Sashe 103
Kura A Rumbu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BILAL
Bacci rabi da rabi yayi saboda alarm ɗin daya saita tun ƙarfe huɗu domin baya son wani dalili da zai janyo har tsautsayi ya gifta gari yayi haske bai fitar da Jalilah daga unguwar ba. Tun kiran farko yayi wanka ya zauna yana jira a kira sallah, ana fara kira kuwa ya shiga ɗakin ya fara tashinta amma tayi masa banza sai ma gyara kwanciya da tayi, cikin ƙufula da halinta ya ce
"Dan Allah ki tashi, kin san dai yanzu zakiga gari yayi haske idan kuma ba so kikeyi ki makara ba". Bata amsa ba ya gaji da tsayuwa yana mitar ta tashi jin har an tayar da sallah ya sa ya fita yana sakin ƙwafa, shi yanzu ya ke tunanin kamar ma da biyu tace sai a nan zata kwana saboda taja masa wani bala'in a unguwa. Hawa uku ya murzawa Get muƙulli kafin ya tafi, yana idar da sallah kuwa bai zauna ba ya fito da sauri ya koma yana tafiya yana satar kallon mutane gaba ɗaya ya tsargi kansa gani yake kamar kowa ya san mace ta kwana a gidansa a haka ya shige ya sakw kullo ƙofar ta ciki.
Duk yanda yayi da Jalilah akan ta tashi tayi sallah ta shirya su tafi taƙi ƙarshe ta balbaleshi da masifa akan ya fita ya bata guri saboda tazo gidansa ne zai uzzura mata ya hanata bacci ai ta san da tafiyar babu kuma sisinsa cikin kuɗin data biya balle yace idan ta rasa jirgi zata ja masa asara.
"Aikin banza kawai saboda na zo wannan akurkin gidan naka shine zaka ringa mun ihu akai in tashi to ba zan tafi ba idan kana da ƙarfi ka ɗauke ni a wuya ka fita dani kuma wlh idan ka ishe ni sai in tashi na fita ƙofar gida ka san ni sarai tijara zan maka nace ka kawoni kwanan gida ka hanani kuɗi na idan ya so sai naga ƙaryar iskanci" ta faɗa tana balla masa harara.
Tsaf ya zuge bakinsa domin baya shakku zata aikata abinda ta faɗa ɗin haka ya wuce yana waigenta tamkar zaiyi kuka ya koma falo ya zauna yana kallon agogo. Har ƙarfe bakwai ta gota bata fito ba ita da tace jirginsu ƙarfe takwas, shahada yayi ya sake komawa ɗakin ya tsaya daga bakin ƙofa yana kallonta ta tashi tana zaune tsakiyar gadon waya kare a kunnenta.
Murmushi ta sakar masa hakan ya bashi ƙwarin guiwar matsawa kusa da ita, da Mamanta take waya sai bayan ta kammala ta buɗe masa hannu alamar ya zo, haka ya ƙarasa ya rungume ta ta ɗora kanta a ƙirjinsa tana cewa
"Jikina duk yayi tsami kazo kayi mun wanka".
"Jalilah bakwai ta wuce fa kada ki makara" ya faɗa yana ƙoƙarin janyewa sai ta sake shige masa tana cewa
"8pm ne fa flight ɗin ba morning ba". Yanda kasan ya kurma ihu saboda takaici, duk yanda ya so ya cigaba da pretending sai da fuskarsa ta nuna ya zameta daga jikinsa yana cewa
"Amma tsakani da Allah me yasa zaki mun haka?"
Kallon banza ta watsa masa kafin ta miƙe tana banƙarewa ta sigar miƙa ya yi saurin ɗauke idonsa daga kanta, toilet ta wuce abinta tana wata tafiyar iyashege. Ya zauna gefen gadon yana cika yana batsewa a ransa yana ayyana yanda zai yi da ita su rabu ƙalau dan ya lura a shirye take data yanka masa nata rashin mutunchin.
Tashi yayi ya matsa bakin ƙofar toilet ɗin jin tana kiransa, ƙaramin kit ɗin ta tace ta miƙe mata ya wuce ya ɗakko shi yana buɗe ƙofar da niyyar ya bata ta ja shi ciki duk kuma yanda ya so da ya noƙe ko a jikinta sai da ya mata abinda take so kafin ta barshi ya fito tayi wankanta. Haka take kamar mayya in dai ta so abu to fa sai ta same shi ko ta daɗin rai ko aka sin haka.
Falo ya koma ya zauna bayan yayi wanka a ɗayan ɗakin ya dafe kansa da yaji kamar yana so ya masa ciwo. Allah ya sani tun sanda Halima ta bankaɗo sirrin sa komai ya fita a ransa kuma yayi alƙawarin dainawa amma kuma ya rasa yanda zai yi da Jalilah dukda ya fara janye mata kuma lokaci kaɗan yake jira dama wannan tafiyar da zasuyi ce target ɗin sa na ƙarshe da zarar sun shigo da kayyakin an buɗe company zai yi duk mai yuwuwa ayi rubutu ta yanda zai mallaki kaso mai tsoka cikin shares ɗin kamar yanda tayi masa alƙawari idan ya so ko sun rabu ya san ya tsira da abinda zai cigaba da riƙe shi.
Kusan yanzu duk wasu kuɗaɗe da yake da su a hannu sun ƙare sai canji ga hidima kuma a gabansa dan bayan ya gama da Zulaiha yana so ya yiwa Hajja gyaran gida dan har ya saka an fara duba masa gidan haya da zata koma shekara ɗaya kafin a gama aikin gidan sannan idan ya samu yanda yake so duk a shekarar nan yake so ya biya musu shi da ita aikin Hajji. Waɗannan burikan da sauransu ya saka ko ya ji yana so ya kawo ƙarshen mu'amalarsu da Jalilah nan kusa sai ya sake ƙara mata lokaci.
Wayar sa ya zaro daga aljihu, tun daren jiyan ya kasheta saboda kada a samu tsautsayi Zulaiha ta kira shi baya kusa a sake maimaita abinda ya faru tsakaninsa da Halima. Kunna wayar yayi, tana gama booting kuwa messages ɗin Zulaihan biyu suka diro na farko ƙorafi tayi ta kira wayar sa a kashe sai kuma wanda da alama yanzu da safen ta turo tana roƙon idan ya ga saƙon ya kirata ko hankalinta zai kwanta.
Kiranta yayi, ringing biyu ta ɗaga cikin muryar bacci.
"Ban lura na sam a ƙoƙarin na rage volume ashe wayar na kashe gaba ɗaya" ya fada mata bayan da suka gaisa. Motsin buɗe ƙofar da ya ji alamar Jalilah zata fito ya saka shi saurin yi mata sallama dan dama ya ce mata har ya fita office ma yau yana da uzurin sassafe. Sake latse wayar yayi ya kasheta ya turata ƙasan pillow ganin ta nufo shi tana murmushi.
Ya kasa ɗauke idonsa daga kallon adonta, Jalilah ta iya kwalliya duk kuma kamewar namiji in dai ta giftashi sai ya ƙara mata kallo ɗaya, Allah ya mata wannan baiwar ba namiji ba ko mace da wahala ta mata kallo ɗaya ta ɗauke kai dan bayan kyau na zahiri da take dashi tana da kwarjini da jan hankali.
Kan ƙafarta ta zaune tareda saƙale hannayenta a wuyansa babu ɓata lokaci ta haɗe bakinsu guri guda shima kuma bai yi mata musu ba sai da ta sake shi dan kanta kafin ta narke fuska tana shafa cikinta ya fahimci yaren yunwa take ji dan haka ya tashi suka shiga kitchen tana zaune tana masa hira har ya gama haɗa musu abin kari suka dawo falon suka ci.
Bai san me ya saka duk motsin da tayi a falon sai Halima ta faɗo masa ba ko dan gurin ya daɗe babu mace a ciki ne oho?
Zama sukayi ya kunna Tv ta kwanta haɗi da yin matashi da cinyarsa suna kallo abun su yanda kasan wasu sababbin aure, Mamanta ta sake kiranta sai da suka gama magana tayi ɗan danne danne a waya kafin ta kalle shi ta ce
"Wai ina wayarka ne?"
"Tana can ɗaki na" ya bata amsa ba tareda ya kalleta ba, ajiye tata wayar tayi ta gyara kwanciya ta fuskance shi ta ce
"Mom ce ta tura mun da kuɗi yanzu kaima na aika maka da 5m". Yanda kasan wanda ta ce ta xdxdqq ko nawa ne.
Haɗuwar sa da Jalilah ta buɗe masa ido har ya fara raina abinda Hafiz yake masa wanda a baya yake ganin kamar yanke talauchi yake bashi. Ganin fara cire ɗan kunnenta ya saka ya fahimci abinda take nufi, ɗazun ya gama raya ba zai sake biye mata ba amma kuma abinda ta masa dole itama ya bata tukuici me zafi.
Har ta fara cire undies ɗin ta sai kuma ya dakatar da ita ya ce su koma can part ɗin sa. Ashe ƙaddara da rabon ayi ne suke tafe, suna tsaka da masha'arsu yayi nisa gurin yiwa Jalilan abinda ya san zai faranta mata rai yana tsaka da tsotson ƙirjinta kawai yaji ta ce
"Wace ce wannan kuma?" Ya ɗaga kansa yayi mummunan gani Halima tsaye a kansu a wannan lokacin ta kuma same shi cikin yanayin da ko shi yafi kowa iya lauya zance a duniya bai isa ya kare kansa ba.
Da saurin gaske ya tashi zaune tareda jan rigar sa ya jefawa Jalilan akan jikinta, ya sake kallon in da Halima take tsaye saɓanin ɗazu da take kallonsu ta juya baya sai kuma a lokacin ya lura ba ita kaɗai bace harda Mu'azzam.
Kansa ya dafe da hannu biyu a fili ya shiga furta
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un shikenan na shiga uku"
"Ka shiga uku da me? Wai su waye ma waɗannan da zasu shigowa mutane kai tsaye haka ba tareda an basu izini ba? Kuma baka rufe gidan ba ko a ciki suke dama?" Jalilah ta faɗa cikin yanayin da babu wata damuwar ko tashin hankalin halin da aka tarar dasu a ciki.
"Halima ce" ya bata amsa yana kallon Halima da Mu'azzam suka bar falon, sai ta taɓe baki irin ko a jikinta ta ce
"Kuma sai ta faɗowa mutane haka nan don tana taƙamar gidan ta ne ko me?"
"Dallah Malama ki rufewa mutane baki, ke wace irin mace ce? Baki ganin abinda kika sakamu a ciki har kina da bakin cewa ta shigo ba izini ke bakiji kunyar abinda ta kamamu muna aikatawa ba ma kenan?" Ya taso mata. Hannu ta ɗaga masa kafin tace
"Ko da wasa kada ka sake tunanin ɗaga mun murya domin ni ba tsarar ka bace, kunya kuma kai ka aikata abin kunya ba ni ba dan kai ta sani" ta ja tsaki kafin ta miƙe ta jefa masa rigarsa daya rufa mata a yanda take ɗin kuma ƙirjinta a buɗen ta fice daga falon.
Bacci rabi da rabi yayi saboda alarm ɗin daya saita tun ƙarfe huɗu domin baya son wani dalili da zai janyo har tsautsayi ya gifta gari yayi haske bai fitar da Jalilah daga unguwar ba. Tun kiran farko yayi wanka ya zauna yana jira a kira sallah, ana fara kira kuwa ya shiga ɗakin ya fara tashinta amma tayi masa banza sai ma gyara kwanciya da tayi, cikin ƙufula da halinta ya ce
"Dan Allah ki tashi, kin san dai yanzu zakiga gari yayi haske idan kuma ba so kikeyi ki makara ba". Bata amsa ba ya gaji da tsayuwa yana mitar ta tashi jin har an tayar da sallah ya sa ya fita yana sakin ƙwafa, shi yanzu ya ke tunanin kamar ma da biyu tace sai a nan zata kwana saboda taja masa wani bala'in a unguwa. Hawa uku ya murzawa Get muƙulli kafin ya tafi, yana idar da sallah kuwa bai zauna ba ya fito da sauri ya koma yana tafiya yana satar kallon mutane gaba ɗaya ya tsargi kansa gani yake kamar kowa ya san mace ta kwana a gidansa a haka ya shige ya sakw kullo ƙofar ta ciki.
Duk yanda yayi da Jalilah akan ta tashi tayi sallah ta shirya su tafi taƙi ƙarshe ta balbaleshi da masifa akan ya fita ya bata guri saboda tazo gidansa ne zai uzzura mata ya hanata bacci ai ta san da tafiyar babu kuma sisinsa cikin kuɗin data biya balle yace idan ta rasa jirgi zata ja masa asara.
"Aikin banza kawai saboda na zo wannan akurkin gidan naka shine zaka ringa mun ihu akai in tashi to ba zan tafi ba idan kana da ƙarfi ka ɗauke ni a wuya ka fita dani kuma wlh idan ka ishe ni sai in tashi na fita ƙofar gida ka san ni sarai tijara zan maka nace ka kawoni kwanan gida ka hanani kuɗi na idan ya so sai naga ƙaryar iskanci" ta faɗa tana balla masa harara.
Tsaf ya zuge bakinsa domin baya shakku zata aikata abinda ta faɗa ɗin haka ya wuce yana waigenta tamkar zaiyi kuka ya koma falo ya zauna yana kallon agogo. Har ƙarfe bakwai ta gota bata fito ba ita da tace jirginsu ƙarfe takwas, shahada yayi ya sake komawa ɗakin ya tsaya daga bakin ƙofa yana kallonta ta tashi tana zaune tsakiyar gadon waya kare a kunnenta.
Murmushi ta sakar masa hakan ya bashi ƙwarin guiwar matsawa kusa da ita, da Mamanta take waya sai bayan ta kammala ta buɗe masa hannu alamar ya zo, haka ya ƙarasa ya rungume ta ta ɗora kanta a ƙirjinsa tana cewa
"Jikina duk yayi tsami kazo kayi mun wanka".
"Jalilah bakwai ta wuce fa kada ki makara" ya faɗa yana ƙoƙarin janyewa sai ta sake shige masa tana cewa
"8pm ne fa flight ɗin ba morning ba". Yanda kasan ya kurma ihu saboda takaici, duk yanda ya so ya cigaba da pretending sai da fuskarsa ta nuna ya zameta daga jikinsa yana cewa
"Amma tsakani da Allah me yasa zaki mun haka?"
Kallon banza ta watsa masa kafin ta miƙe tana banƙarewa ta sigar miƙa ya yi saurin ɗauke idonsa daga kanta, toilet ta wuce abinta tana wata tafiyar iyashege. Ya zauna gefen gadon yana cika yana batsewa a ransa yana ayyana yanda zai yi da ita su rabu ƙalau dan ya lura a shirye take data yanka masa nata rashin mutunchin.
Tashi yayi ya matsa bakin ƙofar toilet ɗin jin tana kiransa, ƙaramin kit ɗin ta tace ta miƙe mata ya wuce ya ɗakko shi yana buɗe ƙofar da niyyar ya bata ta ja shi ciki duk kuma yanda ya so da ya noƙe ko a jikinta sai da ya mata abinda take so kafin ta barshi ya fito tayi wankanta. Haka take kamar mayya in dai ta so abu to fa sai ta same shi ko ta daɗin rai ko aka sin haka.
Falo ya koma ya zauna bayan yayi wanka a ɗayan ɗakin ya dafe kansa da yaji kamar yana so ya masa ciwo. Allah ya sani tun sanda Halima ta bankaɗo sirrin sa komai ya fita a ransa kuma yayi alƙawarin dainawa amma kuma ya rasa yanda zai yi da Jalilah dukda ya fara janye mata kuma lokaci kaɗan yake jira dama wannan tafiyar da zasuyi ce target ɗin sa na ƙarshe da zarar sun shigo da kayyakin an buɗe company zai yi duk mai yuwuwa ayi rubutu ta yanda zai mallaki kaso mai tsoka cikin shares ɗin kamar yanda tayi masa alƙawari idan ya so ko sun rabu ya san ya tsira da abinda zai cigaba da riƙe shi.
Kusan yanzu duk wasu kuɗaɗe da yake da su a hannu sun ƙare sai canji ga hidima kuma a gabansa dan bayan ya gama da Zulaiha yana so ya yiwa Hajja gyaran gida dan har ya saka an fara duba masa gidan haya da zata koma shekara ɗaya kafin a gama aikin gidan sannan idan ya samu yanda yake so duk a shekarar nan yake so ya biya musu shi da ita aikin Hajji. Waɗannan burikan da sauransu ya saka ko ya ji yana so ya kawo ƙarshen mu'amalarsu da Jalilah nan kusa sai ya sake ƙara mata lokaci.
Wayar sa ya zaro daga aljihu, tun daren jiyan ya kasheta saboda kada a samu tsautsayi Zulaiha ta kira shi baya kusa a sake maimaita abinda ya faru tsakaninsa da Halima. Kunna wayar yayi, tana gama booting kuwa messages ɗin Zulaihan biyu suka diro na farko ƙorafi tayi ta kira wayar sa a kashe sai kuma wanda da alama yanzu da safen ta turo tana roƙon idan ya ga saƙon ya kirata ko hankalinta zai kwanta.
Kiranta yayi, ringing biyu ta ɗaga cikin muryar bacci.
"Ban lura na sam a ƙoƙarin na rage volume ashe wayar na kashe gaba ɗaya" ya fada mata bayan da suka gaisa. Motsin buɗe ƙofar da ya ji alamar Jalilah zata fito ya saka shi saurin yi mata sallama dan dama ya ce mata har ya fita office ma yau yana da uzurin sassafe. Sake latse wayar yayi ya kasheta ya turata ƙasan pillow ganin ta nufo shi tana murmushi.
Ya kasa ɗauke idonsa daga kallon adonta, Jalilah ta iya kwalliya duk kuma kamewar namiji in dai ta giftashi sai ya ƙara mata kallo ɗaya, Allah ya mata wannan baiwar ba namiji ba ko mace da wahala ta mata kallo ɗaya ta ɗauke kai dan bayan kyau na zahiri da take dashi tana da kwarjini da jan hankali.
Kan ƙafarta ta zaune tareda saƙale hannayenta a wuyansa babu ɓata lokaci ta haɗe bakinsu guri guda shima kuma bai yi mata musu ba sai da ta sake shi dan kanta kafin ta narke fuska tana shafa cikinta ya fahimci yaren yunwa take ji dan haka ya tashi suka shiga kitchen tana zaune tana masa hira har ya gama haɗa musu abin kari suka dawo falon suka ci.
Bai san me ya saka duk motsin da tayi a falon sai Halima ta faɗo masa ba ko dan gurin ya daɗe babu mace a ciki ne oho?
Zama sukayi ya kunna Tv ta kwanta haɗi da yin matashi da cinyarsa suna kallo abun su yanda kasan wasu sababbin aure, Mamanta ta sake kiranta sai da suka gama magana tayi ɗan danne danne a waya kafin ta kalle shi ta ce
"Wai ina wayarka ne?"
"Tana can ɗaki na" ya bata amsa ba tareda ya kalleta ba, ajiye tata wayar tayi ta gyara kwanciya ta fuskance shi ta ce
"Mom ce ta tura mun da kuɗi yanzu kaima na aika maka da 5m". Yanda kasan wanda ta ce ta xdxdqq ko nawa ne.
Haɗuwar sa da Jalilah ta buɗe masa ido har ya fara raina abinda Hafiz yake masa wanda a baya yake ganin kamar yanke talauchi yake bashi. Ganin fara cire ɗan kunnenta ya saka ya fahimci abinda take nufi, ɗazun ya gama raya ba zai sake biye mata ba amma kuma abinda ta masa dole itama ya bata tukuici me zafi.
Har ta fara cire undies ɗin ta sai kuma ya dakatar da ita ya ce su koma can part ɗin sa. Ashe ƙaddara da rabon ayi ne suke tafe, suna tsaka da masha'arsu yayi nisa gurin yiwa Jalilan abinda ya san zai faranta mata rai yana tsaka da tsotson ƙirjinta kawai yaji ta ce
"Wace ce wannan kuma?" Ya ɗaga kansa yayi mummunan gani Halima tsaye a kansu a wannan lokacin ta kuma same shi cikin yanayin da ko shi yafi kowa iya lauya zance a duniya bai isa ya kare kansa ba.
Da saurin gaske ya tashi zaune tareda jan rigar sa ya jefawa Jalilan akan jikinta, ya sake kallon in da Halima take tsaye saɓanin ɗazu da take kallonsu ta juya baya sai kuma a lokacin ya lura ba ita kaɗai bace harda Mu'azzam.
Kansa ya dafe da hannu biyu a fili ya shiga furta
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un shikenan na shiga uku"
"Ka shiga uku da me? Wai su waye ma waɗannan da zasu shigowa mutane kai tsaye haka ba tareda an basu izini ba? Kuma baka rufe gidan ba ko a ciki suke dama?" Jalilah ta faɗa cikin yanayin da babu wata damuwar ko tashin hankalin halin da aka tarar dasu a ciki.
"Halima ce" ya bata amsa yana kallon Halima da Mu'azzam suka bar falon, sai ta taɓe baki irin ko a jikinta ta ce
"Kuma sai ta faɗowa mutane haka nan don tana taƙamar gidan ta ne ko me?"
"Dallah Malama ki rufewa mutane baki, ke wace irin mace ce? Baki ganin abinda kika sakamu a ciki har kina da bakin cewa ta shigo ba izini ke bakiji kunyar abinda ta kamamu muna aikatawa ba ma kenan?" Ya taso mata. Hannu ta ɗaga masa kafin tace
"Ko da wasa kada ka sake tunanin ɗaga mun murya domin ni ba tsarar ka bace, kunya kuma kai ka aikata abin kunya ba ni ba dan kai ta sani" ta ja tsaki kafin ta miƙe ta jefa masa rigarsa daya rufa mata a yanda take ɗin kuma ƙirjinta a buɗen ta fice daga falon.