata ta haife ni ban taɓa ganin irin wannan kalan tsiya ba.
[4/4, 6:37 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 24*
A ƙaramar akwati na zuba mana duk abun da na san zamu buƙata a yinin, Baba Jummai ta goya Al'amin tana tsaye tana jiran na yafa gyale na da na ajiye a gefe. Zama na yi a gefen gado ina rarraba ido kamar wadda ta yiwa sarki ƙarya, ta kalle ni ta ce
"Ya kuma kika zauna? Tun da dai an kaiwa maƙwaftan nan abinci se ki tashi mu tafi kuma su ce zasu shigo yinin suna".
"Baba ban gayawa Bilal ba" na faɗa ba tare da na kalle ta ba,
"Naga abinda ya ishe ni ni Hasana, yanzu gidan ku ɗin da zaki tafi shine kike cewa baki gaya masa ba? Me ze miki? Naga tun farar asuba ya fice ya bar miki gidan gashi har sha biyu ta taho ko ɗan tsako be leƙo gidan nan daga dangin sa ba, kar kiyi ta kanki kin ji. Ni dai idan ma ba zaki tafi ba se in yi gaba abu na in ya so ki saka ce gidan duk bugun da za'a yi karki buɗe tun da dai baki da abun bawa ma su shigo mikin" Cewar Baba Jummai. Se na miƙe na yafa mayafin jiki a sanyaye, ta nufi ƙofa tana cewa
"Jira na taro mana ɗan sahu ba ma fita haka da akwati ana kallon mu ba" ta fita. Komawa na yi na zauna na yi tagumi hannu biyu, ko a waya ba wanda ya kira ni se kace wata mara galihu. Tunanin in da Bilal ya tafi na shiga yi, gashi ba waya a hannun sa balle na kira shi kuma gaskiya zan so na tafi can gidan nima tun da zamana a nan dai a yau ba shi da wani amfani. Muryar Baba Jummai da na jiyo da wani da ban gane ko waye ba ya sa na fita tsakar gida na tarar da ita tare da Abubakar da Saleh suna ƙoƙarin saƙale Rago a jikin window ɗakin tsakar gida.
"Yanzu da ze yi yankan tun farar safiya ba'a yi ba se yanzu da rana ta take?" Na jiyo ta tana faɗa, su dai ba su tanka mata ba suka gama ɗaure shi kafin suka shigo falon muka gaisa a tsatstsaye suka wuce. A falon na zauna Baba Jummai kuma ta kwance Al'amin ta hau aikin gyara kayan ciki tana yi tana mita duk ta cika mun kunne se kawai na koma cikin ɗaki na rufo ƙofa ta. Har bacci ya fara ɗiba na sama sama hayaniya ta tashe ni, kamar na doka tsallen murna ganin su Amal da sauran cousins ɗina kusan su goma. Zuwan su ya wartsakar da ni musamman da na gansu da tulin ruwa da lemo katan katan ga wasu kuloli da suka ce saƙon Anty Labiba ne ta ce kar wanda ya taɓa se ta zo. Zuwa la'asar gida ya gama cika taf da dangi na kusa da na nesa ana ta harkokin arziƙi har sannan kuma yan cikin gidan su Bilal babu wanda ya zo.
Babu ce kawai Anty Labiba bata dafo ta kawo ba tun daga kan abinci zuwa snacks da abubuwan sha iri iri. Nan gurin dining ɗina ta sa aka tura shi gefe ta zuba kayan suka ringa serving, daga yanda taƙi matsawa ko nan da can daga kan abincin na fahimci ta shirya wani abu shi yasa har zuciya ta nayi farin ciki da rashin zuwan dangin Bilal dan dai na san koma menene saboda su ne. Biyar da wani abu na shiga canza kaya saboda me ɗaukar hoto da ya zo se ga yan gudan su Bilal zuga guda yan ɗakin su da kuma yan uwan Hajja babu dai dangin Baban su ko ɗaya ko matan yayyen sa a ciki.
Dama tun da Khausar ƙanwar Mijin Fainusa ta zo take tambayar bata ƙaraso ba ne na ce mata eh bata zauna ba kuma ta tafi dama jiki na ya bani sai ta kira Fainusan ilai kuwa se gasu manya da yara Anty Amina ce kawai babu.
Falo na suka fara shiga suka gaisa da yan uwana da ke zaune kafin Fadila da Fainusa suka iske ni ɗaki, Fadilan ta ce na basu key ɗin can falon Bilal tun da nan ɗin ya cika da mutane. Ban musa ba na ɗauka na bata dan zan fi so su ware gefen.
A can na same su muka gaisa mai hoton ya fara shiga can muka yi hotunan kafin na dawo tsakar gida muka cigaba. Na ɗauka za'a samu wanda zai yi tunanin basu abinci shi yasa na cigaba da sabgogina, Ummi yar Anty Sauda yayar su ta biyu tazo tayi kira na wai inji Maman su. Na tarar da su kowacce fuska a ɗaure kamar zasu rufe ni da duka. A gadarance ta ce mun
"Da alama kin manta muna zaune a nan ko Halima?"
Duk da na fahimci in da maganar ta ta dosa dan banga ko ledar ruwa an ajiye musu ba amma na ce mata
"Na san kuna nan mana Anty"
"Iskanci ne wato ya saka aka barmu a gantale ko kuwa jira ake mu fito mu ɗibi abincin da kanmu?" Anty Hauwa, ƙanwa ce gurin Hajja abokanan wasa suke ta faɗa. Se na miƙe ina cewa
"Kuyi haƙuri, ina ga sun shafa'a ne bari na je na musu magana, yanzu za'a kawo muku" na fita daga falon ina ji suna bi na da ƙananun maganganu. Rasa ta yanda zan tunkari Anty Labiba na yi dan haka na ja Amal gefe na ce ta ɗauki manyan kuloli a kitchen ta zuzzuba abinci idan Anty Labiba ta tambaye ta ta ce ƙawaye na da zasu zo an jima za'a ajiyewa se ta kai mun ɗakin Bilal ta ajiye. Shiru shiru kusan minti goma sai gata, da sauri na tare ta ina tambayar ina abincin ta ce mun Anty Labiban ta ce ba ze ƙare ba duk wanda ze zo ma ze samu. Ban ji daɗi ba, na ringa jele tsakanin falon da ɗaki amma na kasa yi mata magana. Bana so na yiwa wani babba maganar ta ce na kai ƙarar ta ko wani abu amma kuma a take taken ta naga alamar ta shirya yi musu wulaƙanci ne kawai tun da ai taga zuwan su har gaisawa suka yi kuma ita idan ta haihu naga ai tun ma kafin a fara rabawa mutane abinci take ware na dangin mijin ta.
Hansa'u na jawo akan ta yiwa Anty Labiban magana ta ce wlh babu ruwanta. Na kasa tsaye na kasa zaune ga Ummi tsaye bakin ƙofa na san kuma ba ze wuce sake aiko ta akayi karɓar abincin ba kuma tana ji Anty Labiban na yekuwar idan da me buƙatar ƙarin wani abu ya zo ya karɓa, ina kallo ta jinjina kai irin zata je ta kai rahoto ta juya se kawai na yanke shawarar yin shahada na mata magana. Ina matsawa gurin na jiyo Mama Sa'a matar kawun su Mama tana tambayar ta an kai wa dangin miji na abinci kuwa?
Anty Labiban ta ce
"Aa ba'a kai musu ba, na manta". Na sauke ajiyar zuciya a filiz na san ba ƙaramin mutunchin Mama Sa'ar take gani ba da har ta bata amsa me daɗi haka, ina ji ta wuce tana ce mata