Sashe 18
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganin kusan minti talatin shiru Anty Labiba bata leƙo ta kira shi ba ya fara tunanin ko bacci Haliman ta koma dan yana da yaƙinin ido biyu ba zata gaza neman sa ba tun da tasan yana gurin, tashi yayi yana ƙarfafawa kansa guiwa akan ko me Anty Labiba zata faɗa se ya koma ɗakin, yana kai hannu ze buɗe ƙofar ta fito, kallo me kama da harara ta masa haɗi da yin tsaki ta raɓa shi ta wuce se yaji ransa ya ɓaci. Ta girme shi kuma ƙanwar mahaifiyar Halima ce amma kuma hakan ba shi yake nufin zata ringa wulaƙanta shi kamar wani wanda yazo mata maula ba. Shi badan Halima ba me ma ze haɗa shi da ita har ta ringa wulaƙanta shi haka?
Fuska babu walwala ya shiga ɗakin, na ɗaga kai da sauri jin an buɗe ƙofa muka haɗa ido ban san sanda na miƙe ina sakin murmushi ba ya nufo ni shima yana murmushi yace
"Kin tayar mun da Hankali Halims, me yasa?"
"Sau ke gani na nayi ƙasa ina wasa da gefen hijabi na ba tare da nace masa komai ba, ganin sa ya bani nutsuwar zuciya ya kuma tabbatar mun yana tare dani ma'ana ya janye waɗan can kalaman marasa daɗi daya faɗa mun jiya wai mu haƙura da juna.
"Ki zauna kar ƙafafun ki su gaji" ya faɗa yana kallo na se na ƙarasa na zauna akan gado har sannan murmushi be bar kan fuskata ba, ya matso da kujera kusa da ni ya zauna yana leƙa fuskata yace
"Ashe haka kike so na ban sani ba Halims?"
Harar wasa na masa ba tare da nace komai ba, ya sake gyara kijerar da yake a kai ya langwaɓar da kai yana kallo na yace
"Ko da nace mu haƙura ƙarya nake yi ni da kaina nasan bazan iya jure rashin ki a tare da ni ba. Tun da kika tafi ni kaina dauriya ce kawai irin ta maza ta sa ba'a kawo ni an kwantar a gadon Asibiti ba mutuwa ce kaɗai zata iya raba ni dake Halims amma muddin ina raye dole zan nemo mafita, ki taya ni da addu'a Allah ya hore mun na fita kunyar ki kafin ranar auren mu albarkacin wannan son da kike mun bazan baki kunya ba".
Bude ƙofar da aka yi ya saka yaja baya daga gare ni muka kalli ƙofar a tare, Abba ne ya shigo tare da Uncle Mudassir Autan su Mamanmu. Cikin jin kunya Bilal ya miƙe daga kujerar da yake zaune yana musu sannu da zuwa, fuskar Abba babu yabo babu fallasa ya nufo in da nake se Uncle Mudassir ne ya amsa masa kafin shima ya matso yana mun murmushi na gaishe su ya shiga tambayar jiki na sannan ya ɗauki folder dake kan bedside ya shiga dubawa dake shima likita ne.
"Dr yace zuwa yamma zasu sallame ki tun da babu wani abu ko akwai in da yake yi miki ciwo ne yanzun?" Abba ya tambaye ni, se na shafa ciki na da naji yayi ƙara alamar ina da buƙatar cin wani abu na girgiza masa kai a hankali nace
"Babu komai Abba na samu sauƙi".
"Allah ya ƙara afuwa, ki huta. Su Goggo Habiba suna hanya ni na hana Mu'azzam ma ya kawo ta tun da safe saboda an ce a barki ki huta yanzun ma ta tayar da rigima ne tun da kuma sallamar ki za'ayi shi yasa nace su zo ɗin kawai" Abba ya sake faɗa. Nayi rau rau nace
"Goggo Habiba kuma? To Mama fa?" Be bani amsa ba ya juya kan Bilal da tun shigowar su yayi shiru kamar ruwa ya cinye shi yace
"Ina ganin zaka iya tafiya ko" se ya kalle ni kafin ya shafa kai haɗi da rusunawa yace
"To Abba, Allah ya bata lafiya yasa kaffara ne" Abba da Uncle Mudassir suka amsa da amin se ya nufi ƙofa yana waige na.
"Idan ka samu sarari yau ko gobe kazo ina son ganin ka" Abba ya faɗa Bilal na dab da fita, take na karanci razanar da Bilal yayi se kuma ya waske yana murmushi yace
"To Abba idan ma yanzu kake son ganin nawa se na jira ka a waje"
"Ka same ni a filin sukuwa ƙarfe huɗu zuwa biyar na yamma" Abban ya bashi amsa daga nan ya fita bayan ya sake musu sallama zuciyar sa fal zullumin ganin me Abban Halima yake so yayi masa?
Se da akayi sallar magriba muka bar asibiti saboda wata allura da aka yi mun ƙarfe shida. Na lumshe ido na ina ci gaba da sauraron faɗan da Goggo Habi take yi, tun da taje asibitin bakin ta be huta ba har yanzun da muke hanyar komawa gida zagi kalar wanda ta manta ne kawai bata mun ba har tana cewa in da ita ce Labiba bari na zatayi na mutu kawai tun da turbar da na zaɓar wa kaina kenan to saboda Allah ni na ɗorawa kaina son Bilal ake nufi ko me? Allah da kansa ya ce shi yake sanya ƙauna a zukatan mutane, menene laifi na sabo da nayi so domin Allah? Zuciya ce kowa da irin tasa, wani yana ɗaukar abubuwa da sauƙi in da wani yake zafafawa babu kuma wanda za'a ce baya kan daidai.
Naji daɗi kuma ban ji ba da naga mun wuce gidanmu ba gidan Anty Labiba ba. Allah ya gani haushin ta nake ji saboda ita ce silar komai da bata uzzurawa Bilal da tambaya ba ai da komi ba lalace haka ba rashin jin daɗin komawa gida kuma da naji nasan surutun Goggo Habi tsaf ze iya haifar mun da wani sabon ciwon se dai ba ta tata nake ba tun da nasan bata da ikon sakawa ko hanawa a cikin lamarin aure na, kakata ce ta ɓangaren uwa ba uba ba balle naji tsoron zata iya tilasta Abba yayi abin da suke so.
Abin da ya saka jiki na yin sanyi yanda ko kallon banza ban ishi Mama ba balle na arziƙi, haka nan na shige ɗaki na jiki babu ƙwari ina jin babu daɗi. Mama da ko ciwon kai nake yi se ta damu bata samun nutsuwa har se taga na warke ita ce zan kwana a asibiti ba taje ta duba ni ba sannan in dawo gida tayi kamar bata san da wanzuwata ba? Ko da yake ba laifin kowa bane se na Anty Labiba ita take zugata, se kace ita wani ya mata dole a sanda ta kawo nata mijin da ni ban ma gama tantance yaren sa ba har yau, su ba yarabawa ba ba igala ba haka nan kuma ta aure shi suke zaune shekara goma ba wanda yace mata saboda me se ni zata saka a bakin duniya ta cusawa kowa tsanar wanda nake so.
Da daddare gurin ƙarfe sha ɗaya yunwa ta matsa mun dole na katse wayar da muke yi da Bilal na fito neman abin da zan ci. Tun ƙarfe tara muke waya, yau ɗin ya dawo asalin Bilal ɗina me so na da tattalin farin ciki na. Zumuɗin da nake jini nin ban ga yana yi akan auran mu ba se gashi yau ya tashi gaba ɗaya ya rikita ni da tsadaddun kalaman soyayya irin waɗan da kunnuwa suke da muradin sauraro a ko da yaushe. Rabon da muyi hira ta nutsuwa kuma me daɗi irin haka tun ba'a saka ranar auren mu ba. Kamar yanda ya ce mun wani alkhairi ne ya sakko mana ba zato na tsammani yana zaune kawai wani tsohon abokin Baban sa ya kira shi yake cewa ya samu labarin zeyi aure, a taƙaice dai ya saka yayi masa list na duk wani abu daya rage masa cikin harkar auran yace ze ɗauki nauyi zancen da akeyi har ya turo masa kuɗaɗe ya ce a fara aikin kafin sauran su iso. Ya ce mun
"Halims Allah na son mu kasance tare, a sanda na sare nake ganin ba zan iya ba se ya turo mun da agaji ta in da ban yi tsammani ba. Ke alkhairi ce a rayuwa ta ina roƙon Allah ya bani ikon kyautata miki kwatankwacin yanda kika kawo haske cikin rayuwa ta".
Saboda murna har rawa se da nayi duk da ba wai na gama jin ƙwarin jiki na bane ba, na ringa kwararawa ko ma wanene wanda ya kawo mana wannan ɗaukin addu'a. Bamu kashe wayar ba se da naji zuciya ta ta fara tashi dalilin yunwa ga kuma surutun da muke ta yi ba dan Bilal ya so ba muka rabu akan da zarar na ci abincin na yi masa ko flashing ne.
Abba da Mama na tarar zaune a falo, gaba na ya faɗi ganin hawaye akan fuskar Mama Abba kuma yana durƙushe gaban ta da alama haƙuri yake bata, na matsa kusa dasu da sauri ido na na kawo ruwa na fara tambayar me ya faru?
"Babu komai Halima, wai tunanin zakiyi aure ki bar mu ne duk ya fara sanyayar mana jiki shi ne take kuka" Abba ya faɗa kamar me yin magana da yarinya yar shekara biyar ko ƙasa da haka. Fashewa nayi da kuka na zauna gaban Mama nace
"Ni ce ko? Sabo da ni kike kuka?"
"Me yasa zan yi kuka saboda ke Halima? Bana fatan ubangiji ya nuna mun ranar da fushin wani daga cikin ku ze taɓa zuciya ta har yasa in zubar muku da hawaye ina neman tsari da hakan. Hawayen tausayin nake yi bana baƙin ciki ba" Mama ta faɗa se Abba yace
"Haba Amina ban san sands kika zama me nace akan magana guda ɗaya ba, shi ba zaki yarda da ƙaddara ki bar komai a hannun Allah ba?"
Fuska babu walwala ya shiga ɗakin, na ɗaga kai da sauri jin an buɗe ƙofa muka haɗa ido ban san sanda na miƙe ina sakin murmushi ba ya nufo ni shima yana murmushi yace
"Kin tayar mun da Hankali Halims, me yasa?"
"Sau ke gani na nayi ƙasa ina wasa da gefen hijabi na ba tare da nace masa komai ba, ganin sa ya bani nutsuwar zuciya ya kuma tabbatar mun yana tare dani ma'ana ya janye waɗan can kalaman marasa daɗi daya faɗa mun jiya wai mu haƙura da juna.
"Ki zauna kar ƙafafun ki su gaji" ya faɗa yana kallo na se na ƙarasa na zauna akan gado har sannan murmushi be bar kan fuskata ba, ya matso da kujera kusa da ni ya zauna yana leƙa fuskata yace
"Ashe haka kike so na ban sani ba Halims?"
Harar wasa na masa ba tare da nace komai ba, ya sake gyara kijerar da yake a kai ya langwaɓar da kai yana kallo na yace
"Ko da nace mu haƙura ƙarya nake yi ni da kaina nasan bazan iya jure rashin ki a tare da ni ba. Tun da kika tafi ni kaina dauriya ce kawai irin ta maza ta sa ba'a kawo ni an kwantar a gadon Asibiti ba mutuwa ce kaɗai zata iya raba ni dake Halims amma muddin ina raye dole zan nemo mafita, ki taya ni da addu'a Allah ya hore mun na fita kunyar ki kafin ranar auren mu albarkacin wannan son da kike mun bazan baki kunya ba".
Bude ƙofar da aka yi ya saka yaja baya daga gare ni muka kalli ƙofar a tare, Abba ne ya shigo tare da Uncle Mudassir Autan su Mamanmu. Cikin jin kunya Bilal ya miƙe daga kujerar da yake zaune yana musu sannu da zuwa, fuskar Abba babu yabo babu fallasa ya nufo in da nake se Uncle Mudassir ne ya amsa masa kafin shima ya matso yana mun murmushi na gaishe su ya shiga tambayar jiki na sannan ya ɗauki folder dake kan bedside ya shiga dubawa dake shima likita ne.
"Dr yace zuwa yamma zasu sallame ki tun da babu wani abu ko akwai in da yake yi miki ciwo ne yanzun?" Abba ya tambaye ni, se na shafa ciki na da naji yayi ƙara alamar ina da buƙatar cin wani abu na girgiza masa kai a hankali nace
"Babu komai Abba na samu sauƙi".
"Allah ya ƙara afuwa, ki huta. Su Goggo Habiba suna hanya ni na hana Mu'azzam ma ya kawo ta tun da safe saboda an ce a barki ki huta yanzun ma ta tayar da rigima ne tun da kuma sallamar ki za'ayi shi yasa nace su zo ɗin kawai" Abba ya sake faɗa. Nayi rau rau nace
"Goggo Habiba kuma? To Mama fa?" Be bani amsa ba ya juya kan Bilal da tun shigowar su yayi shiru kamar ruwa ya cinye shi yace
"Ina ganin zaka iya tafiya ko" se ya kalle ni kafin ya shafa kai haɗi da rusunawa yace
"To Abba, Allah ya bata lafiya yasa kaffara ne" Abba da Uncle Mudassir suka amsa da amin se ya nufi ƙofa yana waige na.
"Idan ka samu sarari yau ko gobe kazo ina son ganin ka" Abba ya faɗa Bilal na dab da fita, take na karanci razanar da Bilal yayi se kuma ya waske yana murmushi yace
"To Abba idan ma yanzu kake son ganin nawa se na jira ka a waje"
"Ka same ni a filin sukuwa ƙarfe huɗu zuwa biyar na yamma" Abban ya bashi amsa daga nan ya fita bayan ya sake musu sallama zuciyar sa fal zullumin ganin me Abban Halima yake so yayi masa?
Se da akayi sallar magriba muka bar asibiti saboda wata allura da aka yi mun ƙarfe shida. Na lumshe ido na ina ci gaba da sauraron faɗan da Goggo Habi take yi, tun da taje asibitin bakin ta be huta ba har yanzun da muke hanyar komawa gida zagi kalar wanda ta manta ne kawai bata mun ba har tana cewa in da ita ce Labiba bari na zatayi na mutu kawai tun da turbar da na zaɓar wa kaina kenan to saboda Allah ni na ɗorawa kaina son Bilal ake nufi ko me? Allah da kansa ya ce shi yake sanya ƙauna a zukatan mutane, menene laifi na sabo da nayi so domin Allah? Zuciya ce kowa da irin tasa, wani yana ɗaukar abubuwa da sauƙi in da wani yake zafafawa babu kuma wanda za'a ce baya kan daidai.
Naji daɗi kuma ban ji ba da naga mun wuce gidanmu ba gidan Anty Labiba ba. Allah ya gani haushin ta nake ji saboda ita ce silar komai da bata uzzurawa Bilal da tambaya ba ai da komi ba lalace haka ba rashin jin daɗin komawa gida kuma da naji nasan surutun Goggo Habi tsaf ze iya haifar mun da wani sabon ciwon se dai ba ta tata nake ba tun da nasan bata da ikon sakawa ko hanawa a cikin lamarin aure na, kakata ce ta ɓangaren uwa ba uba ba balle naji tsoron zata iya tilasta Abba yayi abin da suke so.
Abin da ya saka jiki na yin sanyi yanda ko kallon banza ban ishi Mama ba balle na arziƙi, haka nan na shige ɗaki na jiki babu ƙwari ina jin babu daɗi. Mama da ko ciwon kai nake yi se ta damu bata samun nutsuwa har se taga na warke ita ce zan kwana a asibiti ba taje ta duba ni ba sannan in dawo gida tayi kamar bata san da wanzuwata ba? Ko da yake ba laifin kowa bane se na Anty Labiba ita take zugata, se kace ita wani ya mata dole a sanda ta kawo nata mijin da ni ban ma gama tantance yaren sa ba har yau, su ba yarabawa ba ba igala ba haka nan kuma ta aure shi suke zaune shekara goma ba wanda yace mata saboda me se ni zata saka a bakin duniya ta cusawa kowa tsanar wanda nake so.
Da daddare gurin ƙarfe sha ɗaya yunwa ta matsa mun dole na katse wayar da muke yi da Bilal na fito neman abin da zan ci. Tun ƙarfe tara muke waya, yau ɗin ya dawo asalin Bilal ɗina me so na da tattalin farin ciki na. Zumuɗin da nake jini nin ban ga yana yi akan auran mu ba se gashi yau ya tashi gaba ɗaya ya rikita ni da tsadaddun kalaman soyayya irin waɗan da kunnuwa suke da muradin sauraro a ko da yaushe. Rabon da muyi hira ta nutsuwa kuma me daɗi irin haka tun ba'a saka ranar auren mu ba. Kamar yanda ya ce mun wani alkhairi ne ya sakko mana ba zato na tsammani yana zaune kawai wani tsohon abokin Baban sa ya kira shi yake cewa ya samu labarin zeyi aure, a taƙaice dai ya saka yayi masa list na duk wani abu daya rage masa cikin harkar auran yace ze ɗauki nauyi zancen da akeyi har ya turo masa kuɗaɗe ya ce a fara aikin kafin sauran su iso. Ya ce mun
"Halims Allah na son mu kasance tare, a sanda na sare nake ganin ba zan iya ba se ya turo mun da agaji ta in da ban yi tsammani ba. Ke alkhairi ce a rayuwa ta ina roƙon Allah ya bani ikon kyautata miki kwatankwacin yanda kika kawo haske cikin rayuwa ta".
Saboda murna har rawa se da nayi duk da ba wai na gama jin ƙwarin jiki na bane ba, na ringa kwararawa ko ma wanene wanda ya kawo mana wannan ɗaukin addu'a. Bamu kashe wayar ba se da naji zuciya ta ta fara tashi dalilin yunwa ga kuma surutun da muke ta yi ba dan Bilal ya so ba muka rabu akan da zarar na ci abincin na yi masa ko flashing ne.
Abba da Mama na tarar zaune a falo, gaba na ya faɗi ganin hawaye akan fuskar Mama Abba kuma yana durƙushe gaban ta da alama haƙuri yake bata, na matsa kusa dasu da sauri ido na na kawo ruwa na fara tambayar me ya faru?
"Babu komai Halima, wai tunanin zakiyi aure ki bar mu ne duk ya fara sanyayar mana jiki shi ne take kuka" Abba ya faɗa kamar me yin magana da yarinya yar shekara biyar ko ƙasa da haka. Fashewa nayi da kuka na zauna gaban Mama nace
"Ni ce ko? Sabo da ni kike kuka?"
"Me yasa zan yi kuka saboda ke Halima? Bana fatan ubangiji ya nuna mun ranar da fushin wani daga cikin ku ze taɓa zuciya ta har yasa in zubar muku da hawaye ina neman tsari da hakan. Hawayen tausayin nake yi bana baƙin ciki ba" Mama ta faɗa se Abba yace
"Haba Amina ban san sands kika zama me nace akan magana guda ɗaya ba, shi ba zaki yarda da ƙaddara ki bar komai a hannun Allah ba?"