Sashe 15
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Bilal ka faɗa mun kai tsaye me kake nufi ko me kake so ayi yanzu dan Allah tun baka janyo zuciya ta ta buga ba" na katse dogon sharhin daya ɗakko wanda babu abin da nake fahimta a ciki. Shiru yayi ina kallon yan da abin wuyan sa ke sama da ƙasa alamar magana na cikin sa ya kasa furtata kafin ya sake riƙe hannaye na biyu duk yanda naso na ƙwace be bani dama ba haka ya kafe idon sa cikin nawa yana murza zoben dake hannu na yace
"Ina son ki Halima bana fatan na rasa ki amma a yanzu bani da halin auren ki".
"Dagaske Bilal dama yaudara ta kake yi ba aure na zaka yi ba?" Na faɗa cikin karyewar sauti. Se ya ƙara ƙarfin ruƙon da yayiwa hannaye na yace
"Allah shine shaida ina son ki Halima dai dai da rana ɗaya ban taɓa niyyar yaudarar ki ba"
"Amma da bakin ka yanzu kace ba zaka iya aure na ba, me yasa tun farko baka faɗa mun ba se da ka bari auren mu ya rage sati biyu?" Na faɗa ina fashe wa da kuka.
"Nayi zaton zan iya Halima, na ɗauka zan samu yanda nake so kafin lokacin amma hakan yaci tura. Ta yaya kike zaton iyayenki zasu bani ke bayan ba ni da ko muhallin da zan ajiye ki?" Ya faɗa tamkar shi ma ze fashe da kukan. Kamar zan shiɗe nace
"Shi kuma wannan gidan fa? Ko dama ba naka bane ƙarya kayi mun kace na ka ne?"
"Gida na ne Halima amma wannan shi da kango ai basu da maraba ta yaya mutum ze shiga ya zauna a gurin da ko daɓe babu? Ki aje maganar wannan gidan a gefe kawai dan dashi da babu banbancin su kaɗan ne. Da ace ina da sararin da zan kama miki haya ma da wlh bazan damu ba amam bani dashi, a yanzu bani da wasu kuɗi a tare dani se wanda za a siyawa Fadila kujera su kansu basu gama haɗuwa ba dama sadakin ta ne na cika kuma na ranci wani abu ciki dashi na ƙarasa aikin fulasta ai kin gani sanda muka je iya waje ne da fulasta ba ayi a waje ba ko? Zaɓi biyu ne kaɗai ya rage mana Halima, ko dai a ɗaga auren mu wanda bana zaton iyayenki zasu amince tun da har sun ambata dama akwai wanda suke so su haɗa ki dashi a familyn ku kenan se dai na haƙura dake tun da bani da halin auren ki shikenan rayuwa ta tazo ƙarshe ban san wace alƙibla zan kalla ba idan babu ke a tare da ni".
[12/19/2024, 8:06 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 7*
Page 7
Na fi minti goma tsaye a ƙofar gidan mu ni ban shiga ba kuma ban bar gurin ba. Maganganun da mu kayi da Bilal ne suke mun amsa kuwwa a kunnuwa na da ƙwaƙwalwata bana kin ko wanne sauti dake zagaye dani banda muryar sa.
"Ba ni da kuɗin da zan ƙarasa gini Halima, ba kuma ni da sararin da zan kama haya a yanzu. Abu biyu ya rage, ko dai iyayen ki su ɗaga auren mu ko kuma mu haƙura gaba ɗaya, ƙila a gaba idan muna da rabon kasancewa tare se muyi aure. Ina son ki Halima amma bani da halin mallakar ki a yanzu" kalaman ƙarshe daya gaya mun kenan. Bana ko gani sosai na shiga bubbuga ƙofa, se da na buga sau uku kafin aka buɗe. Musa ne, jikan Goggo Habi Ƙanwar Mahaifin Mamanmu. Ɗan ta ɗaya Baba Sulaiman kuma shine mahaifin Musan accident suka yi dashi da matar sa duk suka rasu. A Birnin gwari take da zama dama naji Anty Labiba tana faɗar tace tun biki na saura sati biyu zata zo ashe har ta zo ɗin kuwa.
Kallo na ya tsaya yi saboda niƙab ɗin dake fuska na raɓe shi na wuce ina haɗa hanya, motar Abba da na gani a ajiye yasa na gane yana gida dan haka kai tsaye na wuce falon sa. Tare da Aminin sa Baba Hashim na same su suna magana daga kuma yana yin fuskokin su na fahimci ko ma me suke tattauna ba magana me daɗi bace. A tare suka amsa sallama ta suna kallo na, ka ƙarasa gaban Abba, tamkar wadda tazo isar da saƙon rasuwa haka na fashe da kuka irin me gigitar nan har jiki na yana jijjiga. Abba ya miƙe hankali tashe ya ruƙo ni yana cewa
"Lafiya Halima? Me ya samu su Labibar?" Haka Baba Hashimu ma cikin kaɗuwa suka ringa tambaya ta me nene amma na ƙi cewa komai har se da nayi kuka iya kar yi na se da naga Baba Hashimu ya nufi ƙofa yana cewa
"Bari na kira Amina" se lokacin na buɗe baki daƙyar nace
"Ba se ka kira ta ba". Se da na sake kwashe kusan minti biyar ina kokawa da kukan dake taho mun da zarar na buɗe baki kafin daƙyar na iya cewa
"Abba Bilal ne"
"Me ya same shi?" Abban ya tambaye ni. Ina kuka tamkar raina ze fita na tsara musu duk yanda mukayi da Bilal da abin da ya gaya mun ban rage komai ba. Su kayi shiru kamar ruwa ya cinye su banda sautin kuka na da ƙarar fanka baka jin komai har kusan minti goma da alama duk su biyun bakin su ya mutu sun rasa abin da zasu faɗa ne. Daƙyar Baba Hashimu ya katse shirun yace mun
"Ki bar kukan haka Halima kiyi shiru muyi magana". Se da na sake shafe wasu mintunan kafin na iya tsagaitawa da kukan, yace
"Zaman nan da muka yi zancen ki muke yi Halima. Mahaifinki ya kira ni yana cike da damuwa akan lamarin auran ki. Yau saura kwana goma sha huɗu amma babu wata magana me ƙarfi daga gidan maza su basu zo akan suna sane da lokaci ba kuma basu ce wani abu dangane da shirun da suka yi ba. Yanzu Alhaji Salahu muke ji yazo mu ji ta bakin sa akan abin da ya kama muyi se kuma gashi kin zo da wannan maganar. Ina ganin ai ba abin kuka da tayar da hankali bane ba, dama kullum cikin yi muku addu'a muke akan Allah ya zaɓa muku mazaje na gari. Irin haka babu daɗi, amma sha'anin aure da ace ayi azo ana dana sani daga baya gara a haƙura se kiga ubangiji ya musanya miki da wanda ya fishi zama alkhairi a gare ki".
Kukan dana sake fashewa dashi se ka rantse da Allah irin marin nan na shammata ya zabga mun, ko da yake ai gara ya dake ni naji zafin a kan fata ta da ciwon da yake neman haifar wa zuciya ta. Na rabu da Bilal fa yake cewa. Daga shi har Abban Kallo na suka ringa yi cikin mamaki za a ko ace ɗimuwa tamkar dai basu fahimci dalilin sabon kukan dana dasa ba. Ban ji nauyin Baba Hashim ba domin dama Abba babu batun jin kunya tsakani na dashi nace
"Wallahi ina son sa Abba, idan na rasa Bilal ban san ya zanyi da rayuwa ta ba ni dai a nemi wata mafitar amma kar ma a fara cewa in rabu dashi" na haɗe kai na da kujera na ci gaba da rera kuka. Baba Hashim ya ringa salati yana tafa hannu Abba dai yayi shiru ya tallafe haɓar sa da hannu biyu yana kallo na. A haka Baba Salahu ya shigo ya same mu, a taƙaice Baba Hashim ya yi masa bayanin abin da nazo musu dashi yayi shiru kawai yana jimanta abun a ransa yana kallo na, jin kukan nawa bana ƙare bane yasa ya fara magana cikin lallashi yana cewa
"Yi shiru Halimatu kwantar da hankalin ki babu wanda ze raba ku amma ki fara amsa mun tambayar nan tsakani da Allah kar ki mun ƙarya ni kuma zan yi iya ƙoƙari na ganin na samar miki muradin ki". Na tsagaita kukan ina share hawaye haɗi da face maji na da hijabi na, shiry ya ɗan yi cikin jin nauyin maganar da take bakin sa kafin daƙyar ya iya cewa
"Halimatu, kar kiji nauyi ko kunyar mu ki gaya mun tsakanin ki da Allah wani abu na rashin dacewa ya taɓa shiga tsakanin ki da Bilal ne?"
Da sauri Abba ya kalle shi se Baba Hashim ya masa alama da ido akan kar yace komai ni kuwa a yanayin da nake ciki ban ma ji tambayar tasa a wani daban ba kai tsaye na ce masa
"Wallahi Baba Bilal ba ɗan iska bane ni yake so tsakani da Allah ba wai wani abu nawa ba. Ni ko hannu be taɓa riƙewa da gangan ba aure na yake so kawai ba wani abu ba".
"Alhamdulillah" suka haɗa baki su ukun suka faɗa Abba har seda ya gyara zama ya koma cikin kujera ya kwanta haɗi da rufe idanun sa. Nasiha Baba Hashim da Baba Salahu suka shiga yi mun se dai jin su kawai nakeyi badan ina ɗauka ba, sanyin da naji da duk su biyun suke jaddada na kwantar da hankali na babu abin da ze faru zasu kira Bilal suyi magana dashi. Dana fito daga falon nasan in na shiga gurin Mama ƙarshe raina ne ze sake ɓaci se kawai na maida niƙab ɗina na fice na tafi gidan su Hansa'u.
"Ina son ki Halima bana fatan na rasa ki amma a yanzu bani da halin auren ki".
"Dagaske Bilal dama yaudara ta kake yi ba aure na zaka yi ba?" Na faɗa cikin karyewar sauti. Se ya ƙara ƙarfin ruƙon da yayiwa hannaye na yace
"Allah shine shaida ina son ki Halima dai dai da rana ɗaya ban taɓa niyyar yaudarar ki ba"
"Amma da bakin ka yanzu kace ba zaka iya aure na ba, me yasa tun farko baka faɗa mun ba se da ka bari auren mu ya rage sati biyu?" Na faɗa ina fashe wa da kuka.
"Nayi zaton zan iya Halima, na ɗauka zan samu yanda nake so kafin lokacin amma hakan yaci tura. Ta yaya kike zaton iyayenki zasu bani ke bayan ba ni da ko muhallin da zan ajiye ki?" Ya faɗa tamkar shi ma ze fashe da kukan. Kamar zan shiɗe nace
"Shi kuma wannan gidan fa? Ko dama ba naka bane ƙarya kayi mun kace na ka ne?"
"Gida na ne Halima amma wannan shi da kango ai basu da maraba ta yaya mutum ze shiga ya zauna a gurin da ko daɓe babu? Ki aje maganar wannan gidan a gefe kawai dan dashi da babu banbancin su kaɗan ne. Da ace ina da sararin da zan kama miki haya ma da wlh bazan damu ba amam bani dashi, a yanzu bani da wasu kuɗi a tare dani se wanda za a siyawa Fadila kujera su kansu basu gama haɗuwa ba dama sadakin ta ne na cika kuma na ranci wani abu ciki dashi na ƙarasa aikin fulasta ai kin gani sanda muka je iya waje ne da fulasta ba ayi a waje ba ko? Zaɓi biyu ne kaɗai ya rage mana Halima, ko dai a ɗaga auren mu wanda bana zaton iyayenki zasu amince tun da har sun ambata dama akwai wanda suke so su haɗa ki dashi a familyn ku kenan se dai na haƙura dake tun da bani da halin auren ki shikenan rayuwa ta tazo ƙarshe ban san wace alƙibla zan kalla ba idan babu ke a tare da ni".
[12/19/2024, 8:06 PM] Hauwa Galadima: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 7*
Page 7
Na fi minti goma tsaye a ƙofar gidan mu ni ban shiga ba kuma ban bar gurin ba. Maganganun da mu kayi da Bilal ne suke mun amsa kuwwa a kunnuwa na da ƙwaƙwalwata bana kin ko wanne sauti dake zagaye dani banda muryar sa.
"Ba ni da kuɗin da zan ƙarasa gini Halima, ba kuma ni da sararin da zan kama haya a yanzu. Abu biyu ya rage, ko dai iyayen ki su ɗaga auren mu ko kuma mu haƙura gaba ɗaya, ƙila a gaba idan muna da rabon kasancewa tare se muyi aure. Ina son ki Halima amma bani da halin mallakar ki a yanzu" kalaman ƙarshe daya gaya mun kenan. Bana ko gani sosai na shiga bubbuga ƙofa, se da na buga sau uku kafin aka buɗe. Musa ne, jikan Goggo Habi Ƙanwar Mahaifin Mamanmu. Ɗan ta ɗaya Baba Sulaiman kuma shine mahaifin Musan accident suka yi dashi da matar sa duk suka rasu. A Birnin gwari take da zama dama naji Anty Labiba tana faɗar tace tun biki na saura sati biyu zata zo ashe har ta zo ɗin kuwa.
Kallo na ya tsaya yi saboda niƙab ɗin dake fuska na raɓe shi na wuce ina haɗa hanya, motar Abba da na gani a ajiye yasa na gane yana gida dan haka kai tsaye na wuce falon sa. Tare da Aminin sa Baba Hashim na same su suna magana daga kuma yana yin fuskokin su na fahimci ko ma me suke tattauna ba magana me daɗi bace. A tare suka amsa sallama ta suna kallo na, ka ƙarasa gaban Abba, tamkar wadda tazo isar da saƙon rasuwa haka na fashe da kuka irin me gigitar nan har jiki na yana jijjiga. Abba ya miƙe hankali tashe ya ruƙo ni yana cewa
"Lafiya Halima? Me ya samu su Labibar?" Haka Baba Hashimu ma cikin kaɗuwa suka ringa tambaya ta me nene amma na ƙi cewa komai har se da nayi kuka iya kar yi na se da naga Baba Hashimu ya nufi ƙofa yana cewa
"Bari na kira Amina" se lokacin na buɗe baki daƙyar nace
"Ba se ka kira ta ba". Se da na sake kwashe kusan minti biyar ina kokawa da kukan dake taho mun da zarar na buɗe baki kafin daƙyar na iya cewa
"Abba Bilal ne"
"Me ya same shi?" Abban ya tambaye ni. Ina kuka tamkar raina ze fita na tsara musu duk yanda mukayi da Bilal da abin da ya gaya mun ban rage komai ba. Su kayi shiru kamar ruwa ya cinye su banda sautin kuka na da ƙarar fanka baka jin komai har kusan minti goma da alama duk su biyun bakin su ya mutu sun rasa abin da zasu faɗa ne. Daƙyar Baba Hashimu ya katse shirun yace mun
"Ki bar kukan haka Halima kiyi shiru muyi magana". Se da na sake shafe wasu mintunan kafin na iya tsagaitawa da kukan, yace
"Zaman nan da muka yi zancen ki muke yi Halima. Mahaifinki ya kira ni yana cike da damuwa akan lamarin auran ki. Yau saura kwana goma sha huɗu amma babu wata magana me ƙarfi daga gidan maza su basu zo akan suna sane da lokaci ba kuma basu ce wani abu dangane da shirun da suka yi ba. Yanzu Alhaji Salahu muke ji yazo mu ji ta bakin sa akan abin da ya kama muyi se kuma gashi kin zo da wannan maganar. Ina ganin ai ba abin kuka da tayar da hankali bane ba, dama kullum cikin yi muku addu'a muke akan Allah ya zaɓa muku mazaje na gari. Irin haka babu daɗi, amma sha'anin aure da ace ayi azo ana dana sani daga baya gara a haƙura se kiga ubangiji ya musanya miki da wanda ya fishi zama alkhairi a gare ki".
Kukan dana sake fashewa dashi se ka rantse da Allah irin marin nan na shammata ya zabga mun, ko da yake ai gara ya dake ni naji zafin a kan fata ta da ciwon da yake neman haifar wa zuciya ta. Na rabu da Bilal fa yake cewa. Daga shi har Abban Kallo na suka ringa yi cikin mamaki za a ko ace ɗimuwa tamkar dai basu fahimci dalilin sabon kukan dana dasa ba. Ban ji nauyin Baba Hashim ba domin dama Abba babu batun jin kunya tsakani na dashi nace
"Wallahi ina son sa Abba, idan na rasa Bilal ban san ya zanyi da rayuwa ta ba ni dai a nemi wata mafitar amma kar ma a fara cewa in rabu dashi" na haɗe kai na da kujera na ci gaba da rera kuka. Baba Hashim ya ringa salati yana tafa hannu Abba dai yayi shiru ya tallafe haɓar sa da hannu biyu yana kallo na. A haka Baba Salahu ya shigo ya same mu, a taƙaice Baba Hashim ya yi masa bayanin abin da nazo musu dashi yayi shiru kawai yana jimanta abun a ransa yana kallo na, jin kukan nawa bana ƙare bane yasa ya fara magana cikin lallashi yana cewa
"Yi shiru Halimatu kwantar da hankalin ki babu wanda ze raba ku amma ki fara amsa mun tambayar nan tsakani da Allah kar ki mun ƙarya ni kuma zan yi iya ƙoƙari na ganin na samar miki muradin ki". Na tsagaita kukan ina share hawaye haɗi da face maji na da hijabi na, shiry ya ɗan yi cikin jin nauyin maganar da take bakin sa kafin daƙyar ya iya cewa
"Halimatu, kar kiji nauyi ko kunyar mu ki gaya mun tsakanin ki da Allah wani abu na rashin dacewa ya taɓa shiga tsakanin ki da Bilal ne?"
Da sauri Abba ya kalle shi se Baba Hashim ya masa alama da ido akan kar yace komai ni kuwa a yanayin da nake ciki ban ma ji tambayar tasa a wani daban ba kai tsaye na ce masa
"Wallahi Baba Bilal ba ɗan iska bane ni yake so tsakani da Allah ba wai wani abu nawa ba. Ni ko hannu be taɓa riƙewa da gangan ba aure na yake so kawai ba wani abu ba".
"Alhamdulillah" suka haɗa baki su ukun suka faɗa Abba har seda ya gyara zama ya koma cikin kujera ya kwanta haɗi da rufe idanun sa. Nasiha Baba Hashim da Baba Salahu suka shiga yi mun se dai jin su kawai nakeyi badan ina ɗauka ba, sanyin da naji da duk su biyun suke jaddada na kwantar da hankali na babu abin da ze faru zasu kira Bilal suyi magana dashi. Dana fito daga falon nasan in na shiga gurin Mama ƙarshe raina ne ze sake ɓaci se kawai na maida niƙab ɗina na fice na tafi gidan su Hansa'u.